Showing 237001 words to 240000 words out of 242549 words
an yi masa duka.
Tunda Baaba Mari take bata taba samun kwanciyar hankali dari bisa dari ba sai yanzu. Alkawarin Allah Ya cika. Bayan kowanne tsanani akwai sauki tafe. Damuwarta ta shekara da shekaru ta kau. Sauran 'ya'yanta dama basu da matsala irin wadda ta jima tana damunta akan Abbati. Yanzu da komai ya daidaita ta sami nutsuwa.
Mal. Sa'idu ya soke karatun Allah. Sauran 'ya'ya da jikoki duk yasa an dawo dasu gaban iyayensu. Ya kuma aurar da 'Yashshafa ga wani tsohon saurayinta. Deluwa kamar ta hadiyi zuciya. Tana ta mitar yaya zasu yi ida Sha'aib ya zo. Hanne ma ta gama idda har manema sun fara kawo caffa. Ta cigaba da rayuwarta sannan ta rike sirrin Abbati.
***
Wata biyu kenan Abbati da Munzali suna karbar treatment akan hanyoyin tsira daga komawa tsohuwar rayuwarsu. Kafin su taho duk wani abu da suka mallaka sun damka shi a hannun Dr. Abdallah Saraki. Zunzurutun kudi da kadarori. Sutura da takalma kadai ne basu bayar duka ba. Amma hatta zobe da agogo basu bari ba. Motocinsu sun sayar. Gidan ma a satin aka sami mai saya. Sauran abin da basu kammala ba suka bar masa amanar sayarwa. Cikin kankanin lokaci aka dinga gina rijiyoyin burtsatse a kauyukan da suke tsananin bukata. Aka biyawa marasa lafiya da yawa kudin asibiti. Kudi ya zaga inds ya kamata. Dr. Abdallah ya taimaka musu kwarai wurin sauke nauyin da yake wuyansu. Hankulansu kwance a inda suke. Wayoyin hannunsu ma shi ya saya musu kafin su tafi.
Bayan tafiyarsu Alh. Sadisu ya neme su a waya shiru. Sai ya tuntubi Alh. Tahir. Shi ma bai san inda suke ba. A wurin Mami Khadija ya sami numbar Baaba Mari. Takanas ya tafi Kano inda suka hadu shi da Alh. Sadisu suka kirata. Ta hadasu da Mal. Inuwa shi kuma ya faygace musu halin da ake ciki.
"Alhaji da zuciya daya nake kaunar yaran nan. Idan suka dawo kana ganin zasu yarda in saka su cikin siyasa? Ba wai 'yan banga ko makamancin haka ba. Ina so in daga su a idon duniya. Su fara da zama PA dina ko Secretary. Ta yadda duk inda nasa kafa muna tare. A hankali har a sansu wata rana idan muna raye in daga hannuwansu a zaben manyan mukamai" Alh. Sadisu ya ce da Alh. Tahir bayan sun koma gidan Alh. Sadisun.
"Nima nayi tunanin janyo su aikin kwangilata. Amma ina gudun kada su ki amincewa saboda yarana da suka nema a baya. Sannan bani da wani mutumci a tunani a idanunsu. Dama auren zai yiwu da naji dadi. Musamman na Farha." Shi ma Alh. Tahir ya fadi nasa kudirin. Jari zai basu mai tsoka da zai ishesu tsayuwa akan kafafunsu. Amma kuma Alh. Sadisu zai bawa "ina gudun kada su ki karba. Ko kuma su ga kamar nayi ne da wata manufa"
"Hakika haduwarka da yaran nan izina ce garemu baki daya Alh. Tahir. Duba ka gani yadda rayuwarka ta canja. Ina fada ba don izgilanci ba. Yadda ka rabu da harkar mata haka idanuna suka bude na rabu da duk wani abu na haramci a siyasata. Don gani nake kamar hakki ne ya kama Abdul. Kuma naga fa'ida domin na kara samun masoya. Kwarjinin da nake fata na kara yinsa ba tare da na bawa kowa tsoro saboda cin zali ba."
***
Garin Parioli wanda yake cikin babban birnin Italy wato Rome shi ne inda ake da babban masallacin kasar. Saboda girmansa zai iya daukar masallata dubu goma sha biyu a lokaci guda. A daya daga cikin wuraren alwalar maza Abbati da Munzali ne suke alwala. Sun cika burinsu na ziyartarsa kafin su bar kasar. Abbati sanye yake da shudin wando da shudiyar shet wadda ya dorawa jacket sea green. Munzali kuwa bakin wando ne da polo shet ruwan madara a jikinsa. Su biyun sun yi kumari sosai. Ashe duk yadda jikinsu yake wannan abu yana tsotsesu basu sani ba. Sai yanzu suka kara zama cikakkun maza masu cikar kamala. Kowanne ya ajiye gashi a fuska wanda ya kara musu haiba. Alwala suke Munzali yana ta rawar dari. Abbati da ya gama ya koma gefe yana yi masa dariya.
"Nace maka ka k'ara riga akan ta jikinka amma ka dage wai da alamun rana a waje. Yanzu kuma ka zo ka sani a gaba kana makyarkyata kamar wanda ya kulla abota da DJ"
Munzali ya ciko hannu da ruwa zai watsa masa ya kauce yana kara yi masa dariya. A hasale Munzali ya ce,
"Ka dai ji kunya. Wai a matsayin wa na kake amma ka kasa sadaukar min da rigar sanyi. Sai surutu kake min kamar ..."
Kunnensu Abbati ya kamo yana cewa "ban hanaka rashin kunya ba?"
Munzali ya karkace kai saboda zafi yana magiya "me yasa baka san wasa bane. Don Allah ka saki kada kayi min kunne daya"
Zungure masa kai Abbati ya yi sannan ya cire rigar ya mika masa.
"Minti talatin zata yi a jikinka ka bani"
Da farinciki Munzali ya karba ya saka suka shiga masallacin domin yin sallar azahar.
Da suka idar hotuna suka dinga dauka domin tarihi. Ba su suka tafi ba sai da suka yi sallar la'asar. Lokacin jacket din ta koma jikin Abbati. Kowa minti talatin din yake ya bawa dan uwansa. Suna ta atishawa. Abbati ya yi ta mita. Munzali yana tunzura shi da cewa don kada ya barshi da jinya ne ma fa yake karbar aron rigar sanyin. Da zasu tafi addu'a kowannensu ya yi. Kusan abu daya suke roko. Cigaba da samun rufin asiri akan abin da ya gabata na rayuwarsu. Samun sana'ar yi sai kuma kowa ya yiwa dan uwansa fatan samun abokiyar zama tagari ba tare da sanin dayan ba.
Ranar da zasu tafi a airport dukkaninsu dokin ganin Qibdiyya suke yi. Sabo da rigima kamar yara harda fadan waye zai fara daukarta.
"Bayan ma yau baka kira mana ita ba" Abbati ya harari Munzali.
Zama suka yi akan kujerunsu daga jikin juna a jirgi sannan Munzali ya ce "na fada maka kashe min murya Zakiyya take yi. Sai ta kusa cinye kudin da surutu. Kai kuma ka wani dage ba za ka dinga kiranta ba sai kace surukarka"
"Ka sani ko ayi kome?"
Seatbelt din da yake kokarin sakawa ya saki ba shiri ya kalli Abbati.
"Kome a ina? Ni nace maka ina son aure ne ko kuwa ina son Zakiyya?"
Abbati ya ce "ko daya. Aure dolenmu ne Munzali. Indai ba so kake iyaye su sake fara zargin ko mun koma ruwa ne. Ba don na san mun rabu kenan dasu Diamond girl dinka ba ai da ita zan ce ka aura. To amma kaga babu wadda ya dace ka zauna da ita kamar Zakiyya. Ita ce ta haifi Qibdiyya. Ita ta san me ya faru da ita. Ita ce kuma zata san hanyar hana maimaici."
"Shawara ce kake bani?"
"Eh"
"Kana ganin akwai alkhairi idan aka daina rabawa Qibdiyya hankali?"
"Tana bukatar tsayayyen gida da uwa da uba."
"To kai yaushe za ka yi auren?"
"Wa yake ta tawa? Da Hanne tana nan da yanzu bakina alaikum. Yanzu kuwa dole in nema can nesa da gida."
Zancen Farha ya so yi masa amma ya fasa saboda baya son yi masa fami.
"To Allah Ya kawo tagari. Amma ka daina zancen Hanne baiwar Allah. Ni na san ko kadan baka sonta. Shi yasa kana samun dama ka sallameta" cewar Munzali yana dariya.
Shi ma Abbatin dariya ya yi yace "Cutar juna muke kawai. Tana jin haushina ina jin nata."
Jirgin na shirin tashi suka kira Dr. Abdallah, Alh. Sadisu wanda yanzu yake yawan kiransu sannan kowa ya kira iyayensa. Munzali kadaran kadahan suka gaisa da babansa. A hakan ma sun sami cigaba ne a alakarsu saboda jajircewar Munzalin.
***
Tafiyar awa biyar da minti hudu ce ta kawosu Nnamdi Azikiwe International Airport Abuja. Suna fitowa daga ciki mota tazo ta daukesu kamar yadda Alh. Sadisu ya ce musu ya bada umarni da suka yi waya.
"Zai kai ku hotel. Gobe zan zo garin ganin party chairman. Sai mu juya jibi tare. Ina fatan hakan ba zai zama takura a gareku ba"
Wannan shi ne abin da ya fada musu a wayar. Cike da girmamawa suka yi masa godiya. Da zasu fita daga motar bayan sun isa hotel din kudi direban ya basu a envelop.
"Yallabai ya ce ku rike kafin ya iso"
Suka sake yin godiya sannan kamar lokacin tasowarsu duk da dare ya yi sai da suka kira iyayensu. Cikin daren suka tattauna yadda zasu yi idan Alhaji Sadisu ya zo musu da wani abu da zai iya bata musu rayuwa. A yanzu sun hankalta suna matukar tsoron shigewa masu kudi. Babu dangin Iya babu na Baba. Watakila wani abin ake nema a garesu.
Washegari sai bayan isha Alh. Sadisu ya iso. Tare suka je suka ci abinci. Dakinsa a hotel din yace su biyo shi. Gabansu ya fadi amma suka daure.
Yana zaune a kan kujera suna kasa a gefensa ya yi musu magana.
"Na san cewa zukatanku suna cike da tambayoyi da fargabar manufar janyoku da nayi a jiki. Dom Allah ku kwantar da hankalinku. Ko babu komai ceton rayuwar Abdul da ku ka yi ya isheni dalilin son saka musu da abin alkhairi. A dalilinku ya sami sauki har ina shirye shiryen tura shi kasa mai tsarki da biyu cikin iyayensa mata. Sai ya yi a kalla shekara guda yana karatun addini zai dawo gabana ya karasa sakandire. "
Murna suka taya shi yaji dadi kuwa
"Magana ta gaskiya labarinku ya tsaya min a zuciya. Ban taba ganin almara irin wannan ba. Giyar kudi bala'i ce. Musamman ga matasa irinku wadanda kuruciya take diba. Yaran yanzu zasu yi komai domin kudi. Sai gaku na hadu daku zahiri ba labari ba. Kun bude min ido da kusanto da tunanin lahira a dukkan lamurana. A takaice rayuwata duka na canjata kuma duka kune sila. Wannan yasa na daukarwa kaina alkawarin ba zan bari ku tagayyara ba. Rashin abin yi da rashin kudi a hannun wanda ya saba rikewa ba karamar jarabawa bace. Tsananin rabo da tsoron Allah ne kadai zai dakushe zukatanku daga tunanin hanyoyin samun kudi ko ta wace siga. Saboda haka idan kuna da ra'ayi ni Alh. Sadisu Nakano nayi muku alkawarin muddin ina raye da rai da lafiya, zan yi iya yina domin ganin kun zama wasu ababen misali da alkhairi a cikin al'ummarmu. Ina burin duniya ta amfana da alkhairin da nake da yakinin Allah Ya wanzar muku sakamakon mika wuya gareShi. Me ku ka ce?"
Basu ce komai ba sai kwalla. Ikon Allah akwai ban tsoro. Duka duka awanni nawa da suka wuce ne suka zauna suna tunanin yadda zasu yi da rayuwarsu yanzu? Sai gashi mafita tazo daga inda basu tsammani.
Alh. Sadisu ya yi murmushi "in dauki shirunku a matsayin amincewa?"
"Alhaji ko za ka bamu zuwa gobe domin mu shawarci iyayenmu"
"Ka cika babba Abbati. Dama gaggawa daga shaidan take. Ku yi shawara da duk wanda ya dace. Fatana Allah Yasa ku bani damar zame muku uwa da ubs a siyasance. Da yardar Allah ni daku babu mai yin nadama."
Dr. Abdallah suka fara kira. Ya ce idan sun shigo Kano gobe su zo su same shi a gida. Da makomar tattaunawarsu da shi zasu yiwa iyayensu bayani. Daga nan su nemi amincewarsu.
Direban da ya daukosu daga airport shi ne ya kuma zuwa daukarsu. Alh. Sadisu ya sanar dasu cewa zasu tsaya a Kaduna zai ga abokinsa kafin su wuce. Haka suka jera suna biye dashi a baya.
***
Suhaib, Farha, Lilu, Sauda da Mardiyya ne suka fito daga wani babban shopping mall wanda yake makwabtaka da ofishin Alh. Tahir. Mami Khadija ya kuma roka akan burinsa na daidaitawa da yaran. Tayi musu magana harma da fada akan lallai su cire abin da yake ransu su kyautatawa mahaifinsu.
"Shi kadai gareku. Ba zai yiwu don ya auri Yumna kowa ya dauki gaba dashi ba. Duk alkhairinsa gareku bai kyautu ku manta ba saboda wani abu guda daya da bai sabawa shari'a ba"
Fadan a gaban kannensu ne. Su manyan sun san me take nufi. Hakuri suka bata tace to tana so bishi office su nuna masa komai ya wuce. Da yake kullum cikin kokarin janyosu jiki yake suna yakicewa sai kowa yaji babu dadi. Shi ne Suhaib ya ce su fara zuwa kowa ya sayi gift guda daya su bashi.
Sauda da Mardiyya sai tsalle da murna. Ji suke kamar sun dade basu ga Abbansu ba. Kowa ya yi kewarsa. Harda Suhaib kuwa.
Abbati da Munzali a hadadden reception din office din suka zauna suna hira. Alh. Sadisu ya shiga wurin Alh. Tahir ba tare da sun san wurinwa ya zo ba. Yana ciki suna tattauna makomar rayuwar yaran. Niyarsu sai sun gama magana sannan Alh. Sadisu zai kirasu ciki domin su sami fahimta da Alh. Tahir. Yana so su dauke shi a matsayin makusancinsu.
Waya suke yi da Qibdiyya ta cikasu da surutu mai bude kofar ya hangameta. Basu dago sun kalli su waye suka shigo ba koda suka ji ma'aikatan dake wucewa suna ta yi musu maraba.
"Oga yana tare da bako." Wani masinja ya fada musu.
"Bari mu jira shi a nan" Suhaib ya nuna kujerun reception din.
Kafin su karasa duka su biyar din sun ga su waye a zaune. Farha ji tayi kamar zazzabi zai kama ta. Kujerar farko ta gabanta ta dafa yayinda Suhaib da Lilu suka karasa gabansu.
Earpiece ne a kunnen Abbati yana kallon video din Qibdiyya na zuwa sabuwar makaranta wanda tasa mamanta tura musu a lokacin. Munzali ne ya daga kai da yaji alamun ana tahowa gabansu. Mamakin dake fuskarsu Suhaib shi ne a tasa. Da hannu ya zunguri gefen hannun Abbati. Yana daga kai idanunsa a bangaren hagu suka sauka. Duniyar sai ta tsaya cak. Numfashinsa ya dinga fita da sauri da sauri da yayi tozali da Farha.
Jikinsa nauyi ya yi masa saboda bai san me zai ce mata ba. Akwai tarin tambayoyi da ma bayani da zata bukata wanda bashi dasu. Kwanciyar hankalinsa daya shi ne sanin cewa Alh. Tahir ya rufa musu asiri.
Yana can duniyar tunani da kallonta har Munzali suka gama gaisawa dasu Suhaib. Ya rike hannun Lilu yana cewa "ka gafarceni. Kunya ta hanani nemanka."
"Komai ya wuce. Naga message dinka tun lokacin" Lilu ya bashi amsa da fara'a.
Sauda ta turo Mardiyya gaba don su gaisa tana ta nokewa.
"Diamond girl da Hasanarta kuna lafiya? Ya kwana biyu?"
Sama sama suka amsa, hankulansu sun karkata ga Abbati da ya yi mutuwar zaune ga Farha tana takowa wurinsu a hankali. Har ta iso Abbati bai dauke idonsa daga gareta ba. Tana zuwa gefen Munzali taje ta tsaya tayi masa sallama.
"Don Allah ko za ka iya bani wuri in zauna kusa da dan uwanka?" Ta nuna inda yake zaune kusa da Abbati.
Idanu ya dan ware ya ce "na'am?"
Idanun Abbati basu bar kanta ba duk da taki juyowa.
"Hoto nake so a daukemu" ta furta a dake. Hannunta ne ma ya soma rawa wurin kokarin bude jaka domin ta dauko wayarta. Idan ta kama dan karfen budewar sai ta kasa juya shi yadda ya dace. Saboda dauriyarta ta kusa karewa.
"Bashi wannan" Abbati ya mika mata wayarsa ko earpiece din jiki bai cire ba.
Ta mika hannu ta karba kanta a kasa bata yarda sun sake hada ido ba. Lilu ta mikawa don hannunsa tuni ya yo gaba. Ta koma ta zauna a inda Munzali ya tashi.
"Ya Farha"
Ko da wasa bata yi yunkurin amsa kiran da ya yi mata iya jin kunnuwanta ba don ta san muryar ta bace. Daga kai tayi kawai aka yi dace shi ma ita din yake kallo. A haka Lilu ya daukesu hoton suna yiwa juna kallo mai cike da sakonni kala kala.
Ana dauka ta mika hannu ta karbo masa wayarsa. 'Yan uwanta da Munzali suna ta kallon ikon Allah. Numbarta ta soma sakawa sai gani tayi sunanta ya fito baro-baro a jikin screen din.
(Ya Farhata)
Kwalla mai zafi ya sauko mata kowa yana gani tasa hannu ta dauketa. Cikin whtsapp dinsa ta shiga ta bude sunanta ta tura hoton da suka dauka sannan ta mika masa. Yana karba ta haye sama.
Su Mardiyya suka bi bayanta da sauri. Office din Alh. Tahir taje. Ta bude da sallama ta fada kai tsaye. Yana ganinta ya tashi ta iso ta rungume shi sai kuka. Lilu ya rike baki a hankali ya ce "see love"
"Me ya sameta?" Alh Tahir ya tambayi su Suhaib hankalinsa a tashe.
Amsar ya gani da idonsa da isowar su Abbati kofar office din.
Alh. Sadisu ya saki murmushi "Munzali me ku ka yi mata?"
"Babu ruwana fa. Aikin Abbati ne."
Abbati yaji kamar yana kan k'aya a inda yake. Ta daina kukan amma ko fuskarta baya hangowa.
Alh. Tahir dadi kamar ya yi yaya. Farincikin da ya rasa na watanni ya samu da ganin yaransa. Gashi alamu sun nuna Farha da Abbati suna son juna har lokacin. Alfarma ya roki Alh. Sadisu akan su je gidansa kafin su wuce.
"Abba da alama mun kusa shan biki a gida" Sauda ta ce tana tafa hannuwa.
Aka yi dariya sannan kowa cikinsu ya mikawa Alh. Tahir kyautar da ya kawo masa. Bawan Allah sai yaji yana neman yin kuka. Sauda da Mardiyya ya rungume don kada a gane suka fita tare.
Idan Abbati da Munzali sun yi mamakin sabon gidan da suka gani na Alh. Tahir sam basu nuna ba. Mami Khadija tasa mai aikinta ta kawo musu lemo da ruwa sannan ta fito. Ita kanta taji dadin sake ganinsu Abbati.
"Shikenan sai kuka bace Munzali?"
"Dawowarsu kenan kasar tun bayan faruwar wannan abin" Alh. Tahir ya bata amsa.
Bayan tambayoyin yaushe gamo, Sauda da Mardiyya kadai aka sallama daga falon sannan Alh. Tahir ya sake nanata abin da ya fada a gabansu.
"Alh. Sadisu ne ya basu shawarar barin kasar har kura ta lafa. Dukiyar da aka basu kuma sun tattara komai sun mayar ga masu ita. Shi ne suka gujemu a tunaninsu zumunci zai kare tunda yanzu basu da komai."
Wannan abu ya kara tausayinsu ga su Mami Khadija.
"Bawa bai taba yi domin Allah Ya tabe ba. Ba kowa zai iya abin da kuka yi ba Abbati. Mara tsoron Allah ne kadai zai gujeku"
Dama tunda Alh. Tahir ya kirata a waya ya fada mata zai kawo nan shi ne tasa aka kara abinci.
Falon cikin gidan tasa Lilu ya shigo dasu Munzali domin su ci abinci. Alh.