Showing 99001 words to 102000 words out of 242549 words
yi a gabansa a bakin kofar shiga.
Gewayen fuskarta da dan karan hancin nan sun yi fari saboda hoda da foundation. Bakin da ya ci samosa kuma maiko ya zagaye shi. Idan ka kalleta dole kayi dariya ko baka so. Mami Khadija kanta girma ne kawai da sanin mutumcin bako ya hanata darawa. Sauda tayi a fakaice.
Idanunta ta zaro tana kalle-kalle a farfajiyar gidan ko za ta hango mahaifiyarta.
Lilu sai ya sauka daga matattakalar ya jira Suhaib ya karaso. Hab'a ya rike ya ce da yayansa,
"Ya Suhaib, yaushe watan Ramadan ya tsaya har goman farko ta wuce ban sani ba?"
"Ban gane ba."
"Kaga karfin hali" ya nuna 'Yashshafa "masu Iya duba-duba na gani a kofar Mami. Yanzu ashe har cikin falo suke shiga in sun zo. Shi ma ya hau next level kenan."
"Kai fa ka fiye shiririta. Gabadaya ban fahimci kalma daya cikin zantukanka ba."
Hannu ya mika masa yana dariyar da ta bawa 'Yashshafa haushi.
"Bani canji ko dari biyu ce in sallameta tukunna."
Sai lokacin Suhaib ya karasa hawa matattakalar ya kalleta. Duka ya kaiwa Lilu ya goce da sauri.
"Kanwar Abbati ce fa."
Da ya soma dariya sai da ya durkushe a wajen
"Wannan din? Kalleta da kyau Ya Suhaib 'yan Iya duba-duba ne."
Kyale shi Suhaib ya yi ya dubeta duk tayi wuru-wuri kamar wadda ta yiwa Sarki karya. Rangwadar nan ma babu alamunta. Dole Lilu ya cr tashe tazo. Kalmar ce ta bace masa yake ta cewa Iya duba-duba.
"Me ya fito dake?"
"Innata. Inna Deluwa nake nema."
Lilu ya sake kwashewa da dariya "kana ji fa Imna Deluwa take nema sannan ka ce ba ..."
"Ya isheka Lilu" Suhaib ya ce rai a bace. 'Yashshafa ya tambaya inda suka je har aka barta ita kadai.
"Wai wata ce bata da lafiya shi ne suka tafi da matar gidan nan" ta nuna bangaren Mami "cikin kuma sai nake jin kamar fatalwa tana shawagi. Sai shuu, shuu ake yi."
Shi ma mai fadan dariyar sai gashi yana yi harda kyakyatawa. Cikin sa'a kuwa sai ga su Mami sun fito. 'Yashshafa tana hangosu ta sauka da sauri. Gayun ya dawo da karfinsa tunda yanzu dai ta san ba gidan yan kan kai bane yadda ta soma hasashe.
"Mooomi. Moomii"
Hanjin cikin Deluwa a take ya bada wani irin sauti mai karfi. Tsinuwa ta shiga yarfawa aljanun 'Yashshafa wanda ta kwaso a makatantar kwana. Kunya kamar ta nutse. Sai kuma dole ta nema mata sauki domin indai sune suna wahalar da ita. Wani zubin sai tayi wata guda a gida ana tsakar zangon karatu.
"Me ki ka ce Shafa'a?" Ta riko hannayenta tana jin kamar ta fashe da kuka. Yanzu idan Sha'aib ya gujeta dole sai dai ta komawa Abbati.
'Yashshafa tayi murmushi a zatonta sunan ne ya burge Deluwa.
"Moomi."
Kowa yana ji ta ce ''oh ni 'yasu. Makaranki su rasa wurin tashi sai nan?"
"Makarai? Aljanu ne da ita?" Cewar Mami Khadija tana dan matsowa da taussyawa.
Lilu kuwa bayan Suhaib ya koma ya labe a firgice har yana tuntube. Cartoon ma baya kallon mai dodanni saboda kafirin tsoro bare kuma a ce gashi kusa da mai aljanu.
"A makarantar kwana ta kwaso su. Da alama yau bafillatani ne ya tashi kenan." Cewar Deluwa tana marairaicewa "Karshenta shanunsa ne suka bata ya fito nema. Banda haka me zai kai budurwa kiran wata Moomi ana zaune kalau?"
Lilu na jin tsoro amma bai hana shi dariya ba. Suhaib ya figi hannunsa saboda kallon da Mami Khadija tayi musu.
'Yashshafa tana son yiwa Deluwa bayani amma kuma Mami Khadija tana gefensu sai sannu take yi mata. Cikin falon suka koma Baaba Mari ta dinga girgiza kai. Tana ji tamkar ta janyo su Abbati su zo su bar gidan nan. Duk wani abu da zasu yi takama dashi na kare mutumci Deluwa ta zubar dashi. Bata ganin laifin 'Yashshafa domin kuwa yarinya ce mai bin maganar uwa sau da kafa. Duk abin da take yi bai wuce dorar da tarbiyar mahaifiyarta ba.
***
Manyan mata ne a zazzaune suna hira ana ciye ciye da shan lemuka. Manyan mata a matsayin arziki domin ba dukkansu bane masu shekaru. Babu 'yar kass da talatin dai cikinsu. Suturunsu da duk wani abu da yake jikinsu ya isa shaidar cewa suna ganiyar jin dadin rayuwa. Su tara ne kuma kowacce cikin lemon gabanta anyi masa hadi da kwaya daidai ra'ayinta. Wasu har sun fara tambele suna magana irin ta gogaggun 'yan duniya.
Wata hamshakiya da ta gama tumsewa ce ta mike tana wata irin rawa ta tsantsar rashin kamun kai. Suka tashi suna ihu aka soma tayata da liki.
"Ku barni in warwasa kawayena. Jiya na hadu da namijin da ya amsa sunansa ba irin dan rakiyar da nake aure ba..."
"Yeeeeyyyy"
Suka hau shewa ana dariya. Ta cigaba da cewa,
"Saurayin kanwata ne amma ina ganinsa na san dan harka ne. Bugu daya ya kawo min kansa hotel jiya."
Wata shewar ta cika falon da suke. Matar gidan wadda tayi musu masauki ta doki cinyar Jiddo tana dariya.
"Jiddo ta Alhaji Tahir bamu labarin naki mutumin. Ya ku ka kare da makaniken nan na Kano?"
Jiddo bata son a ce ta gaza. Ba yau suka fara harkokinsu ba. Yanzu dai duk sun chanja samari ne. Ta fada musu haduwarta da Danladi amma shiru bata labarta musu yadda aka kare ba.
"Sai zama na gaba za ku ji bayani."
"Amma dai ya turo miki hotuna bayan kin tura naki ko?"
Karya ta gillo musu mai jirwaye da gaskiya "ai tun bayan ganin hoton shegiyar nan a wayar Alhaji nake kaffa kaffa da wayata. Ya turo" sai ihu har sun fara matsowa ganin gulma ta kara da cewa "ina gani na goge."
Mata ne wadda kowacce take dauke da tabo ko bacin ran namiji. A nasu jahilcin da bacewar basirar ne suke tunanin wannan rayuwar ce za ta wanke musu zukata.
Neman matan Alh Tahir bai wani dami Jiddo ba. Amma rashin haihuwa ya mata karan tsaye. Tun tana nema har ta saduda. Duk tarin arzikinsa ba za ta tsira da komai ba sai tumunin takaba in ya mutu...a zatonta!
I just published "20" of my story "UWA UWACE...". https://my.w.tt/XYPGlg7tvcb
UWA UWACE...20
Batul Mamman💖
~Na san kuna hakuri. Hakurin dai zan yi ta baku akan rashin regular post. Nagode da bin rubutuna da kuke yi.
~Afuwan, wadda ta bamu award sunanta Maryam Muhammad Labaran, nayi kuskuren rubuta sunanta a sakon godiya da nayi.
This page is for you sister Habiba Haruna (Mantis Kitchen). Allah Ya kara lafiya.
***
Buba da Habi sun shigo gidan sun tarar da Deluwa cikin tashin hankali da fargabar abin da ya sami 'Yashshafa. Sai fada take tana nanatawa lalura ce kuma babu wanda yafi karfin ta kama shi. Talaka da maikudi. Dan kauye da dan birni babu inda ba a aljanu. Su gidan wani abokin Buba suka je. Mutumin da kansa ya zo ya tafi dasu tun kafin fitarsu Abbati. Habi tana jin abin da ya faru ta yi 'yar dariya. Kafadar 'Yashshafa ta dafa ta ce,
"Gwaggo Deluwa dake take fa. 'Yashshafa ko ba Momi kike nufi ba na 'yan gayu?"
'Yashshafa dai kamar ta nutse a kasa. Idanuwa duka a kanta. Dadinta daya ma wannan mai dariyar da yayansa basu biyosu ba. Mami Khadija ma dariyar tayi ta tashi ta shiga ciki za ta hado musu 'yar tsaraba, musamman ma dai 'yar budurwar nan mai abin dariya. Deluwa na ganin ta rufe kofar koriďo din da zai sada ta da dakinta ta kaiwa 'Yashshafa duka a baya rai duk a bace.
"Yanzu ke Momi din ne baki iya fada ba ki ka hau kukan saniya? Ca nake 'yar gidan Bibalo ba momi suke ce mata. Kawai sai mooo, mooo ake ji kamar saniya ta tsinke daga turkenta. Mtseww"
Buba da Habi suka bushe da dariya. Sallamar Farha suka ji Baaba Mari ta soma hamdala. Tafiya zasu yi yanzu yanzu in Allah Ya yarda. Bata bukatar Hanne ta zo ta bar nata abin fadin kamar na Deluwa da 'Yashshafa.
Kafin ta shigo tun a waje Lilu ya tareta ya bata labarin gamonsa da 'yar tashe. Dariya taso yi aka kuma bude gate Abbati ya shigo. Zuciyarta tayi wani irin dokawa mai wuyar fassara. Abin sai ya bata mamaki tunda a hanya ta san Munzali ke jan motar. Bata ga alamun Munzalin ba sai mace. Shi ne ta shige bangaren Mami da sauri don ma kada su hadu.
Ya kula da irin saurin da take yi wanda yake da nasaba da gudun haduwa da Hanne. Da gaskiyar Munzali dai da ya ce masa kishinsa take.
"Wai shiga ka ke so nayi na kirasu? To wane bangaren zan je?"
Hanne ta katse masa tunani da ta bude kofa za ta fita.
"Don Allah Hanne ki kama kanki. Kin san abubuwan da bana so. Kar ki gwada musu a gidan nan. Godiya kawai muka zo yi musu na kyautatar da suka yi mana."
Ya san halinta. Ko babu komai tsakaninsa da Farha ba zai so ta shiga tayi abin da zai zubar mata da kima a idonsu ba. Idan Farha rabonsa ce zai so ta shigo gidansa tana ganin mutumcin wadda ta tarar kuma kanwa gareshi.
"Naji" ta amsa da kunkuni.
Abbati dakatawa ya yi aka yi musu izinin shiga bayan ya yi sallama. Yana saka kafarsa Farha na shigewa wata kofa da yake tunanin kitchen ne. Murmushi kawai ya yi sannan aka gabatar da Hanne ga Mami. Anyi sa a Mami Khadija tayi mata kwarjini shi yasa ta gaisheta a mutumce.
Da kyar Mami Khadija ta samu suka ci abincin don sun matsu su tafi Kano a ranar. Basu dade suna jiran Munzali ba ya iso. Wurin Mardiyya ya fara zuwa suka yi sallama. Mama Nasima tana son tambayarsa alakarsa da abokan tafiyarsa da Mami Khadija amma yau ba hali. Ciwon karyar Mardiyya duk ya tsaya mata a rai.
Da zasu bar gidan Abbati ya so Farha ta fito ko yaya ya sake ganin fuskarta amma taki. Tsoron ganin matarsa take yi. A yadda ta ganshi hadadde dan gayu da wuya ace matarsa ba haka take ba. Idan kuwa haka ne kila sai ta raina kanta. Karshenta kuma tafiyar da bata taba irinta da wani d'a namiji ba ta sami tangarda. Gara dai kada ta kai kanta kallon abin da zai iya tada mata hankali.
***
Fitar su Hasiya ba dadewa Ale Gambo ya dawo. Salima na durkushe bakin murhu tana faman hura wutar itace cike da tashin hankali saboda daren da girkin ya yi. Gashi itacen danyene, yaki kamawa sai hayaki yake ta fitarwa. Daga bakin rariyarsu 'yan matanta ne suke wanke wanke.
Takunsa dif-dif tamkar wani doki mai ji da karfi ya shigo tsakar gidan. Sannu da zuwan da yaran suke yi masa ma bai ji ba sai kira yake kwalawa Salima. A razane ta fito domin da wuya suke wanyewa lafiya idan ya shigo a wannan yanayin. Cikin tsananin fushi da mamakin rainin da ya soma shiga tsakaninsu ya nuna ta da dan allinsa. Har wani haki yake ga feshin yawun da ya kan yi in yana magana cikin fushi.
"Hasiya na gani ta fita."
"Wani abin ne ya sameta?" Salima ta tambaye shi da firgici.
"Nawa ta baki?"
Maganar ta doketa sosai ba kuma don yau aka fara ba. Mijin aurenta ne, uban 'ya'yanta, wanda bai taba sanin darajarta ba yake yi mata wannan tambayar. Duk inda mutumci yake sun dade da yin hannun riga da Ale Gambo. Maganganunsu dasu Hasiya na dazu suka dawo mata. Tabbas zancen Ayaah gaskiya ne, babu wanda zai iya k'watar mata 'yanci a wannan yanayi sai ita da kanta. Tana jin tsoronsa har cikin kasusuwanta domin dukanta yake kamar ya sami gardi daidai dashi. Amma haka ta daure ta yatsina fuska tana magana cikin bacin rai ita ma.
"Ajiya ka bata ko bashi?"
Hagu da damansa ya waiga babu kowa sai yaransu suna kallonsa. Ya dawo da idonsa kanta tare da nuna kirjinsa.
"Wai dani kike Salima?"
Haka kawai taji kwarin gwiwa yana ciccibata. Daurin zaninta da yake neman kwancewa ta gyara tana cewa,
"Idan akwai wani Gambon a gidan nan bayan kai to dashi nake."
Jikinsa sai ya hau tsuma kamar mazari. A zatonsa ko hauka take bata isa ta maida masa magana haka ba. Daga shi har ita sun ji karar kwanukan wanke wanken domin a tsorace yaran suka mike. Sun tabbata sai ya dakar musu uwa. Hularsa ya cire ya yar a gefe. Kodaddiyar babbar rigarsa tabi bayanta.
"Baba kayi hakuri"
Ko kallonsu bai yi ba ya dubeta yana jinjina kai. A firgice take sosai amma tayi alkawarin daukar mataki.
"Dama ina da labarin Hasiya" ya ce yana kumfar baka "ance tafi kowa rashin kunya a cikinku. Wato zuwa tayi ta kitsa miki gaibu tace kiyi min rashin kunya ko? Tunda baki da hankali har ki ka karbi shawararta za ki ga abin da zai biyo baya. Wallahi Salima daga yau ko daga ido ki kalleni kin daina.."
"Idan ka isa ka kasheni kawai ka huta." Ta bashi amsa da kuka.
"Mama kiyi shiru don Allah" cewar autarta.
Ita da yaran babu wanda ya kula da lokacin da ya hanyo igiyar gugar rijiya. Murdeta kawai ya yi ya kama daidai inda zai masa dadin riko ya shiga lafta mata.
Salima taki yin ihu kamar yadda ta saba. Tsayuwa tayi kyam dukan yana sauka a jikinta amma zuciyarta ke karbar zafinsa.
Shi kuma gogan rashin jin magiyarta ya sake tunzura shi. Hannu ya daga ya kai mata dukan da yafi kama da naushi a gefen fuska. A lokaci ne kuma ta aiwatar da shawarar Ayaah. Tafiya tayi luuu ta zube a kasa. Yaran suka yo kanta suna kuka. Ale Gambo ya soma masifa yana jiran ta tashi yaji shiru.
"Ke Salima. Salima? Tashi mana" ya ce jikinsa na yin sanyi. Igiyar ya saki ya dan ja baya.
Babbar 'yar tasu mai shekaru sha uku Ihsan tana ganin ta fadi ta ruga makota a guje tana kuka. Duk da haka Ayaah ta ce suyi amma a tsorace take ko suman gaske Ummanta tayi. Kuka take tana kururuwa kamar yadda Ayaah ta fada mata a dan tsukin lungunsu.
"Wayyo Allah. Baba ya kashe mana Umma"
Hankalin Ale Gambo ya tashi sosai da yaji me take cewa. Girgiza Salima ya shiga yi yana faman kiranta kamar mahaukaci. Durkushe a wurin makotan da suka fara shigowa suka same shi.
"Haka kawai naga ta fadi nima." Ya dubi yaransa a darare "ai ban mata komai ba ko?"
Basu amsa masa ba sai ihun da suka cigaba da yi.
"Baba ya kashe Ummanmu da duka."
Salati kawai ake ji sai matan da suke neman taimaka wa Salima.
Shi kuma Ale Gambo sai huci yake da surutai mara sa kan gado. Duk wanda ya gan shi a wannan lokacin ya san ya shiga rudani, amma yana kokarin boyewa don kada ya tonawa kansa asiri. Hannuwa yake ta dagawa kamar mai shirin tashi sama.
"Ni ban mata komai ba! Daga maganar fatar baki sai mutum ya suma? Salima ki ji tsoron Allah ki mike. Wai me nayi miki?"
Ba a dauki lokaci ba ta dan farfado musu amma taki ta sha ko da ruwa ne ga kuma baki duk sai fitar da jini yake. Gefen fuskar nan inda ya daka ya kumburo suntum kamar alkubus. Kan a ce me gida ya kacame da 'yan jaje cikin daren, daman makotan ta da dama suna da masaniyar ba yau ya fara bugun ta ba.
Wani dan tsoho da yake yawan zama nan gindin bishiyar kofar gidan nasu ne yace to ya zama tilas su nemo iyayenta a sanar dasu kafin ya kashe musu 'ya wataran sai dai a kai musu gawa.
Kowa ya yi na'am da zancen. Shi ya saka wasu magidanta biyu tare da Ihsan suka hau adaidata zasu je a fada wa iyayenta halin da ake ciki. Ale Gambo yana neman yi musu taurin kai domin ya gudu samarin layin suka kama shi. An tsayar da magana cewa da an dawo da iyayenta zasu wuce dashi ofishin 'yan sanda.
***
Idanu ta runtse tana mai jin haushin kanta. Shigowar Innayo ta bakwai kenan dakin amma ta kasa motsa baki tayi mata tambayar dake cin ranta. Dangin Babansu da makota da dama sun zo mata barka. Amma yadda babu kowa daga gidan mijinta haka nan babu daga dangin Innayo. Hatta na cikin Kanon babu wadda ta zo. Abin ya yi mata ciwo. Indai ba su ma din sun tsaneta ba me zai hanasu zuwa? Ga yaranta da take masifar kewa kamar tayi hauka.
Sallamar Uwani ta jiyo tayi saurin share kwallarta. Sai dai tuni Uwanin ta gani lokacin da ta bankado labulen dakin.
"Kuka Zara? Naga uban kayan abinci su akarambana (Hasiya) suna gyarawa wai na suna. Ba dai rigima ku ka yi da Alh. Unais ba?"
Bangare daya na fatan haka ne ko don tayi mata dariya. Ta jima tana fada mata kudin miji ba a tinkaho dashi. Burgewa shi ne ki tashi ki nemi na kanki. Daya bangaren kuma mai sauran imani yana fatan ba haka bane. Shi ma kuma domin kada 'yan bani-bani su kara yi mata yawa idan Zaran ta durkushe ita ma.
"Bama waya ma" ta amsa mata muryarta tana karyewa "sai dai matsalarsa bata gabana. Na san yadda zan yi na rama duk abubuwan da suka yi min shi da Haj. Fatakwal."
"To meye kike hawaye?"
*
A waje Maimuna, Hasiya, da Murja da Ummita wadanda daga gida suka wuto nan din kai tsaye ke ta aikin kayan miya da nama. Yaran Maimuna duka maza ne. Biyu cikinsu, manyan sune masu yayyanka nama. Hira suke yi cike da nishadi Ayaah sai ta dinga jin kanta kamar bare. Gefe ta koma tana daddanna waya amma ko kadan abin baya burgeta. So take ayi da ita amma bata san kan hirar ba. Zantuka ne da dukkansu suka san wani abu a kai.
Hasiya tana ta lura da ita. Yanzu kam tana sane ta ki sakota cikin hirar saboda ta kara gaskata maganar Salima. Ta kuma samu abin da take so. Ayaah ta bata rai sai wani karkada kafa take wanda ta san da wata cikin yayyenta za ta yi mata magana karshenta a kare da rigima.
"Ayaah."
Kamar jira take ta amsa kiran Antinsu Maimuna da sauri.
"Na'am"
"Jeki ki karbo jaririyar nan wurin Zara na goya miki ita. Kin dai iya goyo ko?"
Yanzu ma da saurinta ta gyada kai "na iya"
"Dan wa ki ka taba goyawa?"
"Aji tsoron Allah dai banda karya"
Cewar Ummita da Murja suna mamakin yadda ma ta amsa