Showing 21001 words to 24000 words out of 259198 words
Chapter 8 - Rudin Kuruciya Book Complete Original By Ayshercool.txt
ɗan murguɗa baki tace "meya hana kazo ka ɗauka da kanka?"
"Nifa kin san taron mutanen nan ne bana so, in ba zaki kawomin ba shikenan"
"Zan kawo maka ba dan halinka ba"
"In dan halin nawane karki kawomin, bana son wulaƙanci fa"
"Meye wani abun wulaƙanci kuma? Ina zaman zamana ka sani aiki"
Tsaki yayi ya kashe wayar ya ajiye yace "Aikin banza ayi a gama wannan bikin ya tafi ya bawa mutane guri, ko ma huta da wannan jarabar, kullum gida a cike mutum baze huta ba, Aikin banza kawai"
Se mita yake shikaɗai, haka nan ya tuno Nana da ta zage shi ɗazu a falo.
Wani dogon tsakin ya kumayi, ya ji ina ma ya kama Nana, da se ya kusa karyata, seya tataka ta ya koya nata hankali, daƙiƙiyar yarinya fusaka kamar ta yaron aljani.
Shikaɗai ya cigaba da soki burutsunsa, yana zage zage.
Khairat tai sallama ta shigo bedroom ɗin, ta kalleshi tace "lafiya kake tsaki kai kaɗai, tun daga falo ana jiyoka kana masifa ciki ciki"
"Bakomai" ya bata amsa.
"Kai faɗan naka ya kai ka dinga yi kai ka ɗai ma a ɗaki, sekace me aljanu?"
"Ke kika sani miƙomin Abinci na ni"
"Au in maka abun arziki amma ba godiya, se gadara da isa ko, wallahi ka canza hali Sadik, wannan ba halin shiga jama'a bane"
"Ina ruwana da wata jama'a, kawai an takurawa mutane, mutum da gidansu anzo an hanaka sakewa, wai ma dan Allah suwaye yau kuma a gidan nan, dan ni wata mahaukaciya ce ta shigo min ɗaki yau"
Dariya Khairat tayi tace "wace irin mahaukaciya kuma? Gaskiya duk baƙin Gidan nan banga Mahaukaciya ba"
"Ni na ganta ai"
"Gaskiya ba wata mahaukaciya, Kakar ka ce fa tazo da 'yan ƙauyen ku za'akai lefen Dr."
"What!" Sadik ya faɗa yana yatsuna fuska.
" 'yan ƙauye kuma Farhan?"
Cikin mamaki Khairat tace "Farhan kuma? Ka manta sunan nawa ne?"
"Ohh sorry, Khairat nake so ince, meye haɗin 'yan ƙauye da kuma kai lefe? Kai Allah ya sa dai yau wannan tsohuwar zata tafi"
Khairat tace "kakar taku?"
"Ita ɗin mana, tsohuwar nan jarababbiya ce ta ƙarshe wallahi, faɗan tsiya ne da ita ga takurar masifa da sa ido, ni shiyasa ko ƙauyen nan bana zuwa, dama am allergic to the water of the village, ke nifa Even iskar garin nan is irritating me, Abincinsu ma ƙyama yake bani, sam bana zuwa garin nan"
"Taɓ aikuwa tace tana gidan nan har ayi bikin dr."
"Kut, wallahi Farhan barin gidan nan zanyi, ina zan iya da tashin hankali da takura?"
"Farhan again?"
"Ohh sorry, ke nifa Farhan ce a zuciyata da kuma harshena, shiyasa nake kiranki da sunanta"
Ɗan haɗe fuska Khairat tayi tace "wace kuma Farhan?"
"Sirikar mother ce, ana auren dr. Se nawa da Farhan Yarinya"
"Aure kuma Sadik, waze maka Aure Yanzu?"
"Ke dalla ban isa auren bane, ke tashi ki ban guri ma kin sani a gaba, zanci Abinci"
"To ni meye haɗina da cin Abincin ka?"
"Zaki tashi ki barmin ɗaki ko sena ji miki ciwo"
Ta miƙe tace "kana cewa kakarka masifaffaiya, ai kaima masifaffaen ne da be san abun arziki ba, kuma gobe ma rana ce"
Share Khairat yai ya zuba Abincinsa ya fara ci.
Yaci ya ƙoshi ya miƙe tsam, ya haye gadonsa ya fara chatting, tunani yake ina ma Farhan ta na da waya, da ya kirata ya ji muryarta yaji daɗi.
Faruku na shiga falo, ya tarar da Inna ga Daddy da Usman duk a zaune a falon, dam be san da zuwansu ba, ya ƙarasa gaban Inna yace "Sannu da zuwa"
Ta ɗaga kai ta kalleshi tace "Sannunka, ba'a ganinku se anzo inda kuke ko Faruku?"
Ya ɗan shafi sumarsa yace "ba haka bane Inna, ya Hakimi yana lafiya?"
"Yana lafiya, sedai yana mitar baya ganinku"
"Abubuwa ne suka ɗanyi yawa amma insha Allah muna nan tafe"
Inna tace "yadda ka tara wannan gemun ai kyawunta ace kaima da naka auren za'a haɗa"
Daddy yace "haba Inna, guda nawa Faruk ɗin yake? Dan ya tara gemu yarone ƙarami kawai abunsu ne na yaran zamani ya tara wannan uban gemun, amma haryanzu be kammala karatu ba"
"Haka dai, boko boko boko, to boko yana hana Aure ne, in dai yaro yana da yadda zeyi, ku dena yiwa 'ya'yanku kallon yara fa, zamanin nan se addu'a kawai"
Ran Mother ya fara ɓaci ds Inna, a ranta tace "da yake kowa irinku ne, Aure, Aure, da yaro ya fara tasawa besan komai ba se a hau Aure, se tara 'ya'ya nan da nan mutum yabi ya lalace ya tsofe da wuri, saboda ku dai Jima'i shikaɗai mutumin ƙauye ya sani" ta ja gajeren tsaki ta bar falon.
Inna tace "Ni haryanzu banga ɗaya yaron naka ba Abdullahi"
Daddy yace "ina ga be dawo daga makaranta bane"
"Aikuwa dai ina son in ganshi dan rabona da shi na manta"
Daddy yace "a daiyi haƙuri ranki ya daɗe"
"Sadik! Sadik!"
Ya jiyo muryar Faruk na kiransa tun daga falo, tsaki Sadik yayi yace "sekace be san in da nake ba yake min wannan kiran daga waje"
Yai banza ya cigaba da danna wayarsa.
Faruk ya shigo bedroom ɗin yace "kana ji ina kiranka amma kai min banza?"
Sadik yace "na amsa ba ka ji bane kawai"
"Kaje Inna tazo, tana neman ka kaje ka gaisheta"
Yatsuna fuska yayi yace "tana nemana kuma? Me nayi?"
"Se kayi wani abun tukuna? Kajeka gaisheta"
"Nifa yanzu na dawo daga school gaskiya na gaji, Yanzu ina zuwa zata fara ƙaƙalen abunda za tai faɗa a kai, dama ni ba ta sona wannan tsohuwar, kawai ka ƙyaleni"
"In baka je ba, kaga ta ji daɗin hucewa akan Mother, tace ita ke sangarta ka"
Tura baki Sadik yayi ya juya baya, dan karma ya cigaba da jin abunda Faruk ze faɗa.
Se bayan la'asar sannan aka kai kayan lefen nan gidansu Yarinyar da Usman ze aura, iyayenta duk da kasancewa suma masu abun hannu ne, amma sunyi murna sosai sunyi appreciating kayan da aka kawowa 'yar ta su na lefe.
Daga nan gurin kai kayan 'yan uwan su Daddy na ƙauye aka maida su, aka dawo da Inna da sauran ƙawayen Mother gida.
Sadik kuwa be fito ba se bayan la'asar, ya fita ya silale ya bar gidan, ya tafi nasa yawon.
Ɗaki aka bawa Inna ita da Nana a falon ƙasa, ɗakin ba laifi babba ne, da banɗakin sa a ciki, ga gado da katifa a ɗakin, se ƙaramar sif ta kaya.
Nana nata faman taka tsantsan akan abunda za tayi, dan kar tayi abunda Inna zata mata tijara a cikin mutane, dan ita Inna ba ruwanta koba gaban waye idan tai ba dai dai ba faɗa za tai mata.
Sadik kuwa Be dawo ba se dare, lokacin kowa ya kwanta, sannan ya shiga falo ya wuce Kitchen, ya ɗakko Abincin sa ya koma BQ.
Ita kanta Mother ba ta ji daɗin zaman Inna a gidan nan wai se biki ba, dan sam bata son sa ido irin na Inna.
Mother na ta zuba ido taga ɗan auta, amma sam auta be shigo Gidan nan ba, tasan dama ba lallai ya shigo ba saboda mutane da ke gidan.
Dan haka da safe tai niyyar zuwa ta ganshi kafin ya tafi Makaranta.
Nana kuwa ba ta gajiya da ƙarewa gidan nan kallo, saboda tsaruwar gidan ba ƙaramin burgeta yake ba, tana sha'awar cigaba da zagawa da ganin in da ba ta shiga ba ta gani, sedai tana tuno arangamar da su kai da Sadik tai tsaki tace "Aikin banza kawai, Allah yasa kar in kuma haɗuwa da wannan sakaran, idan na kuma ganinsa kuwa nima sena masa rashin mutunci"
Gari ya fara haske, Inna tana can tana laziminta, Nana ta lallaɓa ta fito, masu aiki se kaiwa suke suna komowa, suna ƙoƙarin tsaftace gidan, Suna ta ƙoƙarin gyara komai, Mother na fitowa suka fara ƙoƙarin gaisheta, amma se wani shan ƙamshi take tana amsawa da ƙyar tana cigaba da basu umarni.
Ɓangaren Daddy ta nufa, tarara ya tashi, ya kalleta yace "good morning sweetie"
"Morning dear, ka tashi lafiya?"
Kamar ƙaramin yaro ya ɗan ɓata fuska yace "not that fine, kin gujeni mun dena kwana tare"
"Mutane na kaiwa na komowa, kawai a ganni a ɗakinka ga mahaifiyar ka a gidan nan"
"Ina ruwan Inna damu, ai ita ba ruwanta damu, yakamata kije ku gaisa, ni naje na gaisheta kuma tana mitar Sadik be zo ya gaida ita ba"
Mother tace "ai kasan halin ɗan naka, shifa mutane ne ba ya so, ni kaina ban ganshi ba tun jiya, yanzu nake sa ran zuwa in dubi shi ma, zan sa yazo ya gaisheta"
"Ai gara yazo su gaisa, kar ranta ya ɓaci"
A ranta tace "jarababbiyar tsohuwa ba, yanzu se ta samu a gaba da ɗana da surutu" amma a zahiri tace "insha Allah zan tura shi, me zan dafa maka ne?"
"Komai ma kika dafa ni ci zanyi, am missing Your food, komai kika bani zanci"
Tai murmushi tace "shikenan ina zuwa"
Ta jiya ta fito, Nana cikin masu aikin nan su talatu ta shiga, tana tai musu surutu da tambayoyi, tace su bata ta taya su mopping, amma suka hanata.
Sedai surtun nata dariya yake basu, Nana Akwai baki, amma duk da dariyar da suke Mother na fitowa, suka nutsu suka cigaba da abunda suke.
Nana ta kalli Mother tace "Ina kwana"
"Lafiya" Mother ta amsa da ƙyar.
Ba ƙaramin haushi Nana taji ba da yadda Mother ta amsa nata gaisuwa, Nana a ranta tace "aikuwa za'a daɗe ban kuma gaisheki ba"
Ta jiya ta fita harabar gidan, abun sake burgeta yayi, duk yadda yake da hadimai a gidan Hakimi, amma wannan sun sha banban.
Saboda an fito da wasu daga cikin motoci ana wankewa, ga masu gyara flowers, suna basu ruwa komai gwanin ban sha'awa.
Nana ta ƙarasa gurin me wanke mota tace "Dan Allah ka bani abun zuba ruwan nan in wanke motar nima"
Dariya yayi ya kalleta yace "kina mace zaki wanke Mota, ai wannan aikin maza ne"
"To ai iya zuba maka ruwan kawai zanyi"
"A'a ba ruwana, ai ba aikin mace bane"
Nana tace "to me bawa bishiyoyin nan ruwa idan nace ya ban ze bani, ai naga mata ma zasu iya yi"
'je ki tanbaye shi kiji"
Ba musu ta nufi inda dattijon kewa Flowers ban ruwa, tace "dan Allah nima zanyi"
Waigowa yai ya kalli Nana yace "ke jikar Inna, wannan aikin ai ba naki bane"
"Kai ya akai kasan ni jikar Inna ce?"
Yai dariya yace "kai ai tun kina zanin goyo nasanki, kuma gaki nan kamar ki ɗaya da ita sak"
Nan ta cigaba da zuba masa surutu kamar wadda aka ƙona a ka.
Faruk ne ya fito da gajeren wando da vest, da gani motsa jiki yayi yace "Baba Ilu sannu da aiki"
Baba yace "yawwa Faruku"
Nana a ranta tace "ikon Allah, ji wanan ƙato ba kunya ƙwauri duk a waje yana yawo a cikin gida, duk tsiraicin sa a waje"
Ya kalli Nana da ta ƙura masa ido yai murmushi yace "kin tashi lafiya?"
Ɗaga masa kai tayi alamar eh, yace "Yama sunan naki?"
Tace "Nana"
Yace "Ohh yeah, Naana exactly, weldone Naana"
Yai maganar yana tafiya, ita kuwa binsa tai da ido tace "iyayi, Nanan ma baza'a faɗa yadda kowa ke faɗa ba se anyi wani iyayi, maganar ma da wani iyayi ake yinta, waisu lallai turawa'
Daga ƙarshe ta koma ƙirga motocin dake harabar gidan.
Mother ta shiga ɗakin Sadik, ta tarar yana saka belt ɗin sa na Uniform.
Yana ganin Mother yai murmushi yace "good morning mother"
"Ba zan amsa ba, yaushe rabon da kaje inda nake?"
"Hmm mother kenan, kema kin san bana son taron mutanen nan, kowa sekabi kana gaishehi ana wani kallon mutum, ana surutu that's why kawai naƙi shigowa, but am really missing you"
Yai maganar tare da kissing ɗin hannun Mother.
Ta kalleshi tace "naji, but kasan Granny ɗinku ta zo ko?"
Yatsuna fuska yayi yace "na sani"
"Amma ba kaje ka gaisheta ba? So kake tazo ta sani a gaba da masifa tace ni na hanaka zuwa ka gaisheta"
Cikin shagwaɓa da sangarta yace "Mother kin san fa ni matar nan ta tsaneni wallahi"
"Haka nan dai zakai haƙuri kaje"
"To yanzu na saka Uniform, kar in makara zanje school, idan na dawo zanje"
"Yawwa Son, safe journey ka kula da kanka"
Ya jinjina kai ya cigaba da shirinsa, ita kuma Mother ta fice daga ɗakin.
Seda ya kammala shirinsa tsaf, ya fito Falo ya tarar Mother ta ajiye masa Abincin sa, ya zauna yai breakfast sannan ya fito dan tafiya makaranta.
An fito da motar da ake kai Sadik makaranta, motar tayi fes se ƙyalli take kamar sabuwa.
Tun daga nesa ya hango Nana a jikin motar, tana leƙawa tana zagaye motar tana shashshafa motar.
Prince na hangota ya tunkaro inda take a fusace, "Ke meye haka! Ƙazama a wanke motar kizo kina taɓawa, wallahi kika sa min datti sekin wanke ta"
Wata uwar harara tai masa tace "motar banza motar wofi, an shafa dattin, sedai ka mutu"
"Ke ni kike gayawa haka? Wallahi zan tattka ki banza Mahaukaciya kawai"
"Seka takanin in gani ai, kuma an shafa dattin, ta tofa miyau a jikin motar ta zura da gudu tai cikin gidan.
Sadik ya tsaya soror yana kallon motar, ba abun yabi Nana ba ya sake makara, yai ƙwafa ya buɗe motar ya shiga, ranasa a ɓace yana tunanin kalar rashin mutuncin da ze mata.
Shikam Musa direban Sadik, kamar ya tuntsure da dariya, saboda abunda Nana tai masa, amma ya gimtse dariyar sa, kar yayi Sadik ya masa rashin Kunya.
Sadik na zuwa makaranta ya samu guri ya tsaya a gurin Assembly, yana jin yadda su Nas suke masa Magana, amma yai shiru yaƙi kulasu.
Farhan na ta leƙe ta hango abun ƙaunarta, sedai yadda ta ga fuskarsa tasan yana cikin damuwa, ransa a haɗa babu alamar fara'a sam a tare da shi.
Jikinta se yai sanyi ta shiga tunanin meya sami Prince haka yai wannan mugun haɗe ran haka?
Aka sallame su daga Assembly ground, suka tafi aji.
Suna zuwa aji, malamin da suke da shi ya shiga ajin, dan haka abokan Sadik basu samu damar tambayar sa abunda ke damunsa ba.
Har malamin ya koyar da abunda ze koyar ya fita, Prince yana tsaki lokaci zuwa lokaci, gaba ɗaya ransa a jagule yake.
Taslim ce ta fara magana tace "Allah ya temaki Yarima, what's wrong with you know? You look somehow disturbed"
Tsaki ya kuma yi tare da ɗan hura hanci, ya gyara zamansa.
Amin yace "yeah, that's what I want ask since, kika rigani meke going ne?"
Prince ya ɗan nisa sannan yace "wallahi mutane ne suka zo suka cika mana gida, harda wata mahaukaciyar yarinya, kidahuma 'yar ƙauye"
Nas ya kwashe da dariya yace "kai Prince, wannan cin mutuncin fa? Ba relative ɗinka bace?"
"Ni nama san wacece? Ni na manta in da nasan ta ma gaba ɗaya, kawai ganinta nai a gidan nan, wata fitsararriya 'yar ƙauye"
Amin yace "kai harka kira wata 'yar ƙauye, ai budurwarka ce 'yar ƙauye"
Sadik yaiwa Amin wani warning glance, ba shiri yace "Ohh am sorry i dont mean to hurt you"
Sadik yace "Ai se nayi maganin yarinyar nan dan na tsane ta gaba ɗaya bana son ganinta"
Taslim tace "to aini har Yanzu banji abunda tai maka ba"
Nan Sadik ya basu labarin abunda Nana tai masa, daga jiya zuwa yau, sosai suka dinga dariya, hakan ya ƙara bawa Prince haushi, dan haka ya tashi ya bar ajin.
Ajin su Farhan ya tafi, sedai suka haɗu a hanya, ya zuba mata idanunsa seda ta ƙaraso in da yake sannan ta tsaya, tare da sunkuyar da kanta.
"Lovely meyasa ba ki zo ajinmu ba yau?"
"Na ganka ɗazu a gurin assembly kamar ranka a ɓace, shiyasa ban zo ba"
"Amma Farhan ki ganni a cikin damuwa amma ki ƙi zuwa in da nake, baki damu da halin da nake ciki ba kenan ko?"
"A'a ba haka bane, naga idan kana fushi baka son aje in da kake ne"
"Kuma se akace miki hadda ke? Da kinzo da tuni na manta da abunda ya faru, kin barni wancan Nasir ɗin sun sani a gaba suna sake bani haushi, dan dai ban biye musu bane"
Farhan tace "am sorry, kayi haƙuri dan Allah"
Yai murmushi yace "bakomai, ai matata bata laifi"
Jin maganar tasa tayi wata uwar gundumemiya, wai matarsa ba ko kunya, shi baya jin kunyar wani yaji yana faɗar irin wannan maganganun sam.
Suka jera suka tafi har ajinsu Farhan, a can ya zauna suka dinga hira, yana bata labarin kayan da aka kaiwa yayansa na lefe yace "ji nai kamar in ƙwace kayan nan a kai gidanku, ace na aurenmu ne Ni da ke Farhan"
Shiruu tai ba tace Komai ba, kuma ba ta ɗago idonta ba.
"Farhan, wai meyasa a duk lokacin da nai miki irin wannan zancen kike yin shiru ne, ko dai ba kya sona ne?"
Ta girgiza masa kai alamar a'a.
"To meyasa ba kya son in miki Wannan zancen?
Tai shiru ba tace komai ba, ya gyara zama yace "Look Farhan, ina da kuɗin da zan iya yin Aure, kuma wallahi ni dagaske nake sonki Farhan, dan Allah ki dena doubting a kaina Please"
Ta sake jinjina masa kai yace "Yawwa, zaki ci wani abun ne?"
Tace "A'a"
Ya zira hannu a aljihunsa ya ɗakko dubu biyu ya ajiye mata.
Zare ido tayi za tai Magana amma ya haɗe rai yace "shhhh" ya juya ya fita ta bi bayansa da kallo.
A varrender ajinsu Farhan, ya haɗu da Sir Nazir, Nazir ya tsaya ya bishi da ido, Sadik ya haɗe rai sosai, ko kallon inda Nazir yake be ba ya wuce.
Tunani Farhan ta shiga yi akan ya za tai da wannan kuɗin da ya bata?
Ba tai aune ba taji mutum a kanta, tana ɗaga ido ta ga Sir Nazir, yace "wato ba ki rabu da wannan yarn ba ko?"
Ɗan tura baki tai, ta sunkuyar da kai.
"Wai ke dan Allah da ma haka kike da taurin kai ne? Waima meyake gaya miki da ya sa kika liƙe masa haka? Ko kuma me kuke yi da yasa kullum se yazo in da kike?"
Ƙin ɗago kanta tayi da ga sunkuyar war da tayi.
"Kije ki cigaba da biye masa karki fasa, nan gaba idan ya gama morar ki, ze watsar da ke ne, a lokacin ne zaki nadama mara amfani, wannan yaron sam ba tarbiyya ce da shi ba, ɓata miki lokaci ze a banza"
Babban abunda yake ɓatawa Farhan rai be wuce duk wanda suke soyayya a makarantar nan ita kadai ya sawa ido ba, kuma abun takaicin be wuce yadda yake dizgata a gaban kowa ba, saboda Prince.
Nazir na fita Yasmeen ta ja tsaki tace "nifa wannan mutumin ya fara ɓata min rai akan abunda yake wa Farhan, ya fiye sa ido da takura wallahi"
Lilly tace "ke bake kaɗai ba nima haka wallahi, ni yana burgeni yadda ya