Showing 222001 words to 225000 words out of 242549 words

Chapter 75 - UWA UWACE COMPLETE BOOK by Fatty Noor.txt

09 Oct 2025

3356

ko kara cewa komai bayan sun yi shiru sai Munzali ya tambaya ko zasu iya tafiya domin yana son ya kai Abbati asibiti.

DPO ya cike takardun da suka dace wadanda suka wanke Abbati daga zargi ya ce zasu iya tafiya.

Gabadayansu tare suka firfito waje. Jikkunan su Asabe a sanyaye. Yayinda wadanda basu san abin da aka tattauna a ciki ba suke ta farinciki.

Kasancewar Hanne tana wurin, Farha bata yi gigin matsowa inda ake ta yiwa Abbati murnar kubuta ba. Amma rashin samun yin hakan ya bayyana tsantsar damuwar da Mami Khadija tayi saurin fahimta a tattare da ita. Tausayi taji ta bata. Tunda bata amsa sunan matarsa ba tabbas bai dace tayi abin da zai sosa ran matar tasa a yanayin da ake ciki ba. A wani bangaren na zuciyarta kuma sai ta shiga wasiwasi akan al'amuran da suka faru a yau. Tabbas idan ta ce babu zargin lauje cikin nadi a game da su waye Abbati da Munzali ta yiwa kanta karya. Babbar damuwarta bata wuce alakarsu da wanda ya sace Qibdiyya da kuma dalilinsa na sace ta ba. Alhalin da kunnuwansu duka sun ji daga bakin Comared cewa kawali ne na kusoshin kasar nan. Abbati ya ce shi almajiri ne amma ji gidansa da irin motocinsu. Shin ko dai su ma kawalan ne???

"Mami?"

Firgigit ta dawo daga duniyar tunanin da take sakamakon tabata da kiran sunanta da Lilu yayi.

"Na bude motar ke muke jira"

Kallon motar tasu tayi taga ashe duk sun shiga bayan sun yi sallama dasu Abbati. Ta shiga baya kusa da Suhaib ta zauna. Sun iso kusa da gate din station din Abbati da ya rufewa Baaba Mari kofar motar Munzali ya tari motar tasu kafin su fita. Saitin tagar gaba inda Farha take zaune ya tsaya amma idanunsa baya suke fuskanta wurin Mami Khadija.

"Mami ku yi hakuri da abin da ya faru dazu da ma damuwar da muka janyo muku yanzu."

Murmushi tayi tana mai kara yabawa da sanyin halinsa.
"Ka bar wannan magana Abbati ta riga ta wuce. Allah Ya tsare gaba. Gara ku samu ku tafi don ka ga likita da wuri."

"In sha Allahu. Nagode..." Ya kallo Suhaib da Lilu ya sake cewa "Nagode"

Farha ce kadai bai yiwa magana ba. Sai murmushi kadai saboda idon Mami. Waje suka yi da motar suka bi bayan Comared wanda yake tare da Alh. Tahir. Kuma shi zai yi musu jagora su koma gida.

A ranar Asabe gidan Lami ta wuce. Bata iya komawa gida ba sannan ba za ta iya fuskantar Munzali ba. Duniyar ce kaf ta daina yi mata dadi. Ta rasa tudun dafawa. Yau ko mashi aka caka mata a zuci iyakar ciwon da za ta ji kenan. Dole bahaushe yake cewa gaskiya tana da daci. Maganganun da taji daga bakin danta basu yi mata dadi ba ko kusa. Amma cikinsu babu karya. Idan Alh. Rabi'u halinsa ne tsallake iyalinsa ya barsu suyi ta kansu da zarar sun fito duniya, ita mene ne nata uzurin? Bata taka rawarta ta uwa a wurin 'ya'yanta ba. Duk wata alamar mace ko uwa ta gari babu a tattare da ita. Kaiconta! Ta ina za ta fara?

Alh. Rabi'u da ya koma gida shi kuma ko runtsawa bai iya yi ba. Dakinsa ya shige ya rufe kofa tun dawowarsa. Gabanin magariba Innayo da su Uwani suka shirya tafiya asibiti dubo Abbas. Aikin nasa karfe bakwai ne da an idar da sallah. Ta cikin dakin ya iya cewa su gaishe su.

Yanayinsa da rashin dawowar Asabe ya sanyata shiga damuwa. Damuwa ba akansu ba. Tunaninta ya tafi kan Munzali da take da yakinin akwai abin da yake faruwa dashi. Da kuma Qibdiyya. Aikin da aka shiga da Abbas ne yasa kowa tsammanin shi ne damuwarta. Shi yasa babu wanda ya dameta da tambaya. Tare dasu Hasiya suka zauna har aka fito dashi suka tabbatar lafiyarsa kalau sannan kowa ya kama hanyar gida.

***
Allah Ya yi dare, gari ya waye. Kowane mahaluki safiyarsa tana zuwa da fuskar da Allah Ya kaddara masa. Wani da dariya wani da kuka. Wani da damuwa wani kuma zuciyarsa fes. Shi bawa har kullum idan yana kwadayin dacewa sai ya zama mai karban rayuwa a duk halin ta zo masa.

A wannan rana wadda ta biyo rana mai tarihi a rayuwarsu Abbati, sun wayi gari da ciwon da jiya ta bar musu. Daga asibitin da Munzali ya kai Abbati, gida suka dawo dukkaninsu. Munzali ya fita ya nemi gidan abinci mai kyau ya sayo musu. Aka taru aka ci kamar ana tura magani. Hanne da Habu kadai ne suka zata shirun nasu yana da nasaba da dukan da aka yiwa Abbati. Ko da suka shishshiga daki domin bawa jiki hakkinsa, babu wanda ya runtsa sai mutum biyun can dai. Juye juye kowa ya dinga yi har aka kira assalatu. Kowa ya tashi kamar jira suke yi. Kafin takwas duk sun hallara a falo.

Zamansu ke da wuya maigadi ya shigo ya fadawa Munzali mahaifinsa yana nemansa. Dan murmushi ya sami kansa da yi domin ya tabbata yau dai neman da yake yi masa na damuwa da lamarinsa ne ba na neman kudi ba. Bai so ace karon farko da mahaifinsa zai damu haka dashi ya kasance akan abu makamancin wannan bane.

Bangaren Abbati ya ce a kawo shi. Ya zo ya zauna suka fara gaisawa da su Mal. Inuwa sai ga Asabe. Kayan jiya ne a jikinta da alamun rashin wanka ma. Tayi wuri wuri da ita gwanin ban tausayi.

"Hanne da Habu ku dan bamu wuri don Allah" cewar Mal. Sa'idu yana mai dubansu da mutuntawa.

Bambarakwai suka ga abin tunda bai saba lallaba dan kowa ba. Habu ya fita waje. Hanne kuma ta haye sama.

Munzali da Abbati suka zazzauna a kasa domin girmamawa ga iyayensu sannan Mal. Sa'idu ya soma magana cike da rauni.

"Ba don wannan al'amari mai muni bane wanda nake fatan daga yau kada a sake tayar da maganar ba, da sai in ce ina son sauran kannena su kasance a wannan zama."

Caraf maganar ta shiga kunnuwan Hanne. Kafafuwanta kuwa suka ci burki a bakin kofar shiga saman daga ciki. Sannu a hankali ta sakaya kofar ta sami wuri ta labe abinta.

Mal. Sa'idu ya cigaba da cewa "Allah shi ne shaida cewa ni Sa'idu ina kaunar 'yan uwana da 'ya'yansu da zuciya daya. A tawa wautar soyayya ce tasa nake juya kowa a gidan a matsayina na babba. Girman kai yasa nake ganin tunda gaba nake da kowa yi min biyayya wajibi ne. Sannan kowa bai san daidai ba sai ni kadai."

Ya dubi Baaba Mari, duba na mai jin nauyin wanda ya sabawa.
"Ki yi min aikin gafara duk da cewa na roka a makare. Tun ranar da ki ka dawo da gawar Sani a bayanki ya dace ace na zauna nayi tunanin halin da na jefamu a ciki. Son zuciya da girman kan da na ambata a baya suka sanya nake jin baki isa na janye kudurina ba. Yin haka tamkar kin yi galaba ne a kaina. Wannan dalilin yasa na kara tamke dammarar juya duk wani abu da kike tunanin kina da iko dashi. Musamman rayuwar Abbati. Sannan magana ta gaskiya, a duk lokacin da ki ka tayar da maganar son sannin sana'ar Abbati, nima ina kwadaituwa da haka. Na kan riski kaina cikin halin tunani da rashin bacci a wadannan lokuta domin nima a tsorace nake. Gudun kada abin da nake gudu ya tabbata yasa bana kaunar jin kina tayar da wannan zancen."

Bayan ya yi shiru Mal. Inuwa ya yi gyaran murya ya ce "laifi ba naka bane kai kadai Yaya. Harda mu da duka wadanda suke da alhakin sanyawa ko hana irin wannan na'u'in karatun. Hakika bana jin akwai wani mai sanya gaba gabas da zai kalubalanci tura 'ya'yan musulmi neman ilimin islama. To amma wannan hanya da aka biyo ba mai bullewa bace. A da can zan yarda idan aka ce mu iyaye maza muna tura yaranmu ne domin karatun Muhammadiya. Yawancin 'yan kasuwa da masu kudin da ake ji dasu a arewacin kasar nan akwai almajiranci a cikin tarihinsu. Su nemi ilimi su hada da koyon sana'a'o'in hannu komai kankantarsu. Yanzu kuwa babu tantama abin ya koma hanyar gujewa daukar nauyin da Allah Ya dora mana na 'ya'yanmu ne. Muna fakewa a bayan addini muna wulakanta rayuwar yaranmu. Ko babu komai duk mai roko baya daraja da kima a idon mutane. Zuciyarsa mutuwa take wurin jiran a bashi. Sannan ta kangare idan bai samu ba, ya dinga ganin laifin duka duniyar baki daya wurin kin nuna masa tausayi."

Baaba Mari dai bata ce komai ba sai sauraron Mal. Inuwa da Mal. Sa'idu suna bankado rawar da suka taka wurin bata rayuwar Abbati.

Munzali kuma ya tsurawa iyayensa ido. Da ya gaji da shirunsu ya kasa hakuri dole sai da ya yi magana.

"Baku ce komai ba Baba"

Asabe ta dukar da kai cikin jin nauyin kowa. Kunya da bakinciki sun mamaye zuciyarta. Tana mamakin yadda akayi ta makance da son duniya a baya har ta iya aikata wannan danyen aikin na sakaci da rayuwar 'ya'yanta.
"Me zan ce Munzali? Ina cike da kunya da nadama amma hakan ba zai canja komai ba. Laifinmu ni da mahaifinka yafi na kowa yawa a wurin nan. Bamu bar muku komai na tinkaho ba sai yawanku wanda ba don kun yi yunkuri da kanku ba da bai amfaneku da komai ba. Kalmar hakuri kadai bana jin za ta yi wani tasiri wurin rage maka radadin wannan al'amari"

Kalaminta ya zaburar da Alh. Rabi'u ga yin magana tana rufe bakinta.

"Mene ne aibun 'ya'yana? A iya sani na arziki ne yawan haihuwar domin kuwa rana gobe kiyama da irina Annabin Rahama zai yi alfahari"

Sallallahu alaihi wa sallam ya ji falon ya karade da ambata kafin muryar Munzali ta doki kunnuwansa cikin fushi.

"Ina abin alfaharin Baba? Waye cikinmu za ka iya fitarwa ka nuna hankali kwance har ma ka yi zaton za ayi alfahari da shi"

"Munzali meye haka ne?" Abbati ya ce dashi da alamun rashin jindadi.

" Gaskiyar da 'yan uwa, makota, surukai, abokai da mu kanmu 'ya'yansa muka kasa fada masa da wuri zan sanar da shi."

Ya mayar da hankalinsa ga Alh. Rabi'u wanda shi ma kallonsa yake da mamaki. Duk jahilcin da yake tunanin Munzali yana fama dashi bai yi tsammanin zai kasance cikin masu kokonto akan hadisan Ma'aiki ba. Hadisi ma irin wannan da ya dade da karade al'ummar da ya taso a cikinta.

"Baba idan anje lahirar za ka tsame wasu cikinmu ne ka nuna a matsayin 'ya'yanka?"

"Munzali kada ka yi sa6o mana" Asabe ta gargade shi ganin kamar zai saki layi.

"Allah Ya tsareni. Laifukana na baya ma sun isheni. Da yardar Allah ba zan sake afkawa zunubi da gangan ba. Ina dai so in ji shin da wa Baba zai yi alfahirin." Ya soma lissafi da yatsun hannunsa "Da 'yan dakin su Marigayiya A'i wadanda suka butulcewa hannun da ya ciccibi rayuwarsu a lokacin da basu da gata zai yi (Innayo)? Su suka fi morar lafiya da kuruciyarta amma saboda rashin uba tsayayye suka manta alkhairi. Ko Uwani da Zara da suka zabi kyama da tozarci ga mahaifiya kamar Innayo saboda gudun talauci? Ko ni da nafi kowa kazanta? Ko Bature da baka san a gidan wa yake kwana ba? Ko Lawisa dake canja samari kamar hula ta kuma gagara zaman gidanka? Ko Ummakati dake jin kunyar a hadata da ku a matsayin iyaye?"

Alh. Rabi'u shiru ba amsa sai muguwar kunyar da ta mamaye shi. Su Mal. Inuwa kuwa nauyi yasa suka ji ina ma kafin a fara maganar suka fita.

Idanu cike da kwalla Munzali ya dubi Baaba Mari ya ce "ki fada musu babu abin alfahiri a haihuwar da 'ya'ya basu sami kulawa, soyayya da kwab'a ba. Wadannan abubuwan masu saukin samuwa ne tunda babu ruwansu da da kudi ko talauci balle mutum ya dorawa halin rayuwa laifi. Annabi SAW ba haihuwar yuyuyu yace ayi ba. Me zai yi da taron al'ummar da fiye da rabinta suka zabi hanyar shaidan a matsayin tafarkin da zasu bi saboda rashin kulawar iyaye? Da kun sauke hakkina da na 'yan uwana da yake kanku da a yau iyayen Abbati ba suyi kukan fadawarsa harkar neman maza ba."

"Neman maza?" Hanne ta yiwa kanta tambayar a hankali tamkar tana jira wani ya sake fassara mata abin da ta riga ta sani. Ta sake maimaita kalmar tana cije lebe kafin kuma a hankali ta dora hannuwa a ka ta dinga nanata "na shiga uku" tana mai buga kafafunta a kasa a hankali don kada a ji. Matsanancin tsoro da fargabar da suka kama ta basu kawar mata da tunani ta yadda za ta so ta bayyana kanta a garesu kafin ta gama jin komai ba.

"Munzali yawan tada maganar nan ba shi da amfani tunda mai afkuwa ta afku. Ku yafi juna kai da iyayenka a cigaba da addu'a" cewar Mal. Sa'idu wanda hasashen halin da Alh. Rabi'u yake ciki na kunya yasa shi magana.

Shi kuwa Mal. Inuwa sai cewa ya yi "tada zancen akwai amfani Yaya Sa'idu. Ai zaman zubeben kwarya ake. A fitar da komai don kowa ya gane ta inda ya kuskure saboda a ji dadin gyarawa" idanun Munzali ya kalla dake cike da zallar bacin rai da tarin damuwa ya kuma kalli Asabe da Alh. Rabi'u "har yanzu da mu daku bamu makara ba. Dama ce muka samu domin shafe abin da ya faru da yaranmu. Don ko mun ki ko mun so, mu ma muna da namu kason a cikin zunubinsu tunda sakenmu ne sila. Musamman mu iyaye maza."

Asabe ta share hawaye ta ce "haka ne."

Shi kuwa Alh. Rabi'u daure fuska ya yi. Yadda bahaushe yakan ce gaskiya tana da daci to shi ma wannan ba karamin dacinta ya ji ba. Ba kuma ya jin zai bari a cigaba da fadarta balle tayi tasiri a zuciyarsa.
"Dakata Malam wa kake da suna?...wace irin magana ce wannan za ka ce muna da rabo a zunubinsu? Na san lokacin da ya fara ne? Ko ni na aike shi?

"Alhaji mene ne haka kuma?" Asabe ta furta ranta ya soma baci. Ko ba komai mahaifin Abbati bai cancanci irin wannan maganar ta rashin girmamawa ba.

Harararta ya yi kafin ya ce "dama tunda kika fara sauraron Innayo na soma kasa gane kanki. Idan ke kina maraba da a qaqaba miki zunubin irin mutanen Annabi Ludu ni bana so" ya mike tsaye yana baza babbar riga "ban san me ya dawo dani gidan nan ba. Na dai tabbata ba wannan maganar bace don wallahi da ba zan zo ba."

Mal. Inuwa ba shiri ya ce "kayi hakuri ban fada da wata manufa ba"

Munzali cije lebensa ya yi bayan ka karewa yanayin da Abbati ya shiga tunda Alh. Rabi'u ya soma magana. Takaicinsa ya karu da ya fahimci har yanzu akwai sauran gyara a lamarin mahaifinsa.

"Har a yanzu da nake kan siratsi irin wannan na rayuwa ba zan ji ni kamar kowane d'a mai iyaye ba?"

Asabe ta yi saurin cewa "Kada ka dauki maganganun Alhaji cikin fushi ya fada. Ka yafe mana don Allah"

"Kada Allah Yasa ya yafe. Aikin banza. Kaje ka gama iskancinka sannan ka dawo kana neman wanda za ka dorawa alhakin aikin da gabbanka suka aikata."

Su Mal. Sa'idu jiki duka ya yi sanyi. Ana neman gyara ga alamun sake tabarbarewar lamari ya taso.

Idan ya cigaba da sauraron mahaifinsa yana jin tabbas zuciyarsa sai tayi bugawar da take ta shirin yi tunda abubuwan nan suka soma faruwa. Shi yasa ya murje idanunsa ya fadi abin da yake ganin daidai ne.

"Idan ka so Baba ka cireni daga cikin 'ya'yanka. Wannan shi ne kadai nake jin abin da zai rabaka da amsa tambaya akan halin rayuwata..."

"Munzali mahaifinka ne fa..." Cewar Asabe tana jan hannunsa don ya kalleta"

"A suna ba. Na cinye kuruciyata sanda nake matukar bukatarsa ma na rayuwa balle yanzu"

"Munzali" Mal. Sa'idu da Baaba Mari suka kira shi kusan lokaci guda.

"Ku barshi ya nuna min iyakata. Dama can kawunanku yafi gani da gashi ba nawa ba"

"Ka taba yi min wani abu da zan gan ka da kimar da Allah Ya baka ta ubana..."

Da karfi Abbati ya ce "Munzali? Hauka kake ko me? Alhaji ne fa! Zo ka tafi gida gani nan zuwa."

Maganar da Munzali bai karasa ba kenan domin baya jin akwai ranar da Abbati zai saka shi ko ya hana shi ya kuma musantawa. Tuntuben bakin da ya yi akan Qibdiyya yake gudu kada Allah Yasa ya kuma maimaitawa.

Alh. Rabi'u da su Baaba Mari kowa ya ji kuma ya gani cewa Munzali bai bar fadi in fada da babansa ba sai da Abbati ya tsawatar. Hakan ya zama sanadin da Alh. Rabi'u ya sake samun abin aibata dan nasa.

Kujerar da ya tashi ya koma ya zauna a dofane yana kare musu kallo shi da Abbati.

"Ikon Mai Sama. Yanzu Munzali duk fadin wurin nan da jama'ar ciki babu wanda ya isa ya hanaka ka hanu sai wannan almajirin? Ka dubi tsabar idanuna ka dinga cab'a min magana son rai."

"Wallahi Abbati ya isa dani"

"Tabdijan!" Ya dubi su Mal. Inuwa "to Billahillazi da sake. Yaran nan basu tuba ba. Sannan ina tsammanin mu'amalarsu bata sauya ba tun kuruciya. Iya shegenku kuke yi har kwanan gobe." Ya kalli Asabe tana sharbar hawaye "ki adana kukanki don basu cancance shi ba. Alhaki kwikuyo gashi nan ya bi kan 'yarku ai. Shi ne don borin kunya ku ka tara mu a nan kuna karanta mana karya da gaskiya."

"A'uzubillahi" cewar Mal. Sa'idu yana mai duban mutuwar tsayen da Abbati da Munzali suka yi "Alhaji wace irin magana ce wannan? Ana kokarin kawo gyara ya za ka sake jifansu da abin da su da kansu suke neman tsari daga gareshi?"

"Baka ji me yake cewa ba? Wai fa ni yake fadawa cewa Abbati ya isa da shi. Koda yake ba damuwa zaku yi ba tunda wanda ya zaba akan mu iyayensa danku ne."

Asabe kuka kawai take yi. Yayinda Hanne ta sulale a kasa bakin kofar da take labe ta zauna. Wani sashe na zuciyarta yana kokarin karbar zancen Alh. Rabi'u. Domin alal hakika ta dade da rashin son alakarsu duba da yadda komai zasu yi sai sun tuntubi juna. Sutura wannan daidaikun ranaku ne suke bambantawa. Bata ganin kowa sai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login