Showing 120001 words to 123000 words out of 242549 words
basu da yawa shi ne aka ramawa kura. Guda biyun ta bashi ya tafi yana murna. Suhaib ya kaiwa domin su ji dadin karbar gayyatar shi kuma ya kira ya fada musu.
*
Kafin lokacin masallaci dama Munzali yake da nufin zuwa dauko Qibdiyya yau. Tunanin zuwansu dinner din gashi Kande bata dawo ba sai washegari sai ya kira Abbati ya fada masa.
"Kada ma ka fara tunanin soke daukota zuwa gobe. Ko so kake a fara ganin kamar akwai uzurin da za ka dinga fifitawa akanta?" Cewar Abbati yana tsaye a cikin wani bakery. Duk wani cake da ya san tana so ya saya yana jiran turn dinsa ya biya.
Munzali ya sha kunu kamar suna tare ya ce "Ka gama kashewa yayarmu murya ni kuma ka dinga yi min masifa. Ya yi kyau!"
Daga inda Abbati yake har hasko fuskar tasa ya yi. Dariya ya dinga yi masa,
"Ai kaine da wani zance kawai don za ka je tsara budurwa baka son babyna ta bata show."
Shi ma dariyar ya yi "Dadin abun kaima tsarin nan dai zaka je. Tun wuri na fada maka idan mun tafi da ita a wurinka zata zauna ku kare kalau."
Da haka suka yi sallama. Munzali ya kira Mardiyya shi kuma Abbati gudun kada Munzali ya shashantar da dauko Qibdiyyan yau ya kira Zakiyya ya ce mata yana hanya.
Abu ne da suka saba dama. A wajen kaita gidan ko daukota daya daga cikinsu ke zuwa ko suje tare. Tunda Zakiyya ta san da tafiyar tun kwanaki biyu ta riga ta hada mata 'yan kayanta. A can dinma tana da kaya domin dakinta guda. Hatta uniform akwai koda watarana dalili zai sa ba a mayar da ita da wuri ba. Fitowa tayi daga daki tana kwala mata kira domin ta zo ta shiryata.
Duk inda take tunanin samunta ta duba babu Qibdiyya babu dalilinta. Hankalinta tuni ya fara tashi tunda ta tabbatar tare suka shigo gidan daga gidan kitso. Dakin mahaifiyarta ta sake shiga ta gama tashin hankalinta.
"Umma kamar fa bata gidan nan. Kuma ga kofar gida a rufe."
Umman tasu kanwa ga Asabe ta mike ita ma cikin firgici.
"Taso min Daddy ya zo ya fita a dubota. Ba har gara Munzali ya zo ace bata nan ba da wannan Abbatin."
Daddy din kanin Zakiyya ne. Hanyar dakinsa ta nufa da gudu gudu sai gashi tana kama kofar dakin shi ma ya kama ya bude. Wata mayyar jallabiya ce da ya nacewa a jikinsa yana murmushin yake. A gefensa kuwa Qibdiyya ce tayi tsilli tsilli da ido.
Dariyar da bata kai zuci ba Daddy ya yiwa yayarsa.
"Oji-oji (hide and seek) muka yi miki kuma baki kama mu da wuri ba ko Qibdiyya?" Ya furta yana tsare yarinyar 'yar shekara biyar da idanu.
"Eh" ta amsa babu wani kuzarin kirki a tare da ita.
Zakiyya haushi ya kamata duk bata kula da yanayin fuskokinsu masu dauke da labarai iri-iri ba. Hannunta tasa ta tankado kan Qibdiyya gabanta.
"Bana son irin wannan wasan, kada ki sake. Wuce muje ki canja kaya."
Tana sake turata Qibdiyya taji wani irin azababben ciwo ya tsirga ta tsakanin kafafunta.
"Washhh Mama."
Kafin Zakiyya ta gama juyowa har Daddy ya sunkuceta ya yi gaba.
"Daga yi miki wasa sai ki dinga hankadeta? In wasan ne ba kya so an daina yi dake."
"Ku wasa ya dama. Kayanta suna kam gado. Kayi sauri ka shiryata kafin azo daukarta, dama karatu nake Abbatin ya kirani."
Falo ta koma inda ta bar wayarta ta dauka ta cigaba da karanta novel din da aka yi update gabanin wayarsu da Abbati. Bata ji komai ba ta nutse cikin karatun ta bar kankanuwar 'yarta a hannun baligin namiji wai ya shiryata don kawai tana takamar shakikinta ne.
Ba yau ta fara ba. Son jiki ne ko sakaci? Allah Masani.
"Saka mata pant."
"Jeki Uncle Daddy ya yi miki wanka kafin na gama."
"Daddy shafa mata mai."
Aikin Zakiyya kenan. Idan ka bibiya kuma zaka samu ba wani abin kirki ne ya tsareta ba da har kula da tilon 'yarta yake yi mata wahala. Gashi bata son takura. A haka ma don anyi sa a Ummansu tana tsawatarwa duk lokacin da ta gani. Ta kan ce mata wannan zamani da uba yake haikewa 'yar cikinsa bau dace tana sakacin sakarwa kaninta ragamae Qibdiyya haka ba. Kowane dan Adam baya rasa makusa. Wannan dabi'ar ita ce ta Zakiyya.
To shi ma Daddy ba yau ya fara latse 'yar yayar tasa ba tare da barazana. Na yau dinne sai yaso wuce gona da iri. A cikin dakin daure fuska ya yi katamau yana yiwa Qibdiyya kallo mai ban tsoro.
"Kina fadawa wani zan sani kuma sai nasa wukata mai kaifi na yanka wuyan Daddy dinki (Munzali) da Papa (Abbati)."
Girgiza kai tayi da sauri tana mayar da kwallarta. Bidiyo din da yake nuna mata na yadda aka yanka wani mutum ta tuna ta runtse ido
"Allah ba zan fada ba."
"Ko kefa " Ya dan kalli jikinta "babu zafi ko?"
"Uhmm" ta ce da saurinta tana gyada kai.
"Good girl."
Abbati na zuwa Daddy ne ya rakota har mota suka gaisa sannan ya ja suka tafi. Abin mamaki a gareshi bai wuce rashin kuzari ko digo a tattare da Qibdiyya ba. Kafin su isa gida ta cure jikinta a bayan mota tayi bacci.
UWA UWACE...25
Batul Mamman💖
A kafada Abbati ya saba Qibdiyya daya hannun kuma ya dauko ledar kayan ciye ciyen da ya siyo mata suka shiga gida. Hanne tana zaune a falo tana kallo. Ganinsa da 'ya a hannu da kaya bai sa ta tashi ba balle ta rage masa wani abin. Sannu kawai ta ce masa ta mayar da idanunta kan tv.
Ko ta kanta bai bi ba ya shiga dakin da Baaba Mari ta zauna kafin su koma Kirikasamma ya kwantar da ita akan gado. Sama ya haye ya yi shirin masallaci ya sauko har lokacin Hanne bata motsa ba. Shi ya fara yi mata magana yana daura links. Sallahun kula da Qibdiyya ya bar mata ya fita.
Tsaki ta buga bayan taji tashin motarsa. Yadda ya bata mata rai shekaranjiya da tafiyarsu Baaba Mari ita ma ba zai ji dadinta ba kuwa. Sama ta haye ta bar Qibdiyyan har suka dawo. Allah Yasa Munzali gidansa ya shiga da tare zasu ji kukanta tana ta kiran Abbati da Anti Hanne. Ransa kuwa ya sosu ba kadan ba. Yana gama rarrashin ya kaita wurin Munzalin sannan ya dawo ya sameta rai a bace.
"Idan Qibdiyya 'yar cikinki ce haka zaki tafi ki barta ta tashi tana kuka?"
Baki ta murguda bata san ya gani ba ta bashi amsa da rashin kunya.
"Sai kaji in da dadi mutum ya nemi abu aki yi masa bayan akwai halin yin hakan."
Ya fara gane inda ta dosa amma ya kyaleta ta cigaba da magana domin ya tabbatar. Zancen shekaranjiyan ne dai ta tayar. Tunda Baaba Mari ta zo tayi 'yan kwanaki ita ma sai tata uwar ta zo.
"Ai uwa bata fi uwa ba"
Daure fuska ya yi da takaicin halayenta.
"Gwaggo Jumai ba kishiyar Baaba bace kina jina. Haka kawai idan ta so zuwa gidan nan ba zan hana ba. Amma ba zan yarda ki tsiro min da abin da zai iya zama rigima a gaba ba. Zuwan daya ba zai zama dalilin zuwan daya ba."
"To kuwa wallahi...."
Dan murmushi ya yi sannan ya katseta "ki cigaba da biyewa Gwaggo Deluwa ta kashe miki aure."
Gabanta ne ya dan fadi saboda bai yi kuskure ba. Gwaggo Deluwa ce zugata akan cewa ya kamata innarta ta zo ta kwashi romon arzikin gidan. Abbati sai ya sami damar cigaba da fadin abin da yake jin zai taimaka masa ya dan dawo da ita kan hanya.
"Ki bar ganin tana ta cewa ta samarwa 'Yashshafa miji a Kaduna. Idan yaki aurenta kin san ni din dai za a kuma kawowa. Shi yasa take so tayi sharae fage yadda idan can bai samu ba nan din ba za ki kawo musu matsala ba."
"Cabdijan" ta furta cikin bacin rai "amma Gwaggo Deluwa ta raina min...."
Bai tsaya jin sauran sababin nata ba ya sake ficewa yana murmushi. Sai da suka yi magariba suka tashi shiryawa zuwa dinar. Hanne da rawar jiki yana cewa ta shirya Qibdiyya ta kamata tayi mata wanka. Wurin tsarki ne ta kula tana kanne ido sai ta alakanta hakan da zafin ruwan. Tsaf ta shiryata cikin riga da skirt na lace tayi mata dauri. 'Yar kwalliyar da taso yi mata da ja gira a hada da jambaki da foundation ba tun yau Abbati ya hana ba. Ya kan ce mata komai da lokacinsa. A bar yarinya taci kuruciyarta idan ta isa adon ba sai an koya mata ba.
A mota kwanciya Qibdiyya tayi a jikin Munzali, Abbati kuma yana tuki.
"Wai ni baka ga canji a wurin Mamana ba? Dan taba wuyanta ko zazabi take yi? Shirun ya yi yawa."
Dago kanta Munzali ya yi ya taba wuyan da goshi.
"Babyn Daddy akwai inda yake miki ciwo?"
Kamar ta nuna masa sai ta tuna kashedi ta fasa. Yanzu ma dai da sauki sosai tunda bai yi mata mai gabadayan ba. Firgici ne ya zauna mata a rai ta rasa walwala saboda bidiyo din da Daddy ya nuna mata. Kai ta girgiza ta sake kwanciya.
Gajeren tsaki Abbati ya yi yana cewa "ka gani ta sake kwanciya ko? Kawai kar mu dade mu biya a dubata. Ni dama saboda shirun ne ma nace mu fito da ita ko ta sha iska."
***
"Nifa ba soyayya muke ba" Mardiyya ta sake nanatawa Farha da Sauda mai bada labari.
"Shi yasa naji yana kiranki Diamond girl" Sauda ta fada tana harararta ganin za ta raina musu wayo.
"Saboda a diamond plaza muka hadu ko kun manta?"
Sauda bata hakura ba ta sake cewa "Amma ai ke ya fadawa zasu zo da 'yarsu."
"Saboda yaga kamar na fiki son yara ne."
"Tunda a rubuce yake a goshi ba! Ke dai idan biki ya tashi kada ma ki nemeni don ba zan miki komai ba tunda tsakaninmu an fara boye boye."
Farha dariya tayi yadda suke hararar juna kowacce tana son a yarda da zancenta. Su ukun sanye suke da skirt da riga na lace fari da purple. Kowacce kamar sauran 'ya'yan dangi taci gwaggwaronta da kwalliya irin ta zamani saisa-saisa. Dokar Maminsu kuma ta tabbata a kansu don bata yarje musu yawo babu lullubi ba saboda biki.
"Duk wadda ta ajiye tarbiyarta tayi yadda take so a bayan idona Allah na kallonta."
Da haka ta kashe musu jiki domin da fari har Sauda da Mardiyya sun fara son bin sahun 'yan mata 'yan uwansu. Da suka kiyaye mutumcinsu kuwa sai suka dinga jinsu a sama a wurin bikin sabanin marasa mayafi. Sun yi matukar kyau kamar a daukesu. Hankalinsu kwance basu da damuwar komai. Jiddo da Mama Nasima ma duka sun zo saboda biki dai na kanin Alh. Tahir ne ko bai auri Mami Khadija ba.
Inda suka zauna ma dai taron 'yan uwa ne daga masu sabbin goyo sai marasa aure anata hira. Kiran Abbati da sanarwa Farha da ya yi cewa sun iso ya kara karfin shewarsu.
"Farha da saurayi? Lallai yau zamu yi farin gani a wurin nan." Cewar wata sa'arta wadda a yanzu take da ciki na biyu.
Idanu suka dawo gareta kowa na fadin albarkacin bakinsa. Abin ne da mamaki saboda duk lokacin da ake haduwa irin haka ana hirar samar sai dai tayi murmushi. Idanu suka saka mata suna jiran ganin waye ya ciri tuta. 'Yar kwallarta ta samu ta danne saboda ganin yadda suke ta murna. A baya din ma basu san babu bane ba wai tana boye shi ba.
Zuga guda ce ta biyo su suka tsaya daga bakin kofar shiga inda ake nuna kati ana jiran su shigo da bakinsu. Farha da ta fisu tsiya sai ta fadawa Lilu ta ce ya shigo dasu. Idan akwai saukin mutane ma ya fara kaisu su gaisa da Mami Khadija. Shi kuma sai ya kira Suhaib saboda katinansu suna wurinsa.
*
Ba tare da wata shan wahala ba Danliti ya iso venue din da Anti Jiddo ta fada masa ya zo ya sameta. Yau bai yi karambanin daukar motar garejinsu ba saboda ta san ko shi waye. Gara ma ya nuna mata fakirancinsa da kyau domin ta kara sakar masa bakin jaka. Yana sauka daga adaidaita sahu ya kirata ta fito waje. Ba karamar kwalliya tasha ba. Mayafinta a kafada daya ta rataya shi sai karamar jaka a daya hannun. Ba ciki take son su shiga ba. Hasali ma idan ta sami faraga so take su dan zaga hotel kafin a tashi daga taron. Shi yasa ma ta san yadda tayi Alh. Tahir ya yarda aka taho da motarta. Dan kanwarsa ne ya tuko kuma ana zuwa ta karbe mukullinta.
(ZINA kenan. Ma'abocinta baya taba cin bulus. Da wuya ne idan bata dawo jikinsa yadda zai yi masa ciwo ba.)
Kasa dauke ido daga kallonta Danliti ya yi har ta iso tana girgiza masa jiki.
"Ka san kana so amma nake turo maka hotuna kana ja min aji" Jiddo ta furta tana kashe masa idanu.
Busassun labbansa ya lasa cike da shu'umanci a zuciyarsa ya ce "ba so ne bana yi ba karfina kawai aka fi."
A kagauce ta ce "Akwai inda zamu iya zuwa kurkusa don na dawo da wuri?"
Da ka ya amsa mata saboda irin kallon da take masa da motsin jikinta duk sun hargitsa masa lissafi.
Danna remote tayi motarta dake gefe tayi kara alamun lock din ya bude. Da ido ta nunawa Danliti ya shiga tana wani irin kakkashe masa idanu kamar wadda ta sha kayan maye.
Danliti ya kama hannun kofa zai bude kenan Suhaib ya isko su. Ta gabansa Anti Jiddo ta fito tana waya da Danliti ya zo bata kula dashi ba. Fitowarsa kenan zai shigo dasu Munzali. Uzurinsa yaso karasawa da ta wuce sai dai karairayar da ya hango tana yi da girgiza jiki ya matukar kada hanjinsa. Yau ko mahaifinsa ne baya jin akwai dacewar tayi haka a gabansa a waje irin wannan ba. Jikinsa ya yi matukar sanyi da yaga irin kallon da Danlitin yake binta dashi shi ma. Maganganunsa basu isa kunnuwansa ba sai dai ganin suna neman shiga mota ya karar da hakurinsa. Baya son dasa musu zargi bisa hasashe amma duk da haka baya jin zai iya dauke kai.
"Anti Jiddo ina zuwa haka ana ta nemanki a ciki."
Sakin mukullin tayi ba shiri sakamakon gumin da ya karyo mata ba shiri har tafin hannu. Daburcewa tayi gabadayanta ta juyo.
"Me ya fito da kai ana tsakar taro Suhaib?"
Kallon tuhuma ya yi musu duk suka ji kamar ya yi musu tsirara a waje.
"Baki gareni zan shiga dasu."
"Oh...to sai ka dawo." Anti Jiddo ta ce da murmushin yake tana fatan ba zai yiwa Danliti magana ba.
"Kai kuma fa?" Ya ce da Danliti fuska a murtuke.
"Am, ammm"
Wani mugun kallo Suhaib ya dinga yi masa sai ya rasa abin fada duk kwarewarsa a karya. Anti Jiddo da ta san koma meye ita ce a ruwa sai ta ce makanike ne zai duba mata mota.
"Waye ya turo miki shi?"
Tambayar ta fito babu digon fara'a a fuskar Suhaib gareta.
"Kawata. Eh kawata ce ta turo shi." Ta amsa da rawar murya.
Hannu kawai ya mika mata "bani mukullin naki. Idan na raka bakin ciki sai na bi shi. Gani ga Lilu ace kin tafi gareji a daren nan Abba ma ba zai barmu ba."
Jikinta sanyi ya yi ga wani irin bacin rai da yake cinta. Danliti zuciyarsa kamar ta fado don tsoro. A haka ya daure ya ce,
"Kawo na tayar na fara dubawa kafin ka dawo. Idan dole sai mun je garejin zan gani."
Shiga motar ya yi ya tayar ya shiga danna totir ya leko da kansa da ya jike da gumi.
"Ina jin ma ba sai mun je ba." Ya dubi Anti Jiddo "Hajiya bakin mai kawai za ki canja."
A firgice ya mikawa Suhaib mukullin ya kara gaba ko waige babu. Suhaib ma sai ya bawa Anti Jiddo ya tafi inda su Abbati suka yi parking ko kallon kirki bai kara yi mata ba. Kwafa kawai tayi tana tsine masa a ranta. Uban da ya haife shi ma yawo yake bata ga wanda zai hanata more rayuwarta ba.
*
Gaban Farha ne ya fadi da su Abbati suka shigo hall din. Bata jin rashin samun masoyi da wuri ne yasa take ganin ya burgeta a komai. Yanzu kam shigarsa take kallo. Kayansu iri daya da Munzali. Yadi ne ruwan toka anyi musu dinki mai gajeren hannu. Kawunansu da hula ita ma iri daya babu bambanci. Wurinsu Mami Khadija Suhaib ya fara kaisu suka gaisheta. Lilu yana wurin ya dauki Qibdiyya wadda take makale a hannun Abbati yana tambayarta sunanta.
"Lilu sarkin yara. Tun yanzu zan fara yi maka addu'ar bibbiyu da uku uku." Cewar matar wani kanin Mami din.
"Ai kuwa matata ba sai ta dauko mai raino ba Anti. Ta dauki daya na dauki daya."
Mami Khadija ta girgiza kai tana kiransa mara kunya su Abbati suka yi murmushi. Iyayensa dake wurin kuwa dariya suka dinga yi masa anata tuna kuruciyarsa da yadda yake daukar musu yara yana musu wasa.
"Kaisu su zauna mana" Mami ta ce da Suhaib wanda ya kafe Anti Jiddo da ido a inda take zaune.
Bayan sun zauna Lilu ya kira Farha ya kwatanta mata inda suka zauna. Tare suka mike da yan uwanta har mutum hudu. Duk yadda taso sai da suka bi bayanta suna dariya.
"Gashi can mai sajen" Sauda ta nuna musu shi.
Kan kace meye wannan sun riga Farha isa. Kunya ta kamata da taji suna ta yi masa tsiya.
"Allah banga laifinki ba Farha. Wannan da ya bayyana da wuri ai da tuni an miki kwace." Wata mai baki ta fada.
Abbati kuwa sai ya kada baki ya ce "ba zan kwato ba fa. Ni nan sai Ya Farha."
Kafin kowa ya farga Suhaib ya bar wurin saboda wata irin shewa da suka saka. An tara masu baki ne a wurin wadanda duk taro sune iyayen zance. Farha kamar ta nutse a kasa ta juya zata bar wurin.
" 'Yan uwanmu kunga ban gama shigar da kaina ba kuna neman korar min ita ko Mun...."
Yana waigawa babu alamun Munzali a wurin sai Lilu da yake bawa Qibdiyya meatpie. Ashe wurin zama daban ya ce Mardiyya ta sama musu tun kafin su shigo. 'Yan matan suka gama dariyarsu suka watse. Ya rage su hudu har Qibdiyya.
Lilu ma