Showing 1 words to 3000 words out of 216282 words

Chapter 1 - KWANTAN BAUNA BOOK 2 COMPLETE BY Nanah Haleemah.doc

??ࡱ?>?? &?????????????? ?
?
? ?
?
???????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?Root Entry???????? ?F?WordDocument????1?%0Table???????? Data
???????????????????? P??U"KSKS?1?%?'???????rr????_s??+4???????????$_?*r?????????;?s;?s?;s???s ?^`????^Normal d??,CJmH sH nHtH_HOJPJQJ^JaJTA`????TDefault Paragraph FontOJPJQJ^Jfi`????f Table Normal :V ?4?
l4?a? OJPJQJ^J(k`????(No List ?'???}t??B?v2?t?\?:t޸??">?w????@V?R?`?5bwh? ?U????r([17/12, 10:39 pm] Nafisat Alwasa: Arewabooks@nanahaleema11
*026.*

Gaban ta ya fad'i k'irjin ta ya fara duka da sauri-sauri ta cire wayar daga kunnen ta ta kalla taga number sabuwa special mai sauk'in haddacewa ta sake mayar da wayar kunne ko zata ji an kuma magana amma shiru ba'a ce komai ba kuma har lokacin ba'a katse kiran ba. Sake cire wayar tayi ta kalla taga dai har lokacin tana tafiya ta sake mayarwa amma still shiru ba'a cewa komai.

Ta bud'e baki zatayi magana aka riga ta ta hanyar fad'in, "Don't confuse yourself." Zak'in maganar sa take ji har sassan jikin ta hakan ya saka ta yin shiru ta kasa magana tana jin maganar sa na zaga ko ina na jikinta ta lumshe ido ta bud'e kafin ta daidaita kanta tace, "waye yake magana ban gane ba." Baice komai ba daman kuma bazai ce ba taji an yanke wayar ba tare da an sanar da ita ba tabi wayar da kallo har lokacin k'irjin ta bai daina bugawa ba.

_Ina sonki._ abinda akace ya fad'o mata a rai ta sake kallon number zuciyar ta cike da mamakin wanda ya kira ta kuma bai fad'a mata waye ba ya kashe, tsaki taja tana so ta kawar da tunanin ko waye a ranta amma abin yaci tura ta zubawa waje d'aya ido kalaman da aka fad'a mata suna yi mata yawo a cikin kanta ta kasa kawar dasu daga kwakwalwar ta.
Tana so ta tuna inda tasan muryar amma ta kasa tunawa dan kamar a waya ta banbanta da wacce ta sani a zahiri hakan ya saka ta kawar da tunanin daga kanta ta kwanta a hankali kalaman Anas nayi mata yawo a a zuciyar ta da gangar jikinta.

&

"Mum yanzu me hakan yake nufi? Ana nufin ina ji ina gani Asad zai auri wata bani ba ba?" Jidda ta fad'a tana kallon Mum hankali a tashe. Mum tace, "nace ki kwantar da hankalin ki nice fa mahaifiyar ki, Asad bashi da wata mata in ba ke ba a duniyar nan."
"Amma naji kina min wata magana daban."
"Eh ya furta yana sonta amma asiri suka masa dan in kika ga yarinyar mai gadin gidan nan ma bazai d'auka ba balle Asad."

Jidda tace, "Mama ban damu da kyanta ko munin ta ba kawai ki sanar dani ni an ajjiye a gefe kenan?." Mum ta fusata tace, "Na fad'a miki ki kwantar da hankalin ki kece matar Asad ba ita ba, yadda nake miki tanadin yadda zaki mallake shi ko uwar sa bata isa ba balle wata banza a gefe da ta shigo yanzu. Asad naki ne ke kad'ai daga ke sai dangin ki dan haka ki nutsu wannan auren ba mai yuwa bane ba."

"Ta ya za'a fasa bayan kince yana sonta?."
"Ita bata son sa ai."
"A ganin ki Mum zak'i amincewa da tayin Asad ne?. Yana da kud'i, yana da kyau ga sarauta taya zata ki amince masa?." Mum tayi shiru kafin tace, "ko ta amince ko kar ta amince bata isa ta mallake shi ba, naki ne ke kad'ai zan iya yin duk abinda zanyi wajan ganin kin zama mallakin Asad koda kowa baya son hakan. Sai na juya Rabi'atu kamar yadda take juya mutane tafin hannun ki nake so Asad yazo ana zuwa wannan b'angaren zance ya k'are."

Jidda tayi bata ce komai ba tana girgiza kanta dan ita maganar ba wata shigarta tayi sosai ba tunda taji ance yana son yarinyar take jin kishinta a zuciyar ta, k'wafa tayi kafin ta tashi ta bar falon ta hau sama. Da kallon Mum ta bita tana k'iyasata abinda zata aikata akan lamarin dan ko da tsiya koda tsiya-tsiya Asad bazai auri Rauda ba y'ar ta zai aura, ko yana so ko baya so.

*?%?%*

Hydar ne zaune a gaban mai martaba shi kuma yana duba littafi a hannun sa kafin ya ajjiye yace, "Ina jinka Hydar." Hydar yace, "Allah ya k'ara maka lafiya Mama tana neman hana Asad auren wacce yake so, tana k'okarin cusa masa ra'ayin k'inta duk da yana sonta ya sanar dani zai iya barin ta sabida Mama. Abba meyasa Mama take yiwa Asad haka dan ya kasance me yi mata biyayya a ko wanne lokaci?."

Mai martaba yayi murmushi ya kashingid'a yace, "Mahaifiyar ku tana da wani hali wanda sai kuna taya ta da addu'a Allah ya cire mata shi daga cikin halayen ta in ba haka ba zata sha wahala yanzu ko nan gaba. Tana amfani da biyayyar da yake mata tana hana shi abinda yake so a ko wanne lokaci dan cikar burinta kawai, amma wannan karon bazan zuba ido ya rasa abinda yake k'auna ba wanda na tabbatar da alkhairin da yake cikin abinda yake so d'in zan nuna mata gaba da gaban ta. Kai ka tabbatar da yana sonta?."

"Na tabbatar da wannan takawa, yana k'aunar ta sosai zan iya cewa itace mace ta farko da Allah ya d'ora masa k'aunar ta. A idanun sa in ana maganar ta mai martaba zai tabbatar da abinda nake fad'a, yana sonta so mai tsanani."
"Ikon Allah kenan. Babu damuwa zan yiwa tufkar hanci kafin ta farga, sai dai ta farka daga dogon bacci ta tarar aikin gama ya riga da ya gama. Gobe kaje kazo min da mahaifin yarinyar zan sanar dakai inda zaka kai shi." Hydar yace, "Allah ya kaimu goben. A huta lafiya" ya fad'a yana tashi ya fita mai martaba ya bishi da kallo.

Ajiyar zuciya mai martaba ya sauke ya kalli gefe guda abubuwa da dama sun cushe masa a kansa da kuma zuciyar sa, shi kansa zai so ayi auren Asad da gaggawa kodan ya cika mutum bashi mulkin ya huta gabad'aya, zai kuma tsaya wajan ganin Asad ya samu abinda yake so a karon farko in sha Allah.

A b'angaren Mama lokaci d'aya ta fize ta rame sabida tashin hankalin da take ciki wanda ta d'orawa kanta, hankalin ta gabad'aya baya tare da ita tana zaune ta zubawa tv ido a zahiri sai ka d'auka kallo take amma ba kallon take ba ta tafi duniyar tunani.
"Mama!." Suhaima ta fad'a daga bayan ta tana k'arasowa kusa da ita ta ta zauna a k'asa kusa da k'afar tana kallon ta. Bata amsa ba hakan ya saka Suhaima tace, "Dan Allah Mamana ta daina saka damuwa a cikin zuciyar ta dan Allah, in Allah ya rubuta yarinyar da ake magana a kai matar sace sai ya aure ta kenan babu amfanin damuwa akan lamarin. kuma....." Kallon da Mama tayi mata ya hanata k'arasawa ta tashi daga kusa da ita cikin tsoro ganin irin kallon da take mata tsaf zata iya bugeta.

"Kar na sake jin wannan maganar a bakin ki matuk'ar kina buk'atar kwanciyar hankali na da naki kwanciyar hankalin, in kuma kina son b'acin raina ne sai ki fara daga yanzu. baza ta zama matar Asad ba da ganin wannan ranar gwara ganin ranar mutuwa ta!" Ta k'arasa fad'a tana kallon Suhaima. Suhaima tace, "Allah ya zuci zuciyar Mama, tuba nake" ta fad'a tana barin wajan tana waiwayon ta.


Da sauri Mama ta d'auki waya ta kira layin Mum ana d'auka bata jira anyi magana ba tace, "ya maganar mu?." Daga can b'angaren Mum tace, "Da nace a bari sai zuwa jibi sabida kar ayi saurin gano muna da hannu a ciki." Mama tace, "A gano mana sai me?! Me zasu iya yi mana?, kiyi gaggawar aiwatar da komai a yau bana so a samu matsala, a b'atar da yarinyar nan daga duniya gabad'aya hankali na zai fi kwanciya!" Bata jima mai Mum zata ce bama ta yanke wayar tana wuci.

Ta kwashe sama da awa biyu a zaune a wajan har dare yayi tana zaune ganin kiran Mum ya saka ta d'auka tace, "Good news please." Mum tace, "na tura wanda zasu shiga gidan, yanzu haka ma sun tabbatar min da suna cikin gidan sun samu mafaka jira suke dare yayi su aiwatar da komai." Mama tace, "kar ki kuma kirana sai an tabbatar an kashe ta" tana fad'a ta yanke wayar ta ajjiye a gefen ta.

Suhaima da take jin komai gaban ta ya fad'i ta zaro idanu waje tare da dafe k'irjin ta ta wuce Maman da sauri ba tare da ta kula da ita ba ta fita zuwa b'angaren su Asad. A haukace ta shiga falon taga Hydar a zaune yana kallon ball ta kalle shi tace, "Yaya Hydar ina Yaya Deaf?." Kallon ta yake ganin ta a firgice yace, "meye kike neman sa?, lafiya kike?."
"Mama ce ta tura a shiga gidan su yarinyar nan a kashe ta."
"What!" Hydar ya furta yana wara idanu tare da mik'ewa tsaye yana kallon ta yace, "Wacce yarinya?."
Suhaima tace, "Wacce Yaya Asad yake so."

"Ke kin tabbatar da abinda kike fad'a kuwa bana son hauka" ya fad'a yana kallon ta a firgice jin abinda baiyi tsammanin ji ba. Girgiza kai tayi tace, "Allah abinda naji tana fad'a a waya kenan, dan tace kar a kuma kiran ta sai an tabbatar an kashe yarinyar. Kayi wani abu bro bana son hakkin kisa ya rataya akan Mama." Asad da ya shigo falon yaji abinda ake fad'a ya kalli Hydar kafin yayi magana ya juya da sauri ya fita.

Da sauri Hydar yabi bayan sa amma kafin ya k'arasa ya shiga mota yaja har ya fita daga gate na biyu ya nufi na farko dole shima ya d'auki tasa motar ya shiga yabi bayan sa da gudu. yayi mamakin gudun da Asad yake yi domin bai ganshi ba alamun yayi nisa sosai dole shima ya ware motar yana binsa a guje.

A can gidan su Rauda lokacin duk sun kwanta kasancewar sun saba baccin wuri har Baba ya kwanta kowa yana muhallin da yake. Rauda tana zaune a gefen gadon da suke kwana ita da Ummulkhairi ta saka dogon wando da riga tana zaune tayi tagumi gabad'aya bata jin dad'in komai tunda ta karanta message d'in Anas har lokacin bata dawo walwalar ta ba. Abu taji an buge a falo tayi shiru tana sauraro sai taji shiru sai ta kawar da tunanin kafin ta fara jin motsi a hankali, ta d'auka Baba ne hakan ya saka bata fito ba jin magana k'asa-kasa ya saka ta k'okarin tashi ta d'auki abinda yake taimaka mata wajan tafiya tana takawa a hankali sabida kar suyi k'ara ta k'araso jikin k'ofar, kokwanto take ta bud'e ko kar ta bud'e zuciyar ta duk ta cika da tsoro haka kawai bata san dalili ba.

"Ban gane d'akin nata a nan ba kun san bama so a samu matsala." Abinda taji an fad'a kenan a hankali gaban ta ya fad'i ta zaro idanu waje kafin ta kuma ji ance, "Mu shiga kawai in kuga ba bata nan sai mu shiga wani duk wanda yaso yi mana gardama muga bayan sa."
Rauda ta dafe k'irji a hankali tace, "Wa suke nema?." Tsoro duk ya bayyana a tare da ita tana jikin k'ofa ta kasa kunne babu zato taji an turo k'ofar tayi baya ta fad'i k'asa tare da yin k'ara.

"Shiiiiiii" d'aya daga cikin su ya fad'a fuskar sa a kulle kafin ya kalli d'akin yaga Ummulkhairi a kwance tana bacci dan d'akin da haske yace, "Kika kuma yi mana ihu sai mun kashe kowa na gidan nan." Kai take girgizawa ta kulle hannun ta da baki tana kuka sosai jikin ta na rawa hankalin ta ya kai makura wajan tashi. d'aya ya kalli d'aya yace, "Mu aiwatar da aikin mu kafin azo a same mu." Ba musu d'aya yayi bayan Rauda ya saka mata igiya a wuya wanda yake tsaye a kanta yace, "Fad'i kalmar ki ta k'arshe domin kashe ki zamu yi."

Bakin ta rawa yake hawaye na zubowa daga idanun jikin ta na kyarma ta kasa cewa komai sai ido da take bin su dashi ganin mutuwa kusa "baki da abin fad'a kenan, kai ja igiyar" ya fad'a yana kallon bayan sa. Tamke igiyar yayi a wuyan ta idanun Rauda suka k'afe sukayi ja sai kakari take amma babu damar yin numfashi sun tokare shi sai bak'in idonta ya juya baka ganin sa sai farin da ya koma ja kawai ake gani, k'afa take jurawa tana k'okarin rike igiyar d'ayan da yake tsaye ya rik'e hannayen ta duka.

Su Asad kuwa duk yadda suka so shigowa gidan abin yaci tura an kulle gidan ta ciki gashi basu san hanyar da zasu bi su shiga cikin gidan ba, hankalin Asad ya tashi matuk'a har ya bayyana a tare dashi ya rasa abinda zaiyi ya shiga gidan gashi jikin sa yana bashi sun kashe ta ko suna gab da kashe ta. Tashin hankalin da yake ji tunda Allah ya kawo shi duniya bai tab'a jin irin sa ba, ji yake kamar ana daka naman jikin sa ana soya zuciyar sa a man da yake da mugun zafi.

Mahaukacin dukan da ya yiwa gate d'in har su da suke ciki sai da suka ji suka tsorata wanda ya matse mata wuya ya sake ta da sauri ya k'arasa wajan taga ya bud'e yana kallon harabar gidan ya kuma jiyo dukan gate d'in da akayi.

"Oga akwai mutane a waje fa ya kamata muyi sauri mu bar nan" ya fad'a yana kallon ogan nasu ya kalli Rauda da take kwance babu numfashi a tare da ita yace, "Muyi sauri mu fice" ya fad'a yana fita da sauri yana fitowa suka had'a idanu da Asad da yake tsaye bayan sa Hydar sai Baba da yake tsaye kusa dasu.

"Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un" Baba ya fad'a hankali a tashe yana shiga d'akin da Rauda take ya ganta a kwance babu numfashi yace, "Shikenan sun kashe ta!."
[17/12, 10:39 pm] Nafisat Alwasa: Arewabooks@nanahaleema11
*027.*

Kalmar da Baba ya furta ta girgiza Asad, wani irin yammmmm yaji yana shiga ko wanne b'angare na sassan jikinsa take yaji duniyar tana juyawa kansa ya sara zuciyar sa na bugawa kamar ana dukan ganga, gaban sa ya fad'i irin wanda bai tab'a yi ba tunda yazo duniya kamar an zare masa kuzarin jikin sa ya tsaya sak yana kallon k'ofar ba tare da ya aikata komai ba.
"Bata mutu ba tana numfashi, da ranta" ya sake ji Baba ya fad'a bai san lokacin da ya sauke ajiyar zuciya ba sabida wani k'aton dutse da yaji ya sauka daga k'irjin sa hakan ya bada damar saukar numfashin sa daidai.

Mutanen Asad yake kalla ya gansu a zube a gaban Hydar ko wanne guiwa a k'asa ya kalli sauran mutanen falon yaga gabad'aya iyalan gidan su bayyana a wajan Rauda ce da mahaifiyar ta kawai babu da alama tana waja Rauda a d'aki, Baba ya kalli Asad ya kalli mutanen ukun da suke zube a wajan yace, "Kashe Rauda suka so suyi ban san dalilin su ba, me Rauda tayi muku zaku kashe ta? Kisa fa da muke kallo a film itace yau har gidan mu..? bazan lamunci wannan abun ba dole maganar nan taje kunnen hukuma sabida gaba."

Asad ya kalli Hydar shima ya kalle shi suka kalli mutane ukun a tare babban ciki yace, "Ranka ya dad'e wallahi Allah turo mu akayi mu kasheta, batayi mana laifin komai ba alqawari aka yi mana in muka kashe ta za'a bamu kud'i masu yawa, ba'a san ran mu bane ba biyan mu akayi akace mu tabbatar bata numfashi."

"K'arya kuke yi, wanne mak'iyi Rauda take dashi da zai aiko a kashe ta?, me take dashi da za'a aiko har cikin gidan su a kashe ta?. Ita ba y'ar film ko y'ar siyasa ba akan me kuke neman rayuwar ta?" Umma ta fad'a tana fitowa daga d'akin tana goge idanun ta cikin tashin hankali. D'aya daga ciki ya kuma cewa, "Hajiya Sadiya ce ta saka mu, itace tace muzo mu kashe Rauda kada mu bar wata shaida da za'a gane hakan. Mun jima a cikin gidan nan b'uya mukayi sai da dare yayi muka shigo nan."
"Wacece Sadiya?" Baba ya fad'a yana kallon su shi kansa hankalin sa ya tashi.
"Mu dai da haka muka santa bamu san sunan da zamu fad'a maka nata ba."

Baba yace, "Zakuyi bayani a gaban y'an sanda dan wallahi sai nayi k'arar ku bazan zuba ido akan wannan lamarin ba dan ba k'aramin case bane ba." Hydar yace, "kwantar da hankalin ka Baba za'a yi musu hukunci daidai dasu baza mu bari su sha ba zamu tabbatar sun girbi abinda suka shuka. Abu na farko a d'auko ta a kaita asibiti a duba lafiyar ta."

Umma ta kalle shi tace, "Bama buk'atar hakan mun gode basai anje asibiti ba ta farfad'o" Umma ta fad'a ranta a jagule tana kallon su.
Shigowar y'an sanda guda biyu ya saka suka juya suna kallon su suka k'araso kusa da Asad suna yi masa alamun jinjina yace, "Ranka ya dad'e, Allah yaja zamanin ka, gani na fito kamar yadda ka buk'ata." Asad bai tanka masa ba sai Hydar ne yace, "wad'annan zaku tafi dasu a kaisu kotu a tabbatar anyi musu hukuncin da ya dace dasu, kisa suka so kisan ma akan mutum mai mahimmaci a wajan Asad." D'aya daga cikin su yace, "An gama ranka ya dad'e zamu tabbatar sun girbe abinda suka shuka. ku tashi muje shigar dare ce yau zakuyi" ya fad'a yana kallon su da suke durk'ushe akan guiwar su.

"Dan Allah kuyi hak'uri wallahi ba laifin mu bane saka mu akayi akace muzo muyi amma ba aikin kaimu bane ba. Ku

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login