Showing 123001 words to 126000 words out of 242549 words
sai ya mike ya dorata akan cinyar Farha.
"Zan bika" ta ce da sauri tana daga hannuwa.
(ABIN LURA: Yaran da kan gamu da sharrin makusanta ta fannin fyade ko koya musu munanan dabi'u sukan saba da abin fiye da tunanin iyaye. Ba ranar Daddy ya fara taba Qibdiyya ba sai dai ranar ne ya fara nufin zarcewa. Wannan ne ya haddasa masa tsoronsa har ta kaishi ga yi mata barazana. Idan uwa bata kula da 'yar alawa da biskit kadai ake toshe bakunan yara musamman masu wayo ace kada su fadawa kowa. Ba tare da sani ba kwakwalwar Qibdiyya ta saba da abin da Daddy yake yi mata. Lilu da yake kusan tsaransa kuma lokaci guda ya jata jiki sai wancan abu yake neman tasiri a kan karamar yarinya. Gani take abin da Daddy yake mata shi ma kila zai yi. Kuma tunda ya fara da kyautatawa me yiwuwa ba zai kaisu da zancen yanka iyayenta ko ya yi mata mai zafi ba.)
Girgiza kai Lilu ya yi ya bata hakuri cewa zai je ya dawo ne sai ga Sauda tazo ta dauketa.
Shiru kan Farha yana kasa haka kawai take jin kunyar Abbati fiye da ta kullum. Nasa shirun bashi da nasaba da kunya sai nazarin yanayinta. Zuciyarsa ce take kara nanata masa lallai yabi a hankali saboda ba lallai bayan anyi binciken asalinsa a mallaka masa ita ba.
"Ya Farha dago kanki muyi magana"
***
Kayan daki gabadaya Uwani tasa Mubasshir fitar mata wurin neman kudadenta. Ko digo bata zargin Salihi saboda haka bai taba faruwa ba. Mubasshir din kuma ta san da wuya yake shigar mata daki. Tafi yarda da cewa wuri ta canja musu amma har yanzu shiru. Ga dadin bakincikinta yadda Ummule take tararta gaba da gaba babu shakka ko tsoro. Da taga wankin hula yana neman kaita dare kawai sai ta nemi Habibu. Ta kikkira wayarsa a iya kwanakin da take neman kudin bata samu ba. Shi ne yau kawai ta same shi a office.
"Hajiya, Hajiya" ya dinga yi mata kirari tun kafin ta iso gabansa.
Murmushi tayi kanta na fashewa ta sami wuri ta zauna. Bayan sun gaisa ta bijiro masa da bukatarta. Kudinta take so na Hajji ta fasa zuwa. So take ya bata taje ta karasa gyaran gida ta tashi.
"Ikon Allah. Metiron lafiya kuwa? Wannan indai ba fitar rabo ba waye ya taba fasa Hajji saboda gyaran gida?"
Cike da bacin rai ta ce "ba za ka gane bane Habibu. Wai ni Salihi ya yiwa kishiya? Kishiyar ma kuma wai gida daya zamu zauna. Bana son yin wani tashin tashina dasu domin nafi karfin haka. So nake ya gani a aikace cewa na haifu cikin uwa da uba. Sannan wannan aikin ba gumin banza nake fitowa nayi ba."
Yawu ya hadiya. Ta ina zai fara nemo wadannan makudan kudade yanzu? Dama jira yake a fara kiran maniyata ya samfe ba za ta kara jin duriyarsa ba sai an gama dawowa. Wannan ba za ta har ina?
"Gaskiya Metiron akwai matsala. Kudi ba zai dawo ba. Na fada miki cewa na riga na biya har Agents sun gama komai. Lokaci ake jira a baku passport dinku."
Huci ta kama sai ta ya tsorata. Ta buga ta raya ya daure ya cigaba da cewa sai dai tayi hakuri. Haka ta hakura ta koma wurin aikinta tana ta tufka da warwara. Da shigarta ba dadewa aka kawo mai haihuwa. Matan manyan mutane sun fi ganewa asibitin kudi akan na gwamnati. Yau sai ga tsuntsuwa daga sama gasashshiya. Matar kwamishinan raya karkara ce da kanta ta kawo surukarta. Nakuda ta kamata kuma suna ganin kafin su isa asibitin da take awo za a iya samun matsala saboda ta soma zubar da jini. Shi yasa suka kawota nan saboda yafi kusa. Uwani kuwa sai tayi uwa tayi makarbiya ta hana kowa tsayuwa kan mai nakudar.
Kafin likitoci biyun da aka sanar su shigo har ta gama shirinta. Kudi kawai take gani har ta samu indai tayi aikinta yadda ya kamata.
"Haihuwa ta nawa ce?"
Da kyar yarinyar ta amsa mata "ta biyu."
Rage murya tayi ta matsa kusa da ita kamar cikin za ta taba sai ta duka yadda za ta ji ta sosai.
"Naga babu dinki a haihuwarki ta farko kuma da alama da kanki ki ka karu."
"Washhh Allah..."
"Ko"
"Likitan ta ce ban karu shi yasa ba ayi ba."
Uwani ta dago kai kamar gaske "wace irin likita ce wannan mai neman kashe miki aure? Ke baki dinga jin jikinki a sake ba?"
"Innalillahi...wayyo Mamaaa"
Jira tayi ciwon ya dan kara sauki ta kuma ingizota.
"Zan taimaka miki. Idan kin haihu yanzu da kari kada ki yarda ko kadan ayi miki dinki. Zan jira ki haihu na baki nambata. Wallahi gyara zan miki giredi amma a gida. sai kinfi budurwa a wurin mijinki."
"Lahaula wala quwwata illa billah....ki rabu dani don Allah" yarinyar ta furta cikin tsananin azabar ciwo.
Ana haka likitocin suka iso. Kafin ma su fara dubata kan d'a ya danno. Ba haka Uwani taso ba haka tana ji tana gani likitocin suka karbi haihuwa. Abin dadi ga maijego wannan ma bata karu ba ko kadan. Uwani sai ta makale a dakin da sunan taimaka mata ta gyara jikinta kafin a fito da ita.
"Kar ki cuci kanki na san zafi ne babban abin da yake saka ku gudun dinki. Allura zan miki wadda zata kashe duk wani ciwo. Mazan yanzu masu dan banzan yawo sai da gyara ake samun kansu."
Bacin rai muraran ta gani a fuskar yarinyar a lokacin da ta tashi za ta fita daga dakin haihuwar tana cewa
"Baiwar Allah ki kyaleni don girman Allah"
Tana fita Uwani ta ciji lebe za ta fara zaginta sai ji tayi ance "ni ina so. A nawa za ki min na dawo kamar budurwa?"
"Dubu ...." ta soma cewa bayan ta bude labulen da ya raba gadon wadda ta haihu da na mai maganar. Ita ma tsohon ciki ne da ita. Ta sanar da ira cewa an kawota tun dazu anyi inducing amma har lokacin bata fara jin ciwo ba.
"Barshi ma. Zan baki dubu hamsin kiyi min aiki mai kyau." Sama ta kalla tayi kwafa "sai na shayar da kai mamaki. Wallahi nafi karfin zama da kishiya."
An tabo inda yake yiwa Uwani masifar kaikayi. Nan ta zauna tana yiwa matar da bata sani ba famfo da nuna mata illar rashin gyara irin wannan ga matan aure.
Ranar fafur taki tafiya gida sai wuraren uku na dare matar ta haihu. Ta so suyi magana tun lokacin amma ganin manyan likitoci suna ta kai kawo sai ta hakura. Ranta fari kal domin ta tabbata dai matar wani ce.
Bayan ta kimtsa an kaita dakin hutu da kanta ta ce a kira mata Metiron Uwani. Da zumudinta kuwa ta shiga ta kara yi mata barka. Matar ta karbi nambar wayarta.
"An riga anyi min dinki amma."
"Karki damu. Kwancewa zanyi nayi miki nawa. Wallahi na yiwa mata sun fi a kirga masu haihuwa a nan da haihuwar gida ko wasu asibitocin."
Ajiyar zuciya ta samun nutsuwa matar tayi sannan suka yi alkawarin ana sallamarta washegari za ta kirata ta bata kwatancen gidanta. Jikin Uwani har rawa ya dinga yi saboda taji kudi. Tana fita matar nan ta dauki waya ta kira maigidanta. Hakuri ta bashi saboda yana ta kiranta lokacin da suke maganar da Uwani bata dauka ba. Farincikinsa na sake samun karuwar zuri'arsu ya nuna mata da tambayar bukatunta idan akwai a lokacin.
Murmushi tayi ta gyarawa jaririnta kwanciya sannan ta ce "Akwai mai girma CMD (Chief Medical Director). Ana badakala a asibitin nan karkashin shugabancinka baka sani ba. Nayi karambani na kama maka daya. Za dai muyi maganar a gida. Amma please my dear ya kamata kasa ido sosai."
Dariya ya kwashe da ita ta tausayin mai tsautsayin da tayi shuka a idon makwarwa. Matarsa lauya ce mai zaman kanta wadda take hadawa da aikin sa kai na kare hakkin bil adama.
I just published "26" of my story "UWA UWACE...". https://www.wattpad.com/1025814941?utm_source=android&utm_medium=com.whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=BatulMamman17&wp_originator=f3dsiNVHQhnPpmsrf6Za7OnPVDBoe2EVQfBDpc9b5%2BNiVBLLjSXjNFjYmWPLib9NKigpf3Pq5gfayzx%2BVgnUFyXLVDLaYKjwlmS6DyEDcbfmbovhnzp33%2FJT2vhpPR%2BV
UWA UWACE...26
Batul Mamman💖
***
Karfe shida da kwata a kofar gidan Alh. Rabi'u ta yiwa Salihi. Garin da sauran duhu hasken rana bai fara fitowa ba. Wasu magidantan ma basu riga sun koma muhallansu daga masallaci ba. Daga ganin yadda ya ajiye mota zaka san baya tare da nutsuwa. Kasheta kawai ya yi ba tare da ya rufe ba ya fita ya soma doka sallama a kofar gidan.
Sallamar tasa ba karamin tsinka zuciyar Salima wadda ko tashi daga kan abin sallah bata yi ba tayi. A hanzarce ta mike suka kusa yin karo da Zara don ita ma ta gane muryar waye. Innayo kuwa iccen da take kokarin turawa a murhu tayi jifa dashi su ukun suka hado a kofar gidan da ko budeta ba ayi ba.
"Karbo min mukulli a wurin Alhaji"
Innayo ta furta muryarta tana fallasa fargabarta. Babu wani abu ko daya da zai kawo Salihi gidan nan da duku dukun asuba mai dadi.
Tare da Alh. Rabi'u Salima ta dawo ya sako babbar riga yana murza idanu don ko sallah bai yi ba. Innayo ya kalla ta jingina da bango zuciyarta tana ta dukan kirjinta.
"Aka ce Salihi ne yake sallama."
"Ni ne Alhaji" ya amsa daga waje.
Nasa hannun ma rawa ya kama yi sai Zara ce ta iya budewa Salihi ya shigo. Daga soron ya durkusa ya gaishesu sannan ya dan sosa keya.
Salima da Zara sai suka bar wurin tunda kowa ya fahimci ba tashin hankalin da suke taraddadi bane.
"Innayo ki bata hakuri tazo mu koma. Indai akan Ummule ne zan raba musu gida."
Alh. Rabi'u ya kalli Innayo kallo na wulakanci sannan ya yi wata irin banzar dariya.
"Hajiya Hauwa kenan. Kin nunawa kowa a gidan nan cewa kin fi kowa iya tarbiya da kyawun hali. Rannan har magana ki ka fada mana ni da Asabe akan 'ya'yanki. Sai gashi a tsukin abin da bai kai wata guda ba uku sun dawo gida. Allah Ya kyauta."
Wucewarsa ya yi ko waige babu. Salihi kunya ta lullube shi yaji kamar ya nutse a wajen.
Numfasawa Innayo tayi ta dube shi da murmushin da ya tsaya a fatar bakinta saboda bacin ran Uwani.
"Salihi aure kayi?"
Da sauri ya kalleta ba tare da ya iya boye mamakinsa ba.
"Uwanin bata fada miki ba?"
"Bata fada ba. Allah Ya sanya alkhairi. Sai dai kuma bata zo gidan nan ba."
Kansa da ya yi niyar yin kasa dashi ya sake dagowa da sauri hankalinsa a mugun tashe. Jiya bata da aikin kwana. A ka'ida ma kafin la'asar take dawowa a ranaku irin wannan. Sai gashi har bayan isha babu duriyarta. Ya dinga kiran wayarta babu amsa, wanda kuma tana sane don kada ya katse mata jiran mai haihuwar da zata zame mata alkhairi. Abu kamar wasa har goman dare. Nan fa yaji ba zai iya bacci ba dole ya tafi asibitin nemanta. Nos din da suke da aikin kwana ranar suka ce masa ta tafi. Basu san tana nan ba tunda kafin zuwansu ma 'yan yamma sunyi nasu sun tashi. Sai da ya tafi ne daya daga cikinsu ta ganta take fada mata wani yazo nemanta. Haka nan taji a ranta maigidanta ne amma sai taki kiransa. Dole zai yi mata ta dawo gida ita kuwa bata cikin masu wasa da neman kudi. Haka ya koma gida ko runtsawa bai yi ba. Tunaninsa ya tafi akan ko tayi yaji ne saboda zuwan Ummule. Shi ne ya taho gidan da sassafe saboda baya son kowa ma hatta Ummule ta fuskanci da b'araka irin wannan tsakaninsu.
"Ikon Allah" ya ce lokacin da yake jin wani irin tsoro a ransa "nima nayi jinkirin zuwan ne saboda tunanin ko ta karbarwa wata aikin kwana ne..."
Innayo ba shiri tayi 'yar dariya tana cewa "banda abinka Salihi yaushe zaka dinga magana kamar yau ka san Uwani? Ita da ba wasu kawayen kirki ba ai da wuya ne ta karbarwa kowa aiki."
Murmusawa ya yi shi ma. Wayar suka sake kira shiru dai ta ma daina shiga. Innayo daurewa kawai take yi amma gabanta sai faduwa yake yi. Salihi yana tafiya taje ta ballo magungunan hawan jininta tasha. Sun yi dashi zai koma asibitin ya sake dubawa. Idan an tabbatar masa ba a nan ta kwana ba zai kirata ya sanar da ita su san matakin dauka na gaba. Jiri ne ma ya yi mata sallama dole ta nemi wuri ta kwanta.
*
Wuraren bakwai da rabi Metiron Uwani ta fito daga dakin Haj. Salma wato matar CMD. Bakinta kamar gonar auduga domin Hajiyar tayi mata alkawarin idan aiki ya yi kyau tana da mutane a kalla shida wadanda zata hadata dasu. Duka kawayenta ne a cewarta da suka hayayyafa ana neman tayar da komad'a. Kudin aikin kowacce sun tsayar a dubu talatin. Nuna mata tayi duka matan manya ne sannan ai suna sayen kayan gyara na sama da wannan kudin sosai. Kai tsaye dakin da suke kwanciya ko ajiye kayansu ta nufa ta dauko wayarta. Tabe baki tayi ganin yawan kiran da Salihi ya dinga yi mata. Da yana sonta ba zai munafunceta ya karo aure ba ta ayyana a zuci. Kiransa tayi yana bakin danja zai karaso asibitin.
"Naga missed calls ne" ta ce dashi da ya dauki wayar da yanayi na nuna kosawa da kiran nasa.
Haushi ya kama shi ya daure ya boye fushinsa.
"A ina kika kwana?"
"Wace irin tambaya ce wannan bayan ka san ina zuwa aiki? To ina asibiti yanzu zan taho gida."
"Sai kin dawo"
Yau kam ya yi niyar nuna mata idan ma da gangan take wannan rashin hankalin to bashi da juriyar cigaba da dauka. Ace ko kadan bata ma san tayi masa ba daidai ba? Ta kwana a waje ba waya ba text sai amsa waya da gadara. Wayar Innayo ya kira ya fada mata sun yi magana sai ta roke shi da ya kawo Uwanin gidanta idan ta koma.
Ita kuma Uwani wayar kafintanta ta kira cikin sa'a kuwa ya dauka. Kayan gado da kujerun da ta saya a wurinsa ta ce tana bukatar aje a kafa mata yau. Dama ta saya ne saboda tayi gyaran daki idan ta dawo daga Hajji.
"Idan kun kusa titin Kofar Famfo ga nambar dana ku kira zai kaiku gidan."
Bayan ta gama dashi ta kira mai labule shi ma ya dinka mata ne na iya falo da dakin baccinta. Karin yadi ta ce ya nema irin wadancan za ta zo bayan la'asar suje ya auna labulen sabon gidan a kara. Kafin nan ta san masu gado sun yi nisa a nasu aikin. A son ranta a gama komai cikin kwana biyu ta tare.
Ginin da kuma wadannan kayayyakin da ta saya su suka cinye mata kudade. Dalilin da yasa ta shiga rudani kenan akan bacewarsa sarka da kudadenta na daki. Shawarar da ta yanke tun kwana biyu da bacewar kudin ce ta sake fado mata taji kwarin gwiwa. A jikin Salihi za ta fanshi kudinta komai runtsi.
Da wadannan lissafe lissafen ta kama hanyar BUK oldsite inda Mubashir yake karatu. Da ta kira shi a waya tsorata ya yi da farko sai yaji ba zancen kudinta bane. Haduwa suka yi ta bashi mukullin gidan nata da bayanin abin da zai yi. Saboda halin rayuwa ta jima da nuna masa gidan tun yana fuloti. Daga nan gida ta nufa zuciyarta kamar an yayyafa ruwan sanyi. Tana tura gate din suka yi ido hudu da Salihi.
"Fita zaka yi ne?" Tayi masa tambayar rainin wayo a zuwan ita har lokacin bata san tayi masa laifi ba.
"Ke nake jira"
Kallonsa tayi shekeke ta wuce ciki tana cewa "wai meye ne kake ta wani bata rai don na kwana a asibiti kamar wani bakon abu?" Dan tunani tayi ta dawo da baya ta ce "Idan saboda ban kiraka bane aiki ne ya min yawa. "
Tsabar takaicinta bai bashi damar amsa mata ba. Daki ta wuce tayi wanka ta fito ta sha shayi a gurguje saboda kada Haj. Salma ta kirata bata gama ba. Tana tashi Salihi da Ummule suka fito daga dakinsa. Dakin nata ya bita shi kadai ya sameta tana sauko da akwatuna.
"Lafiya?"
"Lafiyar kenan" ta ce a yayinda ta dauko wata leda da 'yan mukullaye a ciki. Kwancewa tayi ta dauko wasu masu guda hurhudu ta cirar masa d'ai-d'ai ta damka masa.
"Gasu nan mukullin gate ne da na kofar gida. Idan kayi kwanakin cin amanarka a nan sai ka dinga biyoni nawa muhallin ranar girkina."
Mamakinta yana neman zarta bacin ransa. Sam ya kasa fahimtar inda ta dosa.
"Ban fahimceki ba."
Kugu ta rike da hannu daya bayan ta turo dauri gaban goshi.
"Na gama gini na ina shirin saka 'yan haya kazo min da waccan abar wai kishiyata kuma kana sa rai na karbeta mu zauna a nan. Sai dai ina so ka sani cewa nafi karfin wannan wulakancin. In Allah Yaso ba zan kara sati ba a gidan nan zan koma nawa. Ba kuma zan yafe maka hakkina ko daya dake kanka ba."
"Yanzu Uwani har gida ne dake ban sani ba?"
Kwaikwayonsa tayi tana dariya "yanzu Salihi har aure ne da kai amma sai da matar tayi ciki na sani?" Ganin ya kasa cewa komai ta dora da cewa "da ne maza suke taka mata su zauna lafiya amma yanzu kan mage ya waye. Ko an fada maka kudin da nake nema ina yi ne don na mutu ku ci gado kai da 'ya'yanka?"
"A tare lafiya Uwani"
Daga yanayin fitar muryarsa ma ta gane ba da niyya ya yi mata adduar ba. Shi yasa ita ma ta amsa masa yadda zai ji haushi.
"Amin dai. In ka sami sukuni sai ka kawo kudi ko ka sayo gadon da zaka sa a dakinka na can."
Ya daina mamaki kamar yadda ya daina jin bacin rai. Hukuncinta sai ya zauna ya yi shawara da kwakwalwarsa sosai. Tafiya ya soma yi ta biyo bayansa da sauri.
"Af...baka ji ba. Na ce akwai lissafin da zan maka na abubuwan da bakuwarka ta sace min." Dage gira taga ya yi sai ta hau bayanin cewa ranar da ya kawo Ummule gidan bata ga alamun bakunta a tare da ita ba. Shiyasa rake ganin ba ranar ya fara zuwa da ita ba. A takaice tana zargin ita tayi mata satar kudi da sarka.
Katse zantukan da yake ganin matsalar kwalwalwa ce ta kawo mata su ya yi
"Idan kin gama shiryawa ki zo muje Innayo tana nemanki."
"Ina da uzuri zan biya idan na gama. Maganar