Showing 150001 words to 153000 words out of 242549 words
idanuwansa da suka kara firgita ta.
"Get out of here (bar wurin nan)" ya umarceta da tsawa.
A guje tayi cikin gida tana haki. Murja har ta fitar da rai da ganinta suka yi karo. Bata kula da yanayinta ba ta fada mata sakon Innayo.
Bayan tafiyarta Suhaib ya kalli Danliti wanda yake ta kokawar kwace hannunsa ya kasa. Tuno inda ya san fuskarsa ya yi ba shiri ya saki hannun baki a bude.
"Kai? Ba kai bane makaniken...."
Bai iya karasa magana ba sakamakon ture shi da Danliti ya yi da karfi ya kwasa a guje ya fita daga soron. Tunda ya fita ba shi ya tsaya ba sai da yaje titi. Ya tsaya mayar da numfashi bai yi aune ba wani mai kurar ruwa ya kwashe shi ya watsar a gefe.
*
Innayo da iyalinta har bakin mota suka rako su Mami Khadija. Su suna godiyar ziyara ita tana ta kyautata musu da aka yi. Ita dai Mama Nasima mota ta shige kai tsaye ko waige babu. Tuni ta fara musu da zuciyarta akan amincewa alakar Munzali da Mardiyya. Ta raina gidan da ahalin gidan.
An rarrabu kowa ya shiga mota. Ayaah kamar wadda ta yiwa Sarki karya gabadaya ta kasa sakewa. Duk inda ta motsa sai taga kamar idanun mutumin da taji Kawunta ya kira Suhaib suna kanta. A gaban motar Munzali ta zauna ta hade hannuwanta a tsakiyar cinya. Murja tana baya suka bi bayan motar Suhaib din. Ita dai har suka isa gidan bata san inda tunaninta yake ba. Tsakin da taji lokacin da ta fito daga motar ne ma yasa ta karewa gidan da suka iso kallo. Ido suka kuma hadawa da Suhaib ya sake yin tsaki a karo na biyu sannan ya kawar da kai tamkar yana kyamar kallonta.
Hawaye taji yana neman sauko mata ta daure ta hadiye shi. Da tabi 'yan matan cikin gidan shi tsayuwa ya yi wurin Munzali suna magana. Hankalinta a tashe tana tsoron ko abin da ya gani yake fada masa. Ana ta janta da hira sai dai tayi yake. Cikin abin da bai kai minti talatin ba har an gama kitson. Mami Khadija ta basu kudi suka ki karba. Har ta nuna bacin rai amma suka ki. Sai suka sake burgeta. Dama da a gida suka hadu ba kudi zata bayar ba. Kyauta zata yi musu irin wadda ta dace da 'yan mata.
"Ku karbi nambar juna ku dinga gaisawa. A haka ake fara zumunci."
Abin da tace musu kenan sannan ta juya ta barsu dasu Sauda. Da yake 'ya'yan nata babu girman kai a take suka fara aiwatar da shawararta, aka yi musayar nambobi tsakaninsu. Ayaah jiki ya kasa daina rawa saboda ganin har lokacin Munzali da Suhaib suna magana. Da Munzali ya kallo inda take kuwa sai da taji kamar ta saki fitsari a wurin.
"Ku zo mu tafi"
Kasa daga kafa tayi sai da Murja ta ja hannunta. Da suka isa bakin motar Suhaib ya bata mamaki da ya bude mata gaban sannan ya hada da yi mata murmushi. Kura masa idanu tayi ba shiri domin tabbatar da abin da take gani. Ya kuwa sake yi mata murmushi a karo na biyu. Farha tana yi musu sallama shi ma ya yi harda cewa su gaida gida.
Murmushinsa bai hanata satar kallon Munzali ba a hanya tana jiran ya fara fada. Gani take kamar na mugunta yake mata bayan ya gama hada mata bomb.
Kallon hanya da zurfi cikin tunani da take ganin Munzali ya yi bashi da alaka da abin da take tunani. Suhaib ya yi masa magana ne akan baffaninsu maza da suka yaba dasu har suka bukaci a sanar dasu cewa su turo iyayensu indai da gaske suke. Ya kira Abbati yafi sau shurin masaki amma bai dauka ba tunda gari ya waye. Abin ya karu domin yanzu wayar ko shiga bata yi. Haka ya rufe ido ya kira layin Baaba Mari shi ma shiru. Kafin ya isa kofar gidan Hasiya ya kira mutum ya kai shida a gidansu Abbati. A kalla kowanne ya kira sau uku ko hudu. Hankalinsa ya tashi sosai har ta kai kwatancen gidansu da Murja take yi masa baya ganewa sosai. Sau biyu yana yin kwana sabanin wadda take fada masa.
Tsayuwarsa da mota ke da wuya Ummita ta fito rike da Hasiya a jikinta. Tangadi suke duk su biyun. Hasiya na ciwo, Ummita na firgicin irin aman da taga tana yi. Cikin kankanin lokaci ta fita daga hayyacinta. Ko kashe motar bai yi ba Ayaah da Murja suka fita da sauri.
"Me ya sameta?"
Ummita tana kuka ta fada masa yadda Hasiya ta dinga amai daga kwabin lalle. Babansu kuma tun safe Abdulkarim ya turo aka tafi dashi asibiti tare da Abbas. Duk wannan bayanin a hanya aka yi shi. Gudu irin na ganganci ya dinga yi saboda kakarin da Hasiya take yi a galabaice.
Kiran Abbatin da bai sake samun damar yi ba kenan a ranar domin suna zuwa asibitin emergency aka nufa da ita.
***
"Gabadaya na kasa fahimtar bayaninka Abbati. Haka kawai ta suma bayan bata kwana da ciwon komai ba?" Mal. Inuwa ya furta hankalinsa yana ga Baaba Mari dake kwance akan gadon asibiti rai kwakwai, mutu kwakwai.
Atine ce tayi karfin halin cewa "Ya ce magana suke fa yaji ta daina amsawa"
Duka 'ya'yan Baaba Mari suna dakin da aka kwantar da ita a babban asibitin garin Kirikasamma. Abbati ya rasa me yake masa dadi a duniya. Gefe guda ya samu ya zauna ya hada kai da gwiwa cikin tunani. Tare suke da mahaifinsu Mal. Inuwa da wasu cikin Gwoggoninsu matan 'yan uwansa. Shi Mal. Inuwa yafi kowa nuna gigita saboda yadda yaga Abbati ya fito da ita waje a hannu ko motsi bata yi. Daga shi har 'yan majalisarsa sun dauka bata da rai.
Kowa yana tofa albarkacin bakinsa game da ciwon da ba a san silarsa ba likita ya dawo. Wasu gwaje gwajen jini ya sake rubutawa ya bukaci Abbati ya biyo shi waje.
Da sauri Mal. Inuwa ya ce "Fadi ko ma mene ne Dafta. Nan wajen duka babu bare. Me ya sami Mari?"
Likitan ya dubi Abbati wanda ya gyada masa kai sannan ya fada musu abin da suka gano.
"A gaskiya jininta ya hau fiye da kima har yana barazanar taba mata zuciya. Idan ba a dauki matakin da ya dace ba zata iya samun stroke (mutuwar barin jiki) ko ...."
"Allah ma Ya kiyaye" cewar Mal. Inuwa da rawar murya "indai kudi ne sha Allahu ba zai gagara ba. Ayi mata duk abin da ya dace ga danta nan."
"Malam. Malam"
Ba Mal. Inuwa da ta kira ba, duka wanda yake dakin sai da ya juya da farincikin ganin Baaba Mari ta farfado.
Da hannu ta yafito shi ya matso kusa da gadon ya duka kansa ganin tana ta motsa baki.
"Ku mayar dani gida."
Wani irin kallo ya mata cikin tashin hankali ya daga kansa ya yiwa Abbati inkiya da ya matso. Su Habi duk sai suka fice.
"Kaji taurin kan mata ko? Wai a mayar da ita gida."
Murmushi tayi masa "Idan an kaini asibitin waye zai biya kudin?"
"Wace irin magana ce wannan? Ko kin sami makuwa ne saboda ciwo?"
Muryarta ta kara dusashewa ta ce "kana da sauran kadara ne Malam da zaka sayar ka nema min magani?"
Duk da ya soma harzuka haka ya daure saboda ba lafiya gareta ba ya ce
"Wai ba ga Abbati ba? Mari lafiyarki kuwa?"
Idanun Abbatin ta lalubo da nata. Ya zabge tamkar shi ne kwance a gadon asibitin. Kalamanta na gaba a gareshi ita kanta basu yi mata dadi ba sai dai babu gudu ba ja da baya.
"Ban yafe ba idan ya sake kashe min kwandalarsa. Ban yarda kaima ka kashe min daga kudin da ya baka ba. Sannan idan ban tashi ba ka isar da sakona ga dan uwanka Sa'idu. Ni MARIYA BA YAFE MASA BA!"
I just published "32" of my story "UWA UWACE...". https://www.wattpad.com/1075498851?utm_source=android&utm_medium=com.whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=BatulMamman17&wp_originator=ch%2BCj6HFMGZric%2F0AziznjzpnsGFTeE6FcqyK47HiPNU9s7kTIdx2UmGGuBfIR%2BD6eifgeyno%2B%2FW1iPy3eGVxAoWDWZFgyOGfdmHjoCLwlZRaoqPmxHi7hxgWfHl7GQb
QUWA UWACE...32
Batul Mamman💖
Akwai uwa kuma akwai uwa! Wadansu uwayen sun san cewa 'ya'ya amanar Allah ne kuma suna kokari wurin ganin sun sauke in nauyin. A cikinsu wasu suna yin nasara wurin aikata daidai a wannan tafiya mai dadi da wahala. Wasu kuwa kuskure suke aikatawa wanda soyayyar 'ya'yan ne yake zama sanadiyarsa. A shagwaba 'ya'ya fiye da kima. A kasa tsawatarwa kurakurensu, sannan a karshe a biyewa ra'ayoyinsu koda zuciya da kwakwalwa sun san hakan bai dace ba. Kaso na biyu cikin uwayen bayan wannan rabe raben na masu son sauke nauyi sune masu fifita kawunansu da bukatunsu akan na 'ya'yansu. Irinsu ake yiwa lakabi da ballagaza.
Kwakwalwarta kalau take balle ace lalura ke hanata bawa 'ya'yanta kulawa. Ita bata ma san cewa kuskure take aikatawa ba. A lissafinta kodayaushe ita ce farko kafin danta. Shi yasa take gabatar da farincikinta kafin na danta. Ita fa ko yunwa ke damunsu ita da 'ya'yanta sai ta fara koshi take tunawa dasu. Idan abincin babu yawa sai su kare da sudin hannu. Kulawa wadda ke karkata zukata ga nuna tausayi da damuwa ga mai bayar da ita bata fiya shiga tsakaninta da nata ba. Wannan sakacin nata zai iya zama kalubale kuma babbar jarabawa ga 'ya'yanta da duk wanda ya rab'e su. A karshe da za ta rigasu komawa ga Allah da wahala su ji kewa irin wadda 'ya'ya ke ji idan sun rasa uwa. Albarkacin wata tara, nakuda da shayarwa kadai za ta ci.
Ya ke Uwa!
Ki koyawa 'ya'yanki sonki ta hanyar kulawa, tausayi, jinkai, ladabtarwa da soyayya. Idan a gaba kin sami sabanin tarbiyar da kika yi musu ki sani cewa kowane bawa yana tafe da kaddararsa. Ke dai ki tabbatar cewa kin yi iya yinki har a gaban Allah ta yadda ba za ki zama wata Asaben ba. Kin bata naki ki bata na wasu da basu ji ba basu gani ba.
Kada ku manta laifin ba na Uwa bane ita kadai.
***
Ya dauki kimanin minti goma sha biyar a dakin bata ce komai ba. Hasali ma ko motsi daga inda take bata yi ba. Qibdiyya ce a gefenta idanunta a kumbure sun yi ja, da gani tasha kuka. Ya yi mata magana bata amsa masa ba. Tun shigowarsa da ta taso a guje Asabe tayi mata tsawa ta koma ta zauna.
Gajiya ya yi da shirun. Ya san halin mahaifiyarsa. Karshenta kudi take son karba a hannunsa take ta kirkiro wannan dabarar. Hannu ya zira a aljihu ya zaro dubu goman da ta rage a hannunsa ya dora mata a hannun kujera.
"Qibdiyya taso mu tafi" ya furta a yayinda ya mika mata hannunsa don ta kama.
Sannan Asabe ta tashi da fada bayan ta kwashe kudin "ince ka zo amma don raini baka tsaya kaji me ya faru ba za ka tafi."
Hannu yasa ya matse kansa da yake ciwo. Haka ya soma magana kamar zai yi kuka. Bai san wata damuwar da ta zarce rashin ji daga Abbati ba. Washegari yake son bin sa, ko ma me za ayi gara ayi musu tare. Ko kuma ya bishi a yau....tunaninsa ne ya katse lokacin da Asabe ta sakar masa harsashin da ya bula kwakwalwa da zuciyarsa.
"Ban san wane irin sakaci kake yi da 'yarka har wani tsinanne ya..ya" sai taji bakinta ya sarke sakamakon idanun da Munzali ya zuba mata.
"Me aka yi?" Ya furta da sautin da yafi kama da umarni. Bai ma san ya yi amfani dashi ba saboda yadda ya soma tsorata tun kafin yaji karshen zancen.
Asabe ta hadiyi yawu "ina jin fyade aka yi..."
"Qibdiyyan???" Ya tambaya a razane kafin ma ta kai karshe. 'Yarsa ya dauka da zafin nama yana neman dubata mata jiki.
Asabe tayi azamar karbeta "baka da hankali ne za ka bude mata jiki? Na riga na duba kuma wallahi namiji ya kusanci..."
Innalillahi wa inna ilaihi raji'un....hawaye ne suka ballewa Munzali. Zancen ya dinga bin sassan jikinsa tamkar ana huda shi da alluran da aka kona a wuta. A wurin ya durkushe yana kuka mai sauti. Kuka irin wanda bai taba yin kwatankwacinsa ba. Da zai ci karo da ko ma waye ya tabbata sai dai ayi masa takwara a dangi domin shi kam tasa ta kare. Kashe shi zai yi idan ya so shi ma a hukunta shi.
Asabe gani tayi ya dora hannu a kahon zuci yana bugun kirjinsa. Idanunsa basu bar fitar da hawaye ba.
"Kashe kanka zaka yi ko kuwa zaka tambayeta waye ya mata wannan aikin?" Sannan ta kara da cewa "kuma ina zargin ba abin kwana daya bane domin kuwa alamu sun nuna ta soma sabawa."
Runtse idanuwansa kawai ya yi. Yawancin maza idan 'ya'yansu mata suka isa aure sai kaga suna ja wa manemansu aji. Ba don komai ba kuwa illa tunanin cewa idan ka auri 'yata fa ga abin da zaka yi mata. Wannan kishin yadda uba yake yiwa 'yarsa haka 'ya'ya maza suke yiwa uwayensu idan kaddarar sake aure ta gifta musu. Munzali yaji zuciyarsa tana suya a kirjinsa. 'Yarsa mai shekaru biyar ake cewa ta saba...ta saba da namiji a kananun shekarunta. Shi da ransa, mahaifiyarta ma da ranta. Garin yaya???
(Zina bashi ce Munzali. Kaga Allah Ya bamu 'ya. Idan bamu tuba ba wata rana ita za ta girbe abin da muka shuka)
Kalaman Abbati a wani lokaci da yake yi masa maganar tuba daga wannan alfashar suka dawo masa. A hankali ya tashi yaje gaban Qibdiyya ya durkusa. Ya mika hannuwansa gareta duk ta firgice. Asabe tayi mata dukan da ba a taba yi mata ba a dalilin kin fadan wanda yake mata. Shi yasa ta tsorata ko shi ma dukanta zai yi. Ga mamakinta da Asaben sai ya rungume Qibdiyya. Riketa ya yi sosai a jikinsa yana jin kamar ranar suka fara haduwa bayan haihuwarta. She will always be his baby duk girmanta. Kasancewarta tsatsonsa bai kara mata komai ba sai masifa. Ya cuceta cuta ta har abada domin an bar mata tabo daga barnar da ya kasance yana aikatawa.
"Ki yafe min Mariya. Ki ce kin yafe min."
A razane Asabe ta taso har tana tuntube da kujera.
"Me kake cewa. Na shigesu. Munzali kai ne ka bata..."
Magana ya cigaba da yiwa Qibdiyya da taushin murya.
"Ki yafewa uban da bai bar alkhairin da zaki mora a rayuwarki ba sai sharri. Nayi miki alkawarin gyarawa. Zan yi ta tuba har karshen rayuwata. Ina fatan Allah Ya haskaka rayuwarki Ya wanke miki duhun da na janyo miki."
"Munzali kayi min gwari gwari don Allah. Shin kai ne ka bata 'yar nan?"
"Allah ba zai dora min wannan kaddarar ba in sha Allahu."
"Washhh har hankalina ya kwanta" tace tare da sauke ajiyar zuciya "yadda ka ke magana ne sai a zata kai ne."
Da Qibdiyya a hannunsa ya juyo ya fuskanceta
"Hankalinki kar ya kwanta Asabe. Ke ki ka assasa komai."
"Kar ka dora min laifin da ba nawa ba. Dubata fa kawai nayi na sanar da kai. Banda sakarci ita kadai kwal amma kun kasa kula da ita."
Murmushin bacin rai ya yi "kamar yadda ki ka kasa kula dani da 'yan uwana?"
Ba ta zaci wadannan kalaman daga bakinsa ba shi yasa ta dinga bude baki tana rufewa don mamaki. Da kyar ta iya yin magana muryarta tana fita kamar an shake mata wuya.
"Me kake nufi?"
"Bayan haihuwata da suna da ku ka saka min ke da Baba kuna da wani abin kare kai a wajen Allah game da tarbiyyata? Kin san sana'ata? Kin san silar arzikina?" A yanzu sababbin hawaye sun cika idanunsa har suna zuba amma dariya yake yi "ina dauke da zunubina ga na Abbati da nayi silar fadawarsa mummunar rayuwa. Ba mamaki shi yasa Allah Ya jarabceni akan Qibdiyya."
'Kada kayi sab'o' ya fadawa kansa da ya tuna da cewa da a gaban Abbati ya fadi wannan maganar haka zai ce masa.
Tunanin Asabe sai ya luluka da ita duniya daban da wadda Munzali yake son haska mata. Gani take kamar abin da ya sami Qibdiyya ne yake neman taba masa kai. Banda haka kaf zantukansa basu yi ma'ana ba a cewarta. Tana kallo ya murda kofar dakinta ya fita. Sai dai me?
Yana fita suka yi ido hudu da guda cikin 'yan uwansa mata. Idanunta kadai ya kalla ya san ta gama jin komai. Abin mamaki shi ne yadda zuciyarsa bata ji komai ba. To me zai ji bayan ciwon da yake ciki a yanzu? Matsalarsa bata wuce rashin sanin halin da Abbati yake ciki ba. Sai kuma tunanin irin hukuncin da zai yiwa wanda ya soma ketawa diyarsa haddi.
***
Zaune akan kujera Mal. Sa'idu ne yana karkada kafafunsa. Su hudu ne a falon Baba Mari. Daga ita sai Abbati, Mal. Inuwa da shi babban bako na musamman. Bacin ransa baya bukatar ya bude baki ya yi magana. Yanayinsa kadai ya isa tsorata jama'ar gidan.
Mal. Inuwa kansa a takure yake don idan fadan ya tashi babu mai tsira. Da ya dubi Baaba Mari sai ta bashi tausayi. Duk yadda aka yi zafin ciwo ne ya kaita ga yin wannan kasadar.
Gyaran murya Mal. Sa'idu ya yi gami da yin kwafa.
"Inuwa gani a gaban isasshiyar matarka. Ka umarceta da ta fadi abin da yasa ta aika NI SA'IDU in zo inda take."
"Mari..." Mal. Inuwa ya fada a hankali kamar yana rokonta da ta kawo karshen zaman nan.
Mal. Sa'idu ne ya katse shi
"Idan kuma takamarta haihuwar Abbati ne to ka tuna mata cewa ni da ake zagi, ni ne silar arzikinsa. Bayan duk tijarar da ta gama yi akan tura shi karatu gashi tafi kowa girbar samunsa" ya daga hannu yana kadawa domin kashedi "duk da haka babu wata mace da ta isa ta nuna min iko da danta domin iyayensu maza ma umarni na suke bi. Abbati da duk abin da ya samu nine sila..."
"To Alhamdulillahi..." Baaba Mari ta katse shi.
Kowa sai ya kalleta da tayi magana. Abbati kuwa ji yayi kamar kasa ta bude ya shige ciki kada a sake jin ko da sunansa balle labarinsa. Ya amince da ko ma me zata yi amma hakan ba zai hana shi jin tamkar tsirara yake a gabansu ba.
Kamar tana jin rurin da zuciyarsa take yi sai ta kira shi da hannu. Kafafunsa da yake ji kamar ba nasa ba haka suka kaishi gefenta ya sulale ya zauna. Dan murmushi tayi masa wanda ya sake nutsar da zuciyarsa sannan ta fuskanci Mal. Sa'idu.
"Fashin baki nake son yi muku akan wani abu da kuke yi mara tushe kafin na fadi