Showing 18001 words to 21000 words out of 259198 words

Chapter 7 - Rudin Kuruciya Book Complete Original By Ayshercool.txt

ko a gayamin"

Daddy yai murmushi yace "to ai gashi yanzu kin sani, kai kuma seka hanzarta gayamin jami'ar da kake so a waje, a fara processing tun da wuri"

Nan da nan jikin Sadik yai sanyi, dan yasan tabbas da zarar ya kammala makarantar nan, ƙasar waje za'a ce ya tafi karatu, Farhan ɗinsa fa zata iya jiran sa? Ƙaddara ma zata jira shi, shi baze iya jiran tsayin wannan lokaci, yana bautar biro da takadda ba, bayan shi abunda zuciyar sa take so daban ba, gaskiya Aure yake so, dan yafi damuwa da Yayi Aure akan wannan bokon.

"Ya naga kayi shiru? Ko baka son karatun ne?"

Ji yayi kamar yace baya so, Aure yake so ai masa Kafin karatu, amma yace "A'a ina so, ina nazarin wace jami'a zan tafi ne, don't mind me zanje inyi tunanin wace jami'a ta dace da ni"

Yai maganar yana miƙewa tsaye, Daddy yace "in wani abu ya shige maka duhu, ga yayyenka nan ko kazo ni ka sameni mu tattauna"

"To Daddy, Good night"

Yai maganar yana ficewa daga ɗakin.

Da yaje nasa ɗakin ma kasa baccin yayi, ga ƙoshi ga kwanan yunwa.

Da ƙyar bacci ɓarawo ya sace Prince Sadik, saboda damuwar da yake ciki.

Washegari ya kama Asabar ranar da za'a kai kayan Auren Dr. Usman gidan Hakimi, wanda se an kai can sun kwana sannan za'a kai gidan su Yarinyar da ze Aura ɗin.

Kaya sun kai kaya, akwatuna goma sha biyu ne na alfarma shaƙe da haɗaɗɗun kaya, masu tsadar gaske.

Lefen ya haɗu ƙarshen haɗuwa, haka aka zuba kayan a mota, za'a tafi.

Sadik yana saman bene, yana kallon yadda ake zuba kayan a Mota, ya ɗanyi ajiyar zuciya yace "Allah ka nunamin lokacin da zan haɗa kaya fiye dana Dr. a kaiwa Farhan ɗina, a ce yau gani zan Aure nima.

Yana nan a tsaye aka ja motocin aka tafi dasu.

Shima komawa yai ɗakinsa, ya shirya cikin ƙananan kaya ya fice nasa guri, dan a 'yan kwananin nan zaman Gidan nasu sam baya masa daɗi.

Nana na tafe a hanya tana zura hannu a hijjabinta, tana rarraba ido kar taje wani ya kalleta a banza, Ta koma gida Inna ta gane, tana tafe tana ta sauri kamar wadda take da wani uzuri a gabanta.

Tana zuwa ƙofar gida ta tarar da cincirindon motoci a ƙofar gidan, dama tun safe ta ga ana dafe dafe a gidan, ta tambayi Inna me ake haka amma ta gaya mata baƙar magana, taƙi gayamata meke faruwa.

Fararan fararan ta shiga ratsa mutanen dake harabar gidan, ta shiga cikin gida.

Ta tarar da mata a zazzaune ana ta rangaɗa guɗa, banda masu bushe bushe da ta baro a waje.

Neman Inna ta shiga yi cikin lungu da saƙo na gidan, cikin sa'a ta hango Innan, ta sha Kwalliya.

"Innarmu wai me akeyi ne haka?"

"To tambaya, daga daowarki ko cire kayan makaranta baki ba, kin zo kin cikani da tambaya"

"To Inna ni duk an zo a cika gidan a ina zanje in canza kayan ko ina mutane"

"In kin gama fitsarar kya tafi kije ki canza kayan" Inna tai maganar tana cigaba da hada hadarta.

Ɗakin Inna ta shiga ba kowa a ciki, ta cire kayan makarantar ta, ta zunduma uban hijjabi sannan ta shiga tai wanka, ta fito ta canza kaya.

Inna ta shigo ɗakin zata ɗau abu, ta ga Nana na binta da kallo, Inna tace "kayan lefen Usman aka kawo mu gani, sati me zuwa za'a kai shikenan?"

"Waye kuma Usman?"

Nana ta tambayi Inna, tana ɗan tura baki.

"Au Usaman ɗinma baki san shi ba? Iko se Allah to bari in miki yadda zaki gane, yaran nan masu tara gashi, na gidan Abdullahi"

Murmushi Nana tayi tace "Au se yanzu na gane, to ina kayan lefen suke?"

"Suna turakar Hakimi"

Nana ta zabura tace "bari inje ina gani"

"Ke bana son hauka, da baƙin a gurin zaki je? Kefa wani lokacin kwantacciya ce"

Nana ta ɗan haɗe rai, dan taji haushin ce mata kwantacciya da Inna tayi.

Se la'sar sannan masu kawo kayan suka tafi, Hakimi yace a bar kayan a nan, Ranar da za'a kai lefen, za'a tafi dasu daga nan.

Haka kuwa akayi, aka tafi aka bar kayan a nan, akan se ranar da za'a kai sannan za'a tafi dasu.

Ko da labari ya ishi Mother an baro kayan lefen nan a ƙauye Gidan Hakimi, abun ya baƙanta mata rai, ta dimga sababi akan me za'a baro mata kaya a can, salon a sace musu wani abun, haka tai ta sababin ta ta haƙura.

Ranar Monday a school prince yai shirin ko ta kwana ko da Nazir ze gaya masa wata maganar banzan akan abunda ya faru Ranar Friday, amma yaga be kulashi ba.

Ita kuwa Farhan faragaba ta dinga yi, dan kar ya cimata mutunci, dan ta fuskanci ya tsane ta sosai, ba ita kaɗai ke soyayya a makarantar nan ba amma yabi ya sa mata ido.

Cikin ikon Allah kuwa be tanka mata ba daga ita har Prince ɗin.

Ana fita break kamar jira take, ta tafi ajinsu Prince, sun barbaje suna ta hira ana kwasar dariya, suna tsara irin yadda zasu raƙashe a bikin Yayan Prince da za'ai nan da wata ɗaya, wanda ze kama a cikin hutun kirsimeti da kuma sabuwar shekara.

Sallama tayi tana duba inda za ta ga Prince, yana kashingiɗe yana game a wayarsa, sedai in sunyi abun dariya shima yayi.

Duk d rashin son kallo da Farhan ba tayi, da kwarjini da 'yan ajin nasu Prince ke mata, hakan baya hanata shiga ajin in dai za ta ganshi, kamar yasan ta shigo ya ɗago aikuwa su kai ido huɗu da Farhan.

A tare sukayi murmushi yace "welcome my cwt"

A hankali ta tako cikin tafiyarta me ɗaukar hankali.

Taslim ta kalleta ta ɗan yatsuna fuska, dan yanzu haushi Farhan take bata tace "wai ke kam ba kya gajiya ne? Kullum cikin sintirin zuwa ajin nan ki ke?"

Take jikin Farhan yai sanyi, ta ɗanyi sororo tana kallon Taslim, kuma Maganar Taslim tana kan gaskiya.

Prince yace "Taslim wallahi zan tatala miki rashin mutunci da baki taɓa tsammani ba, ina ruwan ki da ita? Me tai miki ko ajin daga gidanku ki ka zo da shi? Bana son haka ban sawa kowa ido ba, dan haka nima kar a samin"

Taslim tace "Allah ya baka haƙjri sarkin fushi, wasa nake mata"

"To ba'a san wasan" ya faɗa yana harar  Taslim.

Ya kalli Farhan yace "ƙaraso mana"

A hankali ta ƙaraso tana ɗan wasa da yatsunta.

Kan ta zauna ya ɗan tsaya yana kuma ƙare mata kallo, girma Farhan take ƙara yi, ƙara buɗwa take ga wani kyau da take ƙarawa.

Ɗan lumshe ido yai yana murmushi, ta zauna a ɗan nesa da shi kaɗan.

"To ya, kina lafiya my love?"

Sunkuyar da kai tayi cike da jin kunya, tace "lafiya ƙalau"

"Ai tun ɗazu naso in zo ajin ku, sedai nace bari in jira inga zaki zo?"

Murmushi kawai tayi ba tace komai ba.

"Nifa bana son wannan shirun, hira zaki min inji muryarki, kullum sedai ki zo ki kalleni kina murmushi, duk da murmushin naki burgeni yake, but say something"

"I have nothing to say" ta faɗa a ɗan shagwaɓe.

Dariya yai yace "muryarki da turancin kamar baturiyar England"

Seda ta ɗan zare ido jin abunda Prince ɗin nata yace.

"Farhan, an kusa bikin Yayana, zaki zo ko?"

"Yaushe ne?"

"Nan da 1month insha Allah, ai zaki zo ko?"

"Ina tunanin ko za'a barni inje a gida"

"Meyasa ba za'a barki ba?"

"Baban mu yana da tsaro sosai, ba'a barina fita sedai in a 'yan ajinmu wasu zasu je, su zo mu tafi tare, kuma ka bani kati in kai gida"

"Karki damu dan wannan ba Matsala, yama za'ai ai bikin bro tawa matar va taje ba, kin san daga bikinsu se namu fa"

Zare ido tayi sosai kamar ya faɗi wani abun tsoro.

"Meye naga kina zare ido haka?"

"Ya za'ai amana Aure yanzu, mufa yara ne"

Ƙasa ƙasa suke hirara ba wanda yake jina bunda suke faɗa, amma jin abunda Farhan ɗin tace yasa Prince cikin ɗaga murya cewa  "What!".

Seda aka jiyo aka kallesu, Prince ya basar yai ƙasa da murya tare da ɗan haɗe rai yace "suwaye yaran?"

Ɗan tura baki tayi tace "to ai naga ko makaranta ba mu gama ba, kuma base mutum ya girma yake Aure ba, waye ze mana Aure a haka?"

Seda Prince yai murmushi, ya jinjina wauta da ƙuriciya irin ta Farhan, sannan yace "waye yace miki shi girma a fili yake, waye yace miki sharaɗin Aure ne se mutum ya girma sosai za'a masa Aure?"

"Ai haka naga anayi"

"Hmm Farhan kenan, yanzu idan Dad ɗina yazo nema min Aurenki baza'a bni ba?"

Ya faɗa in a very serious tone.

Kamar za tai kuka tace "wallahi ina ga se ya kusa ɓallani, cewa ze ya akai nai saurayi har na fara Maganar Aure?"

"Hakane You Are still Baby, but looking so....

Se kuma yai shiru yana cigaba da ƙuara mata ido, har seda ta ɗan tsargu.

"Amma ai kina sona ko?"

Ɗaga ido tai ta kalleshi, ta mayar ta sunkuyar.

"Hmm i understand"

Babba ne na ss3 ya shigo ajin, yana shigowa Taslim ta miƙe da gudu ta rungumeshi, ya ɗagata yana juyi da ita a tsakiyar class ɗin.

Mamaki ya cika Farhan, wannan wane irin rashin hankali ne da rashin ta ido.
A shagwaɓe Taslim tace "I miss You Honey"

"Miss you too dear, ai tunda na dawo tun lats week ba kya Zuwa bamu haɗu ba"

"Bama gari, munje Abuja that's why, you are well dear, amma dai ka warke ko?"

Babba yace "Alhamdilillah jiki yayi sauƙi sosai"

Farhan kama gaba ɗaya seta tsargu, wata kunya ta mamayeta, ganin haryanzu sunƙi sakin juna Taslim da Mubarak wato Babba.

Sadik yace "gaskiya Mubarak ku fita can waje kuyi, kun san Babyna jaririya ce kuna iskanci a gabanta karku ɓatamin mata ku sa mata wani tunanin daban"

Taslim tace "ba wani jaririya, ta san komai, don't mind them my sugar"

Tai maganar tana kissing Mubarak a kumatunsa.

Nasir yace "kaga in da ake abu, ba irin soyayyarku ba, soyayya irin ta zamanin iyaye da kakanni"

Farhan ta miƙe tace "Na tafi aji"

Sadik yace "sun kore ki ko? Banzaye kawai muje in kaiki class"

Ya miƙe suka jera suka fita, sedai Nas yabi bayan Farhan da kallo.

Amin ya daki cinyarsa yace "kai lafiyarka kuwa?"

"Lafiya ƙalau, ina kallon Yarinyar nan ne kawai, gaskiya ina ni zan sharewa Prince hanyar nan, kan uba ka ga abunda na gani kuwa?"

"Aikuwa da yaci ubanka la'ada waje"

"Kai dall ƙyaleshi, se wani abu yake waishi na Allah, this girl is looking so hot ka gane ai"

"Karka kuskure ya gano ka wallahi, dan karonku baze maka daɗi ba, nasan akan yarinyar nan ba abunda baze iya ba"

Nas yace "za'a cigaba da ɗora shi a layi, idan yaƙi ɗaukar haske zega aika aika"
Suka cigaba da hiararsu ta rashin ɗa'a.

Kwanci tashi asarar rai, satin kayan lefe guda cif, duk 'yan uwa dangin Alhaji Abdullahi duk suka zo suka ga kaya, sannan Inna ta shirya ita da Jikarta aka kawo motoci aka kwashe su su da kayan.

Can gidan Alhaji Abdullahi suka tafi da kayan, Nana ta ware ido ta finga kallon gidaje kamar biscuit, kamar a ɗauka a ci dan kyau da tsaruwa.

A ƙauye ana cewa ba gidan da ya kai na Hakimi ƙaruwa, amma yanzu idonta ya gane mata in da ake gidaje.

Da ana zuwa da ita tsohon gidan, amma Inna ta daɗe bata taka ƙafarta gidan nan ba se yau.

Hajiya Hauwa kuwa wato Mother, taji haushin yadda aka taho da 'yan ƙauye, wai za'a kai kayan lefe, abun nan ya baƙanta mata rai a nata faɗar zasu ɓata mata lamari dan ba hankali suka cika ba.

Ba yadda ta iya tunda ga uwar mijinta, kuma shikansa maigidan yana gari balle tai rashin mutunci, tun asalin kai kayan ƙauye ma abun be mata ba, balle kai kayan lefen tare da su, ga ƙawayenta da 'yan uwanta 'yan gayu amma za'a haɗasu da tarkace.

Aka kuma shishshsigo da Akwatuna, Inna tasa aka sassauke kaya aka sake buɗewa, Hakimi ya sa an ƙara atamfofi dozen a ciki, Inna kuma ta saka zobuna da sarƙoƙin azurfa.

Nan aka dinga guɗa ana Allah ya sanya Alkhairi.

Wata ƙawar Mother tace "kai Hauwa, dangin mijin nan naki duk da 'yan karkara ne, amma sun san abunda yakamata, wallahi da nawa dangin mijin ne, sedai a kaisu a haka inma basu saci abunda zasu sata ba, amma kalli aabun arziki kuma atamfofi masu tsadar gaske, su kansu azurfofin nan masu tsada ne sosai"

Tsaki Mother tayi tace "nifa duk abunda za'a saka da mutanen nan ba sonake ba, inma bayarwar ne a aiko dasu mana, kawai an kwashi kaya an kai musu, an kuma kwasowa an dawo, za'a kuma kwasa a kai kaya dasu, ni Allah yasa ba wani abun sukai wa kayan ba, dan ni ba wani yarda nai dasu ba"

"Ke Hauwa, meye aibun hakan? Taɓɗijan, a zaminin nan ki samu dangin miji suna son 'ya'yanka, ai wallahi banga aibun hakan ba"

Tsaki Mother tai, ta cigaba da cika tana batsewa, tana wani basar da su kamar taga bola.

Daddy ne ya shigo tare da Ango, wato Usman.

Take 'yan ƙauyen nan suka kaure da guɗa ana shewa, Alhaji Abdullahi ya dinga murmushi, haka shima Usman ya dinga murmushi.

Alhaji Abdullahi ne ya fara zubewa a gaban mahaifiyarsa wato Hajiya Inna, ya dinga mata kirari sannan ya gaisheta abun gwanin burgewa.

Ya cire hular kansa ya durƙusa a gabanta yace 'barka da zuwa farar uwa me farar aniya, 'ya ga Hakimi mata ga Hakimi, katangar sukari kowa ya jingina dake se ya lasa, farar uwa abun alfahri 'ya'yanta, shalelen Hakimi barka da zuwa uwata ta kaina"

Seda mutanen da ke falon suka saka shewa, saboda abun gwanin burgewa.

Murmushi Inna  tayi, wanda se fararen haƙoranta suka bayyana sannan ta amsa masa "Sannunka ɗan gidan Innarsa, mun sameku lafiya"

"Lafiya ƙalau Inna"

"An shab turai, Usaman Allah ya kawo mu lokacin Aure, Ubangiji Allah ya Sanya Alkhairi"

"Ameen Inna"

Usaman yace "Inna ina wuni"

"Ba zan amsa ba, bayan ba kwa zuwa inda nake"

Usman yace "ba haka bane Inna, kin san ba zaman ƙasar muke sosai ba"

"Eh kuna can kuna yiwa nasara bauta ba, ai shikenan ni gani nazo ai, ina nan har a yi biki ai, ga kaya nan Hakimi ya ƙara maka, yace yana maka murna, se kuma Allah ya kaimu Lokacin ɗauren Aure ze zo"

Alhaji Abdullahi yace "Masha Allah, muna godiya ranki ya daɗe, Allah ya ƙara arziki yasa afi haka"

Nana ce tace "Kawu ina wuni?"

Ɗagowa Alhaji Abdullahi yai ya kalli Nana yai murmushi yace "ai ban kula dake ba, ni yakamata in gaisheki Uwata ta kaina, ina wuni Ummana"

Rufe fuska Nana tayi cike da jin kunya ba tare da ta amsa ba.

Inna ta nuna mata Usman tace "to kin san wannan? Ko kuma baki sanshi ba se me tara gashi?"

Nana tace "Nasan shi mana"

"To ya sunansa?"

Shiru Nana tayi tana tunani, amma ta kasa tunawa.

"Kaga abunda nake faɗa ko ko Abdullahi, bata san sunan 'yan uwanta ba, sedai tace 'ya'yan kawunmu masu tara gashi"

Alhaji Abdullahi yace "Ayi haƙuri Inna, insha Allah za'a san abunyi"

Nana gajiya tayi da zaman, ana ta hira ta tashi dan fitowa harabar gidan ta sake ganin abubuwa.

Ta fito tana ƙarewa motocin dake harabar gidan kallo, bin motocin ta dingayi ɗaya bayan ɗaya tana shafawa, tana sake lelleƙawa.

Ta gaji da wannan ta nufi wani ɓangaren daban.

Leƙe leƙnta ta cigaba dayi, tana zazzagawa.


Motar Prince na shiga gidan, ya fuskanci da yauma da mutane a gidan, tun daga cikin motar yake jan uban tsaki yana cewa aikin banza anzo an cikawa mutane gida, an hanasu sakewa.

Ya saɓo jakarsa ya nufi BQ yana ƙwafa yana masifa, sedai yana shiga falo ya tarar da ita tana tattaɓa ƙatuwar plasma dake jikin bango.

"Ke wace wannan? Uban me kike a nan?!"

A razane ta waigo ta kalleshi tace "yi haƙuri ban san ba'a shigowa nan ba"

Gani yai kamar ya santa amma ya manta inda a santa.

'ke wace irin banza ce, daga zuwa gidan mutane kawai kije inda ba'a aikeki ba, dama kinga mutane na zuwa nan ne?"

Haɗe rai tayi tace "kar ka sake zagina ba nace kayi haƙuri ba" tai maganar tana tura baki.

'dalla zoki fita ki barmin ɗaki, mahaukaciya kawai"

Nana tace "Kut, wallahi kaine mahaukaci bani ba"

"Ni kike cewa Mahaukaci?"

"To uban waye yace ka fara gayamin mahaukaciya?"

"Ubanki ne" ya bata amsa.

"Sedai ubanka bani ba"

Aikuwa ya nufi inda take gadan gadan....

Free pages are not much, hurry up and subscribe yours.

Ayshercool
07063065680.

[6/4, 4:21 PM] Jakadiyar Arewa: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️

RUƊIN ƘURUCIYA

PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

P. W. A

*Story and written by*
AISHA ADAM (AYSHERCOOL)

Writer of

WATA KISSAR..(Sai mata)
ABDUL JALAL
AƘIDATA (paid book)
WUTA A MASAƘA
NOW RUƊIN ƘURUCIYA (paid book)

_Labarin RUƊIN ƘURUCIYA, na iya zuwa da wani salo, wanda baku saba ganinsa a rubutuna ba, hakan ya biyo bayan akan abunda aka gina labarin, wani abun ze ɓoyu wani Abun baze ɓoyu ba sakamakon labari ne akan teenegers, yara masu tashen Balaga, but hakan ba ya na nufin na sauka daga kan tsarin yadda nake Rubutu bane, ƙofata a buɗe take dan karɓar ƙorafi, gayra ko shawara_

⚠️⚠️⚠️ƘIRƘIRARREN LABARI NE, BAN YADDA A JUYAMIN SHI TA KOWACE SIGA BA SEDA IZININA ❌❌‼️





9_10





Kafin ya cinma ta tuni ta arta a na kare, kamar walƙiyya ta bar falon da gudu, ya bi bayanta sedai yana fitowa ya neme ta ya rasa kamar aljana, se kace iska ta kwashi takadda, ba ita ba alamarta.

Ya ja tsaki ya koma ɗakin, yana ƙoƙarin tuna in da ya taɓa ganin fuskarta.

Ganin hakan ba ze fushsheshi ba yasa ya shige bedroom ɗinsa yana tsaki, gami da jin haushin bikin nan na Yayansa, dalilin wannan bikin da yayime yayimen mutane ake a gidan, masu hankali, sekace akansa aka fara Aure.

Haka yana ƙunƙuni yana mita, ya cire kayan makarantar sa ya shiga yai wanka, ya fito yai sallar azahar, yana son shiga cikin gidan cin Abinci, amma ganin taron jama'a da ke gidan ya hanashi shiga, dan baya son taro sam.

Ya ɗakko tsaleliyar wayarsa ya nemo lambar Khairat ya kirata.

Tana fara ringing ta ɗaga tace "ya akayi?"

Seda ya ɗan yatsuna fuska sannan yace "kina gidanmu ne?"

"Eh ina nan"

"Suwaye a cikin falon nan?"

Khairat tace "ji wata Magana, ta yaya zan iya lissafo maka wanda suke falon, mutane ne da yawa gasu nan a gidan"

"Wani taimako nake son kiyi min"

"Ok am all ears"

"Abinci na zaki kawomin BQ"

Kamar Sadik na gabanta ta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login