Showing 93001 words to 96000 words out of 242549 words
gama shirinta da yamma za ta je gidan Salima. Washe-gari ne zai kama sunan Zara. Anyi mata waya an fada mata batun haihuwar amma har yanzu bata leka gidan ba. Shi ne Innayo ta ce taje ta duba mata. Maimuna ta zama mai wankan jaririya da kanwarta. Innayo ko kallo Zaran bata isheta ba. Jaririyar kuwa ko sau daya bata dauketa ba. Abin da ya tsayawa Zara a kahon zuci har ya zarta damuwarta na shariya daga Innayo.
Abinci dai mai rai da lafiya da kanta take dafawa ta kuma tabbatar ta ci. Daga nan bata sake bi ta kanta sai wani girki. Zara taji ta muzanta ta tsani kanta. Ko hira ta dauko Innayo ba ta taba amsa mata. 'Yan uwanta sun san me yake faruwa amma sun zabi su zuba ido 'ya da uwa su daidaita da kansu.
Da Anti Hasiya ta kira Honourable ta fada masa ta shirya sai ya ce ta tafi da Ayaah. Ta so yi masa musu sai ya nuna mata ya yi haka ne domin ta dinga shiga cikin ragowar kannen mahaifiyarta. Ba zai yiwu su zuba mata ido sai yadda take so ba. Amincewa tayi da kudurin idan Ayaah ta kawo mata raini za ta dauki mataki.
"Ke da wadda zamu gidan nata waye babba?"
Mamakin tambayar tayi tunda tun fitowarsu take zumbura baki. Anti Hasiya ta dauke kai ne kawai don bata son abin da zai janyo Ayaah tayi mata rashin kunya a adaidaita sahu.
"Daga Yaya Maimuna sai ita sannan Zara."
"Ita ce farar nan ramammiya kamar tsohuwa da muka gani a dakin Innayo da sallah?"
Anti Hasiya ta daga yatsa tana kada shi a gaban Ayaah.
"Ki kiyayeni Ayaah. Ban fito dake don ki ci mutumcin 'yan uwana ba."
Da yake bakinta bashi da linzami sai ta rage murya amma yadda ta san Antinta za ta ji.
"Ai dai kin san gaskiya na fada."
Anti Hasiya sai taki kula ta. Gaskiya Ayaah ta fada. Duk gidansu babu wanda ya kai Salima lalacewa a gidan miji. A kalla duk talaucin mijin Maimuna yana kaunar matarsa. Ita kuwa Salima Alh. Rabi'u ya gama cutarta. Duk dan Adam din da za a biya bashi dashi ina yaga daraja?
Daga soron gidan suke jin hargagin Maigidan Ale Gambo yana ta zaginta.
" 'Yar bakinciki, muguwa, azzaluma. Ban fada miki kafin na dawo ki je gida ba? Ace 'yar uwarki ta haihu kin kasa zuwa barka balle ki karbo min..."
Niyar Anti Hasiya ta gama jin dalilin wannan tijara. Idan ba haka ba Salima ba za ta taba fada da bakinta ba. Ayaah kuwa sai ta fada gidan tana doka sallama iya karfinta. Ta san duk abinsa dole ya sararawa matarsa a idon baki.
"Salamu alaikum. Anti Salima kina ina ne? Ina ta doka sallama naji shiru."
Baki Anti Hasiya ta rike tana biye da ita har tsukakkiyar tsakar gidan. Wai tana ta doka sallama. Harda wani Anti Salima kamar gaske.
Salima na ganinsu ta share hawayenta da sauri amma duk sun gani. Ale Gambo ba kunya ya amsa sallamar ya dora da karyar ceton kai.
"Yauwa Hasiya naji dadin ganinki. Don Allah ki fadawa Innayo babu hannuna a ciki. Tun ranar da aka sanar da batun haihuwar Zara nake cewa ta tafi gida barka taki."
Salima ta kalle shi da jajayen idanunta ka kawar da kai. Ale Gambo ya karar da duk wani kuzarinta. Fadan da damuwa tayi har sun haddasa mata hawan jini. Zaman 'ya'ya ukun da suka haifa take yi sai ko gudun karawa Innayo nauyi. A haka ma ita ce karfinta, ina ga ta koma gidan da yara? Dalilinta kenan na daina tanka masa duk bala'insa. Ta daina yin yadda yake so tun lokacin da Innayo tayi ciwon hakori. Duka da zagi babu irin wanda bai yi mata ba a tsukin lokacin. Yau ma tashi ya yi babu komai a jikinsa sai naira dari. Shi ne ya dauka ya bata wai taje gida barka sai ta fadawa Innayo tana son kudi. Ko dubu goma ce ta samo masa kamar ya bata ajiya. Kin tafiyarta be ya janyo mata abin da su Ayaah suka tarar.
"Zan yi mata magana." Kawai ta ce yasa kai ya fita.
Hannun Salima ta ja rai a bace suka shiga dan mitsitsin falonta. Yadda ta san halin Hasiya sai ta fara bata hakuri tun kafin tayi magana.
"Zan je barkar fa. Dama saboda halin Zara ne na ce sai na sami lokaci."
Hasiya ta dage gira ta sha kunu "sannu shugabar kasar Najeriya. Karshen aiki dai kenan da rashin samun lokaci."
"Baki yarda ba kenan?" Salima ta tambayeta tana kirkiro dariyar dole.
"Kema da ki ka fada baki yarda da kanki ba sai ni? Tun yaushe yake dukanki?" Da tayi shiru bata amsa ba sai Hasiya ta canja tambayar da cewa "me yasa baki taba fadawa kowa ba?"
Fashewa Salima tayi da kuka mai cin rai. Tana yi tana sheshsheka saboda yadda ya dade yana ci mata rai.
"Baba dai babu abin da zai yi min idan na fada. Innayo kuma in dai ba ajalinta kike so nayi ba ai ya kamata na hakura haka. Ita ba za ta huta ba Hasiya? Kullum cikin nema banda ma ciwon ido da hawan jini sun hanata sukuni kina tunanin da har yanzu bata cigaba da abinci ba?"
Hasiyan ma sai hawayen tausayin Innayo da Salima. Ta san da Innayo tana da karfi da tuni ta raba 'yarta da wannan kaddararren auren.
Share ido tayi ta kalli Salima "kin san dai bai kamata ki cigaba da zama a haka ba. Idan ya kuma zuwa zai dake ki kar ki yard. Ki kokarta ki kwaci kanki ko da cizo ne."
Ayaah na gefe da 'yat kwallarta saboda tausayin halin da Salima take ciki. Bata taba sanin abin da ya shafesu zai dameta ba amma yau da akayi a kunnenta taji sai ya tsaya mata a rai. Tana jin gurguwar shawarar Anti Hasiya a cewarta ta shiga zancen nasu ba jiran gayyata.
"Wane irin ta kwaci kanta Anti Hasiya? Ko dai baki kula da girmansa bane? Jibgege ne, wannan idan aka sami akasi ta iya cizonsa wallahi karshenta ya zubar mata da hakora. Bai yi ruwan imani ba ko kadan."
Da hawayen sai da tasa Salima yin murmushi da ta ce wai bai yi ruwan imani ba. Hasiya ta ma manta tare suke saboda basu saba hada fita ba. Daure fuska tayi a zatonta Ayaah rashin kunya za ta yi musu.
"Sai ki kawo taki shawarar tunda baki san idan manya suna magana ki kama bakinki ba."
Ayaah ta tsuke bakin tsiwarta "naga nima dai kanwar mamana ce Anti Saliman nan. Abin da ya shafeta ai ya shafeni."
"Haka! Wanda ya shafeni ne bai shafeki ba ko?"
Salima me zata yi banda dariya. Rabonta da ganin Ayaah an kwana biyu. Amma idan ta hadu da Hasiya da wuya su rabu bata dauko zancenta ba. Abin mamaki shi ne kullum hirar korafi ce akan rashin ji da rashin kunyar Ayaah gareta, amma fa ko Innayo ta fahimci ba karamin so take yi mata ba. Irin son da akasarin uwaye suke yiwa tabararrun 'yan autansu.
"Nima ai baki damu da abin da ya shafeni ba."
"Ayaah banda rashin kunya mana. Shi yasa kuke fada da babarki. Wane dan arzikin ne iyayensa suna fada yana fada banda abinki? Bata hakuri." Salima ta umarceta.
Sai da ta yatsina baki ta bada hakurin. Hasiya za tayi magana Salima ta girgiza mata kai da sauri sai tayi shiru.
"Sai ki kawo taki shawarar tunda tawa bata yi ba."
"In yi magana kuma ace bani da kunya?" Ayaah ta fada idonta akan Anti Hasiya.
"Tunda ita ta baki dama ki fada mana. Idan baki fadi taki ba zan dauki ta Hasiya. Iyaka dai ya zubar min da hakora ku zo dubiya."
Anti Hasiya da Ayaah suka yi dariya tare. Sannan Ayaah ta ce,
"Anti Salima idan ya sake zuwa dukanki kar ki gudu kuma kada ki kare. In zaki iya ma ki takali fadan don ayi a wuce wurin. Daga nan dukan farko ki zube kasa ki daina motsi. Don Allah Anti duk yadda zai yi kar ki motsa. Wai baki da 'ya'ya ne?" Ta tambaya tana duba cikin falon kamar lokacin zasu bayyana.
"Allah dai Ya shiryeki. Su Murja sun san kowa cikin 'yan uwansu banda ke. Su uku ne. Babban namiji yana makarantar kwana. 'Yan matan kuma suna islamiyya."
"Sun kai shekara goma?"
"Goma da sha uku."
Ayaah tayi dariya "sun san yana dukanki?"
"Sun sani."
"Anti Hasiya don Allah mu zauna har su taso in yi musu karatun ceton uwa."
Salima da Hasiya sai suka jidadi. Ko me zata ce zasu saurara domin su kara janyota jikinsu ta san mahimmancinsu. A nata bangaren kuwa hasashen yadda zata taimaki kanwar mahaifiyarta take yi.
For once in her life Ayaah sai taji dadi wai yau ita Anti Hasiya ta bawa dama har take saurarenta haka.
Akan hanyarsu ta zuwa gidan Innayo, bayan sun bawa Ayaah dama ta yiwa kannenta hudubar taimakawa mahaifiyarsu ne Hasiya ta dinga maimaita kalan Salima a zuciyarta "Wasu yaran tsabar son ki sauraresu yake saka su fandarewa ko yin abun daukar magana. Da gangan Ayaah take tunzuraki dazu don kawai ki kulata taji dadi. Da alama mai son kulawarce sai aka yi rashin sa'a masu sauraronta basu dorata a turba mai kyau ba har zamanku ya kasance irin haka. Daga yanzu ki dinga janta a jiki kamar yadda kike yiwa 'yan uwanta kina nuna mata cewa tana da matsayi a wurinki ita ma."
I just published "19" of my story "UWA UWACE...". https://my.w.tt/IK4e2j4j0bb
UWA UWACE...19
Batul Mamman💖
***
Duk kokarinsa babu abin da Abbati ya iya karantowa a fuskar Farha. Abu daya kacal ya lura dashi. Wannan annurin na fuskarta yayinda take gaisawa da Baaba Mari ya dauke. Banda shi da ya san da zamansa ma babu wanda zai lura da cewa yanzu ta koma kadaran kadahan. Babu alamun bakinciki ko fushi, babu alamar tambaya ko neman karin bayani. Irin abin nan ne kawai da mutum zai iya dangantawa da dauke wuta. Iya nacinsa na takaitaccen lokaci ya yi domin ta kalli inda yake amma kamar tana sane ta fuskanci wadda yake tunanin ita ma kanwarta ce tana yi mata magana. Fita ya yi jikinsa kamar anyi masa duka ya tsaya a jikin motar ya kira Munzali.
*
Yana zaune baki bude yana ganin ikon Allah. Fruits Mama Nasima ta yanko masa ta kuma tura Mardiyya yi masa girki. Ya rage su biyu a falon ta zauna a kujerar dake fuskantar shi jikinta babu lullubi har lokacin sai farincikinta da yaki boyuwa.
"Wato kuna ta shan soyayya ban sani ba. Gashi kun dace. M da M. Zai yi kyau kuwa a soveniya (souvenir) da katin biki. Irin a saka katuwar M daya sai a jona karashen sunayenku." 'Yar damuwa ya gani a fuskarta ta ce wai yaushe za ka turo ne? Kai ba yaro baq. A shekarun nan naka kana bukatar iyali domin cikar kamala. Bana so ka sami shakku a zuciyarka game da Mardiyya. Na horata sosai da aikin gida. Ko kusa ban sangarta ta ba don ita kadai gareni. Girki, tsafta, kwalliya duka ta kware. Kuma ina da yakinin sauran mu'amala ma ba za ta bani kunya ba. Tun tana da kananun shekaru nake gyara abata." Ta kare magana tana dage masa gira gami da guntuwar dariyar shakiyanci.
Ita ke magana shi ne da kunya. Da za ace masa akwai ranar dai zai so kasa ta bude ya shige ciki don kunya tsaf zai karyata harda rantsuwa ma. Sai gashi a bagas ya gamu da gamonsa.
"Ahhhhhh. Wayyoooo. Cikinaaaa"
Mardiyya ta kwala ihu iya karfinta bayan ta fahimci wace irin hira Mamanta ta dauko. Haka kawai ta matso jikin kofa da taji ana ambaton kwalliya. Sai gata tana zazzare idanu da jin abin da Mama Nasima ke fada. Kunya ta kama ta sai dai babu muhallin biye mata. Idan bata dakatar da hirar nan ba to gaskiya bata san inda za ta tsaya ba. Ita shaida ce kakarta Gwaggo Ladidi ma idan suna wata hirar da 'ya'yanta mata sai ka nemi gudu. Ido ne ya bude tun da jajayen sawu ga rashin ilimin kirki. Sai suyi ta tafka rashin kunyarsu a tunaninsu wayewa ce.
Tare da Mama Nasiman suka isa kitchen din, don yadda tayi karar dole mutum ya firgita. Shame-shame suka sameta a kasa.
"Mardiyya lafiya? Me ya sami cikin naki?"
Mama Nasima ke tambayarta cikin tashin hankali. Ta dago kanta ta dora a cinya tana salati. Ita kuwa Mardiyya ta cigaba da murkususu tana nuna ciki.
"Mama ciwon cikina ne ya tashi."
Mama Nasima ta bita da kallon mamaki
"Dama kina da ciwon ciki ne? Ko menses kike."
Yadda Mardiyya ta kwabe fuska kamar tayi kuka ya kusa saka Munzali dariya. Daga bakin kofa ya tsaya saboda suna hada ido ya gane ciwon karya take yi. Ta bashi tausayi sosai gami da dariyar diramarsu ita da mahaifiyarta.
Juyo da fuskar Mardiyya tayi suna fuskantar juna hankalinta tamkar ya bar jikinta. Ira kenan 'yar, tsoka daya a miya.
"Mardiyya kalle ni nan. Na ce menses ne? Naga baki taba ciwon mara mai tsananin wannan ba."
Gara ace al'ada sau dubu da a ce menses saboda yadda ta tsani kalmar. Amma yanzu sau biyu tana jinta kuma a gaban mutumin da basu yiwa wani sanin kirki ba. Kai ta gyada don ta barta da tambayar. Sannan ta ce akwai maganin da take sha a dakinta dake can bangarensu. Mama Nasima ta mike a sukwane ta fice zuwa neman magani.
"Sai ki tashi tunda ta tafi" cewar Munzali yana dariya a hankali.
Mardiyya ta cukule fuska "dole kayi dariya tunda ka sani karya." Tana magana suna komawa falon "ka zo ka tafi don Allah kafin ta dawo."
"Korata kike yi?" Ya furta bayan ya mayar da fuskarsa kalar ban tausayi.
"Eh"
Zamansa ya yi yana danna waya "babu inda zani tunda ba ke ki ka gayyatoni ba."
A kujera mafi kusa dashi ta zauna idonta yana yawo tsakanin fuskarsa da kofa. Kuka take neman yi.
"Don Allah ka tafi. Wallahi bana jindadin abin da Mama take yi a gabanka. Da wuya ka dinga ganin mutumcinta."
"Mardiyya"
Munzali ya kira sunanta na gaskiya cike da kulawar da bai san daga ina ya samota ba. Kallonsa kawai tayi ta dauke kai saboda jin nauyi a kowacce gabar jikinta.
"Kar ki aibata mahaifiyarki. Damu da iyayenmu babu wanda yake cikakken dan Adam wanda baya kuskure. Suna hakuri damu, muna hakuri dasu. A tsakanin wannan hakurin ake neman balance don a zauna lafiya."
Wani irin rauni ne ya ziyarceta. Tana son mahaifiyarta kuma tana kyamar halayyarta. Duk da haka bata taba jin a ranta wai za ta iya jin kunyar nunawa duniya tsatsonta ba. Abin da Allah Ya baka shi ne naka, dan Adam mai Hamdala shi ne zai kokarin rike tasa kyautar da daraja.
"To kai ta yaya ka nemi balance din?"
"Yanzu nake neman samu albarkacin amini kuma dan uwa nagari Abbati. Da fari da rashin biyayya, rashin girmamawa da nesanta kaina da mahaifiyata na fara sai naga ba a dace ba. Rayuwar taki albarka yadda nake muradi."
Dokin jin yadda yake yi yanzu da tsoron dawowar Mama Nasima yasa ta cewa "yanzu fa? Me kake yi yanzu?"
"Tare zamu nemo Diamond girl. Daga yau sai mu zama abokan shawarar juna game da matan da ya kamata su fi kowa daraja a idanunmu."
Murmushi suka yiwa juna. Mardiyya ta kasa jurewa kallon da yake mata ta tashi da sauri ta shige inda yake tunanin hanyar daki ne. Wayar yaji kuma ya san Abbati ne sai bai kirata kamar yadda ya yi niyya ba. Labarin bakuwarsu ya bashi da yadda Farha tayi bayan Deluwa ta ce matarsa ce.
*
"Subhanallahi. Please kar ka damu. Dama dole ta sani. Zamu bata hakurin jinkirin da aka samu bata ji da wuri ba. Bari dai na fito muje. Amma ni wallahi ban san ina ne hanyar tashar Kawo ba. Ko Suhaib na kusa ka fada masa ya sake taimaka mana?"
Abbati ya girgiza kai kamar Munzali na gabansa. Kansa ya dauki chaji mai wuyar sauka. Zuwan Hanne ba tare da izininsa ba ko kadan bai yi masa ciwo kamar wayar da aka yi masa akan abin da tayi a tashar ba. Wane mai hankalin ne zai so ya amsa sunan mijin ballagaza? Aikin Hanne kenan! Yayi nasa kokarin a kanta tunda har makarantar yaki da jahilci ita ma ya kaita kamar yadda suka yi shi da Munzali. Bata koyo komai ba banda danna waya da yi masa bincike kamar wakiliyar EFCC. Bai manta silar aurensu ba shi yasa bai raba matsayinta da na takalmin kaza ba. Yana can duniyar tunani Munzali ya isko shi.
"Mutumina muje ko. Da kwatance ba za mu bata hanya ba in sha Allahu."
Mukullin Abbati ya mikawa Munzali ya zagaya daya barin zai shiga sai ga Sauda ta fito da sauri. Ba don Mami tayi magana a gaban su Baaba Mari ba da ba za ta zo ba. Ita bata yarda ba ta fara taya yayarta kishi ne akan matar Abbati.
"Uhmm dama Mami ta ce na tambayeku ko kun san tashar daga nan."
"Daga ko ina ma bamu sani ba." Munzali ya bata amsa.
"To ku jira"
Komawa tayi ta fadawa Mami Khadija amsarsu.
"Farha idan motarku da mai kuyi gaba ke da Sauda sai su biyoku a baya." (Mami Khadija ko tana hauka ba za ta yarda ace ta turasu a mota daya alhalin bata sansu ba. Sannan kuma gasu maza. Yadda take kaffa kaffa da 'yan matanta)
Sauda ta tafi bangarensu inda suke ajiye mukullin tasu motar. Guda daya ce Alh. Tahir ya saya musu saboda uzurinsu musamman na makaranta. Farha kadai ya yarda ta tuka kafin su ma su gama secondary.
A can ta hadu da Mama Nasima ta fito daga dakin Mardiyya duk ta hada zufa.
"Yauwa Sauda zo don Allah ki tayani duba maganin Mardiyya. Gata can ba yadda take ciwon ciki ya murda mata. Nayi neman har na gaji"
Kana ganinka ka san tana tare da damuwa. Idanunta sun yi zuru saboda firgici.
"Wane irin magani ne?" Sauda ta tambayeta da mamaki.
"Ciwon ciki ne dai ta ce yana yawan tashi."
Sauda sai ta shiga suka dan bincika babu. Ita ta kawo shawarar su tafi asibiti. Ta dauki mukullin motar ta kaiwa Farha sannan ta fadawa Mami Khadija cewa su Mama Nasima za ta bi. Ta bata goyon baya suka fita tare domin ita ma ta duba Mardiyyan.
"Kuyi hakuri an tsayar daku. 'Yar uwarsu ce babu lafiya. Ga Farha nan zata kaiku har