Showing 132001 words to 135000 words out of 242549 words

Chapter 45 - UWA UWACE COMPLETE BOOK by Fatty Noor.txt

09 Oct 2025

3363

filin nan da sa hannu wanda na saya a wurinsa. Kai hatta Mai unguwa sai da muka je yasa hannu a matsayin shaida."


Duk da yana cike da haushinta sai ta dan bashi tausayi a lokacin. Ba kuka take ba domin tana da bala'in dakakkiyar zuciya. Jikinta ne kawai ya saki sannan sautin muryarta ya fallasa tsoro da tashin hankalinta.


"Ki kwantar da hankalinki tunda akwai takardu za a warware cikin sauki in sha Allahu."


Sambatu ta dinga yi kamar ba da ita yake ba. Katangar gidan ta nuna masa inda tasa aka yi baya da ita kawai don tana son ayi mata rela samma tana tsoron kar ta shiga filin gwamnati. Shi dai hakuri ya bata har suka koma mota tare da Mubashir a baya. Niyarsa su je gida ta amsa kiran Innayo sai ta kafe akan lallai ofishinsu can Ministry of Health zata je ta sami Habibu.


"Shi ne ya jagoranci sayen filin da komai. Zuwa zai yi ayita ta kare don wallahi asara bata kamani ba."


"Waye kuma Habibu?" Salihi ya tambayeta. Bacin ransa na dawowa sabo fil.


"Abokin aikina ne. Shi ya tallata min filin ya kuma shige min gaba."


"Tunda kin auri lusari ai dole wani kato ya fini sanin halin da kike ciki Uwani."


A kausashe Salihi yayi maganar wanda yasa Uwani shan jinin jikinta. Borin kunya ta soma yi masa saboda ta san bata da gaskiya.


"Damuwa kayi dani da zaka san me nake ciki? Ko kai ba aure kayi ba tare da sanina ba? Habibu duk inda yaji harkar karuwa zai nemeni. Kafin ka ce ban fada maka ba ma shi na bawa ya biya min kudin Hajji. Bana damu za ayi 'yan bakinciki su daina hura mana hanci."


Da kannensa mata take ya sani. Shi yasa bai ce komai ba har suka isa gate din BUK ya sauke Mubashir. Kai tsaye ministry din ya nufa sai ga waya an kirata. Koda ta duba sunan (Costumer) ta gani ya bayyana. Murmushi a take ya maye gurbin bacin ranta. Amsa kiran tayi taji muryar Hajiyar nan da ta haihu tana yi mata magana cikin nutsuwa. Uwani ta ajiye komai a gefe ta saurari kwatancen gidan da matar tayi mata.


"Ka saukeni 'Yan Kaba zani" cewar Uwani ga Salihi.


"Ai ko direba nake ya kamata ki rissina lafazinki gareni."


Yatsina fuska tayi ta gyara lullubi sannan ta hayyako masa da fada tana jin kanta daidai da kowa tunda ta tabbatar zata sami kudi. Cikin kudin za ta bawa Habibu a kashe kurar dake neman tashi a gidanta su sallami KNUPDA.


"Sau nawa nake cin arzikin shiga motar taka da har zaka min gori? "


Girgiza kai kawai ya yi "wurin wa zaki a 'Yan kabar?"


"Stitches zan yiwa wata."


"Allah Ya kiyaye hanya."


Sauketa ya yi ta fita ta shiga adaidaita sahu. Yadda yake jin bacin rai ba zai juri ja in ja da ita ba. A yau kadai ya gane har yawon dinke mata take zuwa bai sani ba. Sai yake jin kamar ma bai san wace ce yake aure ba. Karya kwana ya yi ya nufi Ministry din yana son ganin wannan Habibun domin zuciyarsa taki nutsuwa. Ba wai zarginta yake ba domin ya yarda da ita dari bisa dari. Duk bakin halinta ya yarda za ta tsare mutumcinta duk inda take. Harka dai ta kudi ce bashi da tabbas. Idan yana son gyara lamuranta ya kamata ya fara da sanin abokan huldarta.


Da kwatance da kiran waya Uwani ta isa gidan CMD. Bata wani sha wahala ba saboda kwatancen dalla dalla ne duk da ba a fada mata sunan maigidan ba. Hankali kwance ta shiga wani makeken falo bayan anyi mata iso. Gida ne babba irin wanda take burin mallaka wataran. Nan da nan ta sake ganin kimar hajiyar tana tunanin yadda za ta tatsi naira jikinta da kawayenta matan masu kudi.


"Haj. Umma ta ce ki shigo ciki" 


Muryar mai aikin da ta shigo da ita ta katse tunaninta. Sai lokacin taji sunan matar. Wata kofa suka bi sai gasu a wani falon da ya shafe shafin inda ta baro. Sai da ta zauna akan wata luntsumemiyar kujera sannan matar ta tafi. Kimanin minti bakwai sai taji sallamar Hajiyar. Fuska ta saki tana mai kara raina kanta. Kama daga sutura zuwa su sarka babu ta inda Haj. Umma bata burgeta ba. Tashi tayi cikin girmamawa tana yi mata sannu.


"Ya karfin jiki da jaririnmu?"


"Alhamdulillah Matron Uwani. Ya gajiyarki?" ta amsa fuska a sake.


Zama suka yi Haj. Umma ta ce bari ta kira Maigidan su gaisa sai su shiga daki ayi. Uwani taji kamar kakarta ta yanke saka yau. Idan tayi sa'a mijin mai alheri ne ai kila shi ma ya bata wani abu. Irin wannan mutanen idan sun yi maka kyauta baka cewa a'a.


Kamshi ta fara ji kafin sallamar babban mutum cikin wani irin yanayi na seriousness. Kasa dagowa tayi har ya zauna ta gaishe shi.


Muryarsa babu alamun wasa ko digo taji ya kirata da cikakken sunanta. Wani abu da yasa hanjin cikinta kanannadewa da juna cikin azama.


"Matron Uwani Rabi'u!"


Haka ta daga kai jiki na tsuma. Fuskar da ta gani sai da ta kusa sakin zawo. Basu taba haduwa kurkusa ba amma karya take ta ce bata san kamannin CMD dinsu ba. 


"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" ta dinga maimaitawa ba ji ba gani da karfi ga gumi yana bin sassan jikinta.


Dakewa ya yi domin ba abu bane mai wuya ya tausaya mata ya fasa hukuncin da ya dauka. Bai manta da zantukansu da maidakin nasa ba. Inda take cewa yiwa Uwani sako sako tamkar an ce ita ko wasu su cigaba da haka ne. Dole ne ya tauna tsakuwa domin aya taji tsoro. Laifin Uwani mai girma ne. Gara ace matan ke nemanta da abin da take yi. Akalla idan su suka nemeta a waje babu ruwan asibiti. Yanzu kuwa ana samun tangarda basu da mai kwatarsu a hannun hukuma tunda ma'aikaciyarsu ce.


Envelop ya nuna mata akan karamin teburin gilas na gabanta.

"Dauki ki tafi."


"Ranka. Ranka. Ya dade. Ranka ya dade.." ta soma magana tana waigawa ko matar tasa zata fito.


Katseta ya yi ganin za ta bata masa lokaci. "Idan hukuncin da yake ciki bai yi miki ba kina iya kai batun Ministry."


Kafin ta samu bakin magana ya fice abinsa. Kasa bude takardar tayi saboda faduwar gaba. Kafafunta kamar an kwashe mata kasusuwa don kiris ya rahe ta zube a kasa. Kirjinta kawai ke dukawa tare da azababben ciwon kai. Ko a mafarki abubuwan da suka faru yau suke samunta ta san cewa sai ta tashi da hawan jini. Shigowar Haj. Umma wannan karon fuska a tamke ya kara tayar mata da hankali.


Ita mamakin kasadar Uwani ma take yi. 


"Allah Yaso ki duk wadanda kike yiwa aiki ta wannan sigar babu wadda nata ya baci ta shigar da kara kotu. Da license dinki ya dade da barin hannunki. Idan private practice kike son budewa kin san akwai hanyoyi da matakan da ya kamata ki bi domin samun sahalewar gwamnati. Amma son zuciya ya hana. Ace mace tana tsakar nakuda don tsabar rashin tausayi kina tallata mata muguwar sana'arki?"


Kalaman cin mutumci ne suka taba fita daga bakinta ga abokiyar aikinta lokacin da ta taba  yunkurin hanata wannan sana'a. Ashe kura ta san gidan mai babbar sanda. A gaban Haj. Umma ko tari bata iya yi ba har ta gama magana.


"Ki bashi hakuri Hajiya. Tunda ki ka ga ina wannan abu kin san cewa kudi nake nema."


"Kiyi me dashi? Yasa anyi bincike akanki Uwani don kar ya dauki hukunci bisa rashin uzuri. Kina da miji mai rufin asiri. Har mota gareki balle ace kuncin rayuwa ne ya tasoki a gaba. Neman kudi ba hauka bane so kar ma kiyi kokarin justifying laifinki. Ko kina da wata kebantacciyar bukata hanyar da kika biyo bata dace ba."


A shekaru wannan matar bata fi kanwarta ta uku ba Salima. Don tana auren maikudi shi ne za ta tasata a gaba da bakaken maganganu? Wannan abu ya tunzura zuciyarta taji ba za ta bar gidan bayan an koreta daga aiki ba tare da ta rama ba.


Yatsina fuska tayi tana hura hanci ita a dole girmanta bai zube ba.

"Don kin sa an koreni daga aiki kina tunanin zan daina walwala ne? Ana kiran ciwon 'ya mace na 'yar uwarta ne kamar ba a san mata sun fi kowa son ganin karshen junansu ba? Banda munafunci ai bake nake yiwa tallan ba jiya amma kika yi katsalandan kika ce kina so. Auren maikudi ba zai raba mace da talauci ba ehe. Idan kina son burgewa ki nemi na kanki ki wuce wulakancin namiji."


Tun farko Haj. Umma bata ga alamun mutumci a tare da Uwani ba. Sai dai ko kadan bata kawo a ranta abin ya kai haka ba. Ranta ya sosu matuka amma haka ta daure taki magana har Uwani ta dire tana yi mata kallon banza. Hannu ta kai ta dauki envelop din da Uwanin bata kai ga dauka ba ta yaga shi gida hudu ta watsar a kasa.


Uwani tabi takardun da kallo tana kissimawa a ranta rashin nuna tsoronta ya yi rana. Karshenta matar ta tsorata ne taga gara a bar mata aikinta. Murmushi ta soma yi sai dai bai kai ko ina ba idanunta suka soma cikowa da kwalla sa'ilin da Haj. Umma ta soma magana.


Tsaye take kyam kana ganinta ka san mace ce da ta san kanta. Sai tayi mata wani irin kwarjini.

"Suspension ne na wata hudu hukuncin da aka yi miki ba tare da kai zancenki ministry ba. Anyi miki haka ne domin kada mu rabaki da aikin da bamu san irin WAHALAR DA IYAYE suka yi wurin karatunki ba. To amma Uwani kin yi kuskuren fada min maganganu son ranki a cikin gidana. Ki koma bakin aikinki daga yanzu idan kin so. Sai dai ina so ki sani cewa in sha Allahu indai ni Barr. Umma Jibril ina numfashi sai kin rasa license dinki ba ma aiki ba."


Wuta ce dif ta dauke a kwanyar Uwani

'Barr. Umma Jibril din da kusan duk mai jin Rediyo Kano ya sani?' ta tambayi kanta a zuci. Amsa ta bawa kanta domin tana jin sunan ta alakanta muryar da wadda take ji a rediyon.


Da tangadi ta bar gidan don ji take kamar duniyar da ta sani aka kifar. 'Yan uwa da iyaye da mijinta bata ga wanda ba zai yiwa halin da take ciki dariya ba. Zasu samo mafita ko ta wane hali ita da Habibu. Ya san manya a matakai daban daban na gwanati. Idan ta rasa aikinta ta rasa matattakalar rayuwarta ne. Shi ne abin da ta dogara dashi wanda zai kangeta daga talauci.


Habibu ta kira. A lokacin yana tsaye a gaban Salihi yayi tsilli tsilli da idanu. Tambayarsa ya yi akan ya hada shi da ainihin dillalan filin da tayi gini sannan ya bashi shaidar biya mata kudin kujera. 


Mintuna arba'in da suka wuce Salihi ya tambayi masu gadi ko akwai Habibu a wurin. Tashi daya suka amsa da cewa akwaisu har uku. Biyu manyan ma'aikatane. Daya kuwa sub-staff ne mai shigewa manyan. Yana jin haka ya ce a nuna masa shi. Da ya sanar dashi cewa shi ne mijin Uwani ba karamin mamaki da tsoro ya gani a tare dashi ba. Tambayoyin da ya yi masa suka sashi daburcewa ya kasa bada kwakkwarar amsa. Sai gashi ta kira a wannan lokacin. Gefe ya dan matsa da niyar bude mata wuta da borin kunya.


"Habibu akwai matsala. Zan shigo ministry yanzu."


Tana cikin tashin hankali a yadda yaji muryarta. Sai ya fasa fadan ya ce 


"Don akwai matsala sai ki turo min mijinki ya titsiyeni a cikin mutane?"


Adaidaita sahun da ta tare ta hau. Abin da ya dameta daban da zancen da yake yi shi yasa ta amsa shi ba tare da nuna damuwa ba

 "Zuwa ya yi? Yace maka me?"


Habibu sai ya murmusa ya zabi amfani da amsarta ya tada tarnaki tsakaninsu. In ba hakan ya yi ba yau shi za ta karewa.


"Takardun filinki ya ce na bashi da kuma kudin kujerarki. Har yana ikirarin ban isa na fishi sanin matarsa ba. A matsayinsa na mijinki yaba da hakki akan dukiyarki amma ke ce harda yin gini bai sani ba."


Abin ya zo mata bambarakwai saboda sanin Salihi shi yasa ta ce "inji Salihin?"


"Yasin gashi a nan, na baro shi a gefe da zan amsa wayarki. In kin ce na bashi kwafin takardun sai na bayar." Ya rage murya yadda za ta tausaya masa.


"Ka barni dashi. Kada ka bashi komai. Kai kaga ma yi tafiyarka ka bar saurarensa. Wannan wace irin masifa ce?"


Maimakon ya wuce gaba sai ya dawo gaban Salihi ya tunkuda hularsa gaban goshi.


"Da kai bada izinin matar taka kazo yi mata kutse a harkokinta ba? Ta ce kada na baka komai. Ko kunya baka ji ba bayan kayi aure matar ta sami ciki sannan ta sani, shi ne za ka lallabo rabata da arzikinta. Ku kuke janyowa ana zaginmu ace bamu da tausayi. Haka fa kwanakin baya ka matsa mata da sai ta ranta kudin makarantar yara."


Salihi bai taba danasanin auren Uwani kamar yau ba. Banda barin Habibu ya zama uwa da uba gareta yana juyata da sunan shawara harda sirrin gidansa duk ya sani. Allah Kadai Ya san yawan abubuwan da ta sanar dashi. Kala bai iya sake cewa ba ya kama hanyar motarsa yana jiyo dariyar Habibu. Yana hanya  Uwani ta kira shi da tambayar rainin hankali.


"Me kaje yi wurin Habibu?"


"Na baki rabin awa duk inda kike ki sameni a gidan iyayenki."


Da ya ajiye wayar sai kawai ta kama a'uziyya domin ta yarda dari bisa cewa jifa ne ko sihiri aka yi mata. Idan komai zai kwaba bata taba kawowa harda Salihi ba. A zatonta har abada zai kasance tare da ita yana hadiyar bacin rai. Kwafa tayi tare da mugun tsaki lokaci guda da wani tunani ya fado mata.


"Tsafi gaskiyar mai shi. Lallai Mulmule kike ko wa? Ni zaki tarwatsawa rayuwa daga zuwanki?"


Sai kawai ta soma dariya wanda har ya janyo direban adaidaitan ya dinga kallonta ta madubi. Ita kuwa karfin halin amaryar Salihi ne ya saka ta dariyar. A bayyane yake gareta Ummule ce tayi mata asiri. Banda haka me yasa komai bai faru ba sai da tazo gidan? Wata kwafar tayi ta ce da direban Adaidatan ya kaita Dala.


***


"Hummm inji mai ciwon hakori. Ka magantu azo a fara narai-narai da ido ana neman janyo maka zunubin da ba naka ba."


Furucin Asabe kenan bayan Hasiya da 'yan matanta sun gaisheta sun wuce dakin Innayo. Alh. Rabi'u sai ya zata dashi take saboda sun yi sa'in'sa akan  'yar dangin wa ya kamata a sake hadawa da Munzali cikinsu. 


Labule ya daga ya leko da kansa ya watsa mata mugun kallo.

"Dake da Munzalin duka kuna karkashin ikona. Sannan Zakiyyan da suka rabo ba 'yar kanwarki bace ciki daya?..."


Dakatar dashi tayi ta nuna masa dakin Innayo da bakin da ta turo gaba.


"Maida wukar. 'Ya'yan matarka ne naga suna ta sintiri a gidan nan abin ya soma yawa." 


Ta tashi ta koma dakinta yana biye da ita. So tayi ta daga murya wurin fadin maganganu amma Munzali ya ce mata ko labari yaji ta sake takalar Innayo sa rigima zai hanata kudin wata.


"Kwanaki Zara ce ta haihu kullum sai sun zo. Auren Salima ya mutu shima kamar wata uwar zasu iya yi mata suka dinga zuwa. Dazu kuma akan idona Maimuna tazo ta wuce da ledoji harda jakar bacco. Ga Hasiya ita ma ta wuce yanzu. Kar ka manta zuwan mijin waccan kankamojin Uwani shi ma ya ce bai ganta ba. Ni dai ka dauki mataki kafin a fara zaginmu a unguwa."


Buguzum buguzum ya fice daga dakinta ya tafi na Innayo. Ta saka dariya ta zauna jiran tashin muryarsa idan yana fada. 


 Hira ya samu suna yi ga kayan kad'in miya danginsu kuka da daddawa ana ta zuzzubawa a ledoji. A gefe ma akwai ledojin viva biyu cike har baka da danyar masara. Sai kwan zabi cike da katuwar kwarya.


Fuska a sake Innayo ta nuna masa uban kayan dake gabansu.


"Idan kun hadu da Musbahu (mijin Maimuna) kayi masa godiya. Kauye yaje shi ne ya hadomu da abin arziki."


"Ya hadoki dai ke da kike shagwaba shi. Duk wata dawainiyarsu kin dauka kamar ke ki ke auren Maimunan" cewar Alh. Rabi'u cikin fushi yasa kafa ya shure ledar masara guda daya "wai masara kamar wasu mabarata?" 'Ya'yan nasa yabi da kallo saboda duk sun dinke fuska yaja dogon tsaki. Duk tsiyarsu dai shi ne ubansu. Kuma dadin abin yana da Munzali. Tabe baki ya yi kamar anyi masa dole kafin ya fita ya ce "In kun dafa ki miko min inji idan noman ya yi kyau dai."


 Tun a gida Maimuna take cikin farincikin wannan kyautatawa ta mijinta ga iyayenta. Kullum sune masu karba a hannun Innayo ko Hasiya, yau gashi ita ma tana da abin kaiwa gìda asa albarka. Sai gashi tun ba aje ko ina ba Alh. Rabi'u ya yi nasarar kawar da murmushinta. 'Yan uwanta duk sun kawar da kai basa son hada ido da ita don kada su karasa sarar mata da gwiwa. 


"Ina da itace. Zara tashi kije ki dora masarar nan."


Idanuwan sai suka koma kan Zara. Salima ta mike da hanzari tana cewa bari ta dora. Ga mamakinsu sai Zara ta tashi da rawar jiki. Irin rawar jikin nan na mai son burge wanda ya bashi umarni ba na tsoro ba. Ledojin ta kwasa tayi waje ga uban murmushi ta kasa dainawa. 


Sai da ta fita Innayo tayi murmushi tana girgiza kai ta furta kalmar "Zara kenan" da kulawa.


Ita kuwa Zara tana isa waje sai da ta share kwalla. Shareta da Innayo take yi yafi duk wani abu da ya sameta ciwo a yanzu. Daki daya suke kwana amma takaitattun kalmomi ke shiga tsakaninsu. Ta riga ta sauke duk wani dakon rashin albarka da ta dauka akan ahalinta. Shiri take nema da kowa a cikinsu. Da ta dora kin komawa ciki tayi tana ta faman tura icce don tayi saurin dahuwa. Sa'arta daya ma iccen bai nuna mata kurenta ba. Tashin farko ya kama ba tare da ya hada mata hawaye da majina na yaushe gamo ba. Tana jin kukan jaririyarta taki shiga ciki har sai da Hasiya tazo ta kirata. 


"Ke kuma daga hura wuta sai kiyi zamanki ki barta tana kuka?" Cewar Maimuna tana mika mata 'yar.


"Naga duk kwadayin cin masara ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login