Showing 198001 words to 201000 words out of 242549 words
dace Suhaib. Abin da ya kamata nayi tun da dadewa." Ta karashe maganar a hankali tana fita daga dakin.
Da taimakon Allah ta isa dakin da aka saukesu ita da Farha.
I just published "41" of my story "UWA UWACE...". https://www.wattpad.com/1221353664?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=BatulMamman17&wp_originator=dmTI6%2Bd4xW4ySQC9IZSN5Ctp1ECDjPlql7uEEwxNyy6mwmTs5Ncm6yv57bRsBRlDWFHVlr6suRV3pFd4sJuu9eSkRnJfcM3791OugVz9A24ZB4FNIQX9hKS8ACJWWt%2FZ
UWA UWACE...41
Batul Mamman💖
***
Suhaib ya kamata ya kira amma gangar jiki da ruhi suka ki bawa Abbati hadin kai. Haka yatsansa ya dinga jujjuyawa akan sunan Farha yana tuhumar zuciyarsa da rashin jin magana har ya kai ga kira bai ankara ba. Cikin sauri ya kai hannu zai katse kiran sai dannawar tasa tayi daidai da sallamar muradin rayuwarsa. Zuciyarsa wani irin dokawa tayi sai da ya dafe kirjinsa. Ba yadda ya iya dole yayi saurin bin kiran da wani.
Sake dauka Farha tayi cikin macewar jiki da faduwar gaba. Sallamar da ta kuma yi ta riski kunnen Abbati da sautin karaya da tsoro. A take yaji tausayi da soyayyarta sun taso masa. Baya bukatar tuni yana sane da cewa shi mai laifi ne. Cikin kankanin lokaci ya sanya mata rai da soyayya harma da tunanin rayuwa a karkashin inuwa guda. Sai kuma ya soke mafarkin da ta fara ba tare da ya bata gamsashen bayani ba. Barinta cikin rashin sanin tudun dafawa ba karamin cutarwa bane. Bai tashi sanin hakan ba sai yanzu.
Ajiyar zuciya suka sauke a tare wanda sautin ya shiga kunnuwan junansu. Hakan ya sanyasu yin murmushi a lokaci guda.
Farha ce ta fara yin magana da cewa "nayi sallama baka amsa ba"
Tunanin Qibdiyya ne kadai ya hana shi nuna mata zahirin halin da zuciyarsa ta shiga sakamakon jin muryarta kadai.
"Kiyi hakuri. Wa alaikum salam. Kina lafiya?"
"Alhamdulillah. Kai fa?"
"Nima Alhamdulillah"
Shiru suka dan sake yi sannan ya yi ta maza ya ce "Ya Farha muna cikin wani yanayi ne yanzu dake tsananin bukatar addu'a. Don Allah ina neman alfarma ko sau daya ne ki roka mana sauki a wurin Allah."
Tausayi taji ya bata. Ta matsu taji mene ne ya yiwa kyakkyawar alakar da suka fara ginawa shamaki har tazara irin wannan ta wanzu a tsakaninsu.
"In sha Allahu zan yi"
"Baki tambayeni ko meye ba?" Ya ce da dan murmushin karfin hali.
"Na san idan ya kamata naji ba za ka boye ba"
Allah Sarki zuciya. Kalaman Farha kara nutsar da ita suka yi cikin zuciyar Abbati. A kullum yana kara yabawa da irin tarbiya da tsaftar tsatson da ta fito. Kafin ya manta ainihin dalilin kiran nasa ya ce ta yiwa Mami godiya akan taimakon da Suhaib ya yiwa Ayaah kafin su zo Kaduna suyi da kansu. Tunanin sake ganinsa nan kusa yasa ta fada masa cewa suna Kano ga kuma halin da Suhaib din yake ciki.
"Kuna gidan da muka zo biki?"
"Eh"
"Zan zo koda ni kadai ne saboda Munzali ma yau ya fito daga asibiti idan baku koma ba zuwa gobe ko jibi. Don Allah kada ki manta da adduar."
Zai katse wayar kenan yaji ta ce "baka bani abin sadaka ba. Naji ance ku Kanawa ko me zaku yi sai an biyaku"
Dariya ce ta kama shi ya ce "dadin abin kauyenmu a Jigawa yake nima bakon Kano ne"
Da murmushi Farha ta ce "Ai shikenan tunda ka fara rowa"
Da kyar ya iya sallama da ita suka ajiye wayar kowannensu yana jin matsananciyar kewar dan uwansa.
Daga nan zagaye ya dinga yi a titi domin zaman wuri daya ninka masa damuwa yake yi. Wani masallaci ya tsaya a gefen titi da aka kira azahar ya yi sallarsa tare da fatan samun nasara daga wurin Maikowa da komai. Akwai mutane da dama da zai iya kira su wulakanta masa rayuwar Shazali ba tare da ya daga hannu ba. Ya san manyan da zasu yi komai domin farincikinsa. Amma ko kusa ba zai nemi kowa ba. Domin kofar da yake son rufewa ce zata sake budewa. Shi yasa ya zabi kai kukansa inda ba a barin mutum ya dawo empty handed. Kamar jiransa Shazali yake yi kuwa sai ga waya. Sanar dashi adireshin inda zai je yayi da dariyar mugunta. Wannan yasa ya figi motar a guje da fargabar me ya sami 'yarsu.
***
Minti arba'in kafin Shazali ya kira Abbati ya amsa wayar wani kusan gwamnati wanda yake yiwa kawalcin 'yan mata. Da yake zancen nasu ya hada da yadda zasu koma biyan malaman makarantun kwana kamar yadda suke yi a ta maza ana basu dalibai sai ya fita daga gidan. Hirar sirri ce baya so ko Abdul ya san me yake ciki. Mukullan mota ya dauka ya ce masa zai je siyo wani abu ya dawo. Minti goma da fitarsa kuwa Abdul ya kamo hannun Qibdiyya yace ta zo ya kaita wurin mamanta.
Bata yi musun binsa ba don ta soma galabaita. Sam taki cin abinci sannan ga rashin iyaye ko wani idon sani. Abdul gani ya yi tana jan kafafu ya sunkuceta ya goya. Durowar da ya taba gani Shazali ya ajiye mukulli ya duba yaci sa'ar ganin mukullai daban daban a ciki. Lokutan baya bai taba tunanin dauka ba duk da idan Shazali zai fita yana rufe shi a ciki.
Wurin kala shida ya soka a jikin kofar saboda kusan duka girmansu daya kafin ya yi sa'ar jin ta bude. Ajiyar zuciya ya saki gami da sake ruko kafafun Qibdiyya a cikin hannuwansa. Yana sako kafa a waje yaji kamar an dauke masa kansa sakamakon hada kan da bango da Shazali ya yi. A kofar gida ya zauna yana wayarsa. Duk gwajin mukullan da Abdul yake yana ji. Haka ya shigo gidan a harzuke ya banka kofar ta rufe da karfi kafin ya hankada shi. Da kyar Abdul ya iya tsayuwa akan kafarsa don gudun kada ya kifa da baya ya danne Qibdiyya. Bayan ya sauketa kafafunsa ta rike ta buya a bayansa tana kuka. Shi kuwa kunnen bangaren da ya hadu da bangon yaji ya dauke dif sai wata kararrawa ce take bugawa kamar an kada tara a firamare.
"Har kayi tsaurin idon shiga lamarina Abdul? Waye ubanka a garin nan da kake jin ko kasheka nayi za a tada magana ma?"
Abdul babu amsa sai kunnensa da yake ta bubbugawa ko jinsa zai dawo daidai.
Kafadunsa Shazali ya rirrike ya shiga jijjiga shi yana masifa. Abu biyu ke damunsa. Na farko ya san duk kaunar da yake yiwa Abdul ya rasa shi kenan domin ba zai kuma kawo shi gidan nan ba. Na biyu kuwa wani mutum ya wuce ta kofar gidan a daidai lokacin da Abdul din ya tura kofar gidan. Babu tantama ya san cewa an ganshi. Bayan kuma ba a taba jin duriyar kowa a gidan ba.
Da kansa da ya gaji ya sake shi ya nuna shi da yatsa. Har lokacin dai bai dawo daidai ba. Kana ganin kwayar idanunsa zaka gane a cikin dimuwa yake.
"Ka jawowa kanka bala'i don na fuskanci akwai ganganci idan na mayar da kai makarantarku. Ka jirani in kai yarinyar nan wurin ubanta na dawo."
Cikin gidan ya wuce ya tafi dakinsa ya barsu a dan sararin tsakar gidan. Kukan Qibdiyya tuni ya dauke sai ajiyar zuciya saboda tsorata da tayi. A gabanta Abdul ya durkushe ya fiddo wata 'yar karamar waya kirar samsung mai torchlight. A makaranta ma ba a san yana da ita ba. Bai taba kiran kowa ba sai Shazali da suke musayar text messsage. Shi ma kuma bai san yazo gidan da ita ba. Gefen siket din Qibdiyya ya samu ya saka ta ya yi mata nadi biyu. Siket din sai ya dage sama amma ba za a gane da wayar ba saboda dan fadin rigarta.
"Ki boye wayar nan in kin hadu da babanki ki ce ya kira babana."
Da ka ta amsa tana rike dashi har Shazali ya dawo. Hannunta ya fincika ya fita da ita a ransa yana tunanin ko wa zai hadu dashi cikin makota ba zai damu ba domin yana dawowa zai fita da Abdul ya bar gidan gabadaya.
Fitarsu ke da wuya Abdul ya fadi a tsakar gidan. Jini kuma ya dinga silalowa daga cikin kunnen da ya bugi bango ta bangarensa.
***
Duk wata addua da Abbati ya sani ya karanta ta a hanyarsa ta zuwa gidan shakatawar Comared. Manyan motoci ya gani har biyar a harabar gidan. Da yake gidan gona ne mai dan karen girma. A kusa da ta Shazali ya ajiye tasa ya fito ya kira shi a waya. Maimakon ya dauka sai ya fito ya yi masa jagora zuwa ciki. Karfin zuciya ne ya hana shi far masa da duka tun a lokacin saboda bai san me zai sami Qibdiyya ba idan haka ta faru.
A cikin gidan kuwa Alh. Tahir ne zaune a wani daki wanda kofarsa take cikin falon suna magana da Comared.
"Har yanzu babu wani canji dole sai da namijin?" Ya sake maimaita tambayar da bai san sau nawa ya yiwa Comared ba.
Fuska ya kyabe kamar mai jin tausayinsa har zuci ya ce "ko dazu sai da na sake kiransa har nace ko ni zan iya yi maka aikin yace a'a"
"Allah Sarki mutumina. A hakan ma nagode sosai. Na san kai mai taimaka min ne har inda karfinka ya kare."
Comared ya tashi daga bakin gado ya ce "so nake ka kwantar da hankalinka. Yaron kwararre ne ya san me yake yi. Kafin ka farga anyi an gama"
Suna ciki suka jiyo sallamar Abbati domin dai shi Shazali bata gabansa. Hasali ma hankalinsa yana wurin Abdul. So yake ya koma gida ya yiwa yaron rashin mutumci kafin ya watsar dashi a titi.
Falon wayam babu kowa sai kayan ciye ciye da karar tv data AC. Qibdiyya Abbati ya nema da ido babu ita babu dalilinta. Cikin zafin nama da gajiya da danne bacin ransa ya riko Shazali ya tsayar dashi a gabansa. Da kakkausar muryar da shi kansa bai san bacin rai zai taba bashi irinta ba ya ce,
"Shazali ina Qibdiyya?"
To shi ma Shazalin bai san dakin da Comared da Alh. Tahir suke yana kusa dasu ba, shi yasa ya bashi amsa babu kwana-kwana. Dariyar mugunta ya fara da ita kafin ya ce,
"Tana nan kalau ko farcenta ban taba ba. Nan da awa guda idan kaso zaka tafi da 'yarka gida. Bukatarmu kawai kabi umarnin da aka baka"
Murya kasa-kasa Alh. Tahir ya tambayi Comared me yake faruwa. Ganin babu wata mafita sannan ya san a cikin matsi abokin nasa yake shi ne ya yi masa takaitaccen bayani. Bai kai ga yin magana ba suka ji Abbati ya daka wata irin tsawa. Su biyun duka jikinsu ya amsa duk da ba dasu yake ba. Barin ma Comared wanda tun isowarsu gidan yasa aka bata maganin bacci. Tana dakinsa na sama yana jiran Abbati da Alh. Tahir su shiga daki shi ma yaje ya afka mata.
"Shazali! Ka fito min da Qibdiyya idan ba haka...."
Cike da dakiyar 'yan barikin da suka yi nisa Shazali ya katse shi da cewa "in ba haka ba sai me Abbati? Kana da abin da zaka iya ne? Duk wani k'usan gwamnati ko maikudin da kake takama dashi ta dalilin wa ka sanshi?"
"Ana takama da Allah waye yake ta mutane? Wawa irinka ne zai dogara da halitta mai kayyadajjen wa'adi bayan akwai Maihalittar da bashi da karshe. Da nace maka ni da Munzali mun tuba ba da wasa nake ba."
"Aikin banza. Wane d'an son zuciyar ne ya ce muku Allah zai karbi irin wannan tuban naku? Shekararku nawa a wannan rayuwar? Kudi da duk wani connection dinku a kasar nan ba jikinku bane sanadinsa? Sai yanzu kuna tunanin kun gama tara abin da kuke so zaku wani ce kun tuba? Malam in zaka sha giya kasha ta duba. Allah Gafurur Rahim ne kowa ya san wannan. Kawai ku cigaba da gashi suya sai ranar sallah. Idan mutuwa tazo ka gaggauta istinginfari me yiwuwa a dace."
Karkada kai Abbati ya yi da murmushin takaici. A matsayinsa na bawa mai tarin zunubi kuma mai neman rahama ya yi imanin cewa shi din ba kowa bane. Amma duk da haka bakinciki mara misaltuwa ya danne zuciyarsa saboda maganar Shazali. Tsanarsa ta kara ruruwa a zuciyarsa saboda kalaman izgilancin da yaji daga bakinsa. Nasa imanin da tawakkalin kuma suka karu domin ya yarda cewa lallai shiriya ta Allah ce. Su da suka tuba ba wayo ko dabararsu bane. Cike da kosawa ya ce,
"Don Allah Shazali ka fito min da ita mu tafi. Bana son wannan case din ya kaimu gaban police."
Sama Shazali ya nuna masa yana yi masa kallon wulakanci
"To ni waye yace maka ina tsoron police? Kaga Abbati ka amince kayi abin nan ka zo ka tafi don nima uzuri ne a gabana. Mutumin nan ya riga ya saba sakarwa mata kudi kamar hauka. Wannan harkar ma don bako ne shi a cikinta shi yasa na nemo ka. "
"Babu ruwana da sanin ko shi waye. Da Allah fa nake hadaka akan ka bani 'yata mu tafi. Mece ce ribarka idan na koma wannan kazamar rayuwar?"
"Riba? Eh to ina da riba gaskiya. Zan jidadi na rabaku da tuban da kuke ikirari wanda yasa kuke yi min kallon dan wuta. Munafunci ne tuban naku tunda sai da aljihunku ya yi nauyi da haram zaku ce wai kun komawa Allah. Indai ina numfashi sai kun koma ruwa."
Murmushi Abbati ya yi mai ciwo. Bin Shazali ta laluma ba zai kara masa komai ba sai bacin rai. Idanuwansa ya daga yana kallon fanka wanda a zahiri zuciyarsa ce take fuskantar Mak'aginta.
"Ya Allah idan tubana dominKa ne, kuma niyyata ta barin dukkan abin da na mallaka ta haramtacciyar hanya dominKa ce ina rokonKa da ka tsare Qibdiyya. Kasa su fito da ita da kansu. Ya Allah kada Ka bawa Makiyanka dama a kaina da abokina. Kada Ka basu ikon sake mayar damu kazamar rayuwar da ka haramtawa bayinKa."
Kafada Shazali ya kada irin na ka yiwa kanka ya ce "Tunda baka da rabon arzikin nan to ka zauna ka jira Qibdiyya. Tana can ubangidana yana morar jikinta. Na san zamu sami fiye da abin da ya kamata a biyaka"
A guje Abbati ya tashi ya yi hanyar benen jikinsa yana rawa ga gumin da ya wanke shi a take. Ko rabin benen bai kai ba Shazali ya finciko shi ya fado. Akan hannunsa daya ya fada kuma yaji karar da ya yi amma hakan bai hana shi mikewa da zafin nama ba ya bangaje Shazali ya sake nufar benen.
"Qibdiyya! Qibdiyya!!"
Da Shazali ya sake riko shi rufe masa baki ya so yi saboda gudun kada Comared yaji hayaniyar. Idan ya rasa kudin wahalarsa ta kawo Abbati gidan nan ba karamin abu zai yi masa ba domin huce haushi.
Hannun da ya kai da nufin toshe masa baki Abbati ya damko ya sami sa'ar janyo shi ya kifar dashi a kasa. Bai dakata ba saboda tsananin bacin rai da kunar zuciya ya haye kansa ya shiga kai masa duka ko ta ina a fuska da lafiyayyen hannunsa. Cikin kankanin lokaci baki da hanci suka soma fitar da jini.
Duk kokarin Shazali da son ture shi ya kasa. Ihun neman ceton da yake yi da kyar yake fita saboda wahala.
Tun farkon maganganunsu Alh. Tahir yaji jikinsa yayi sanyi da Comared ya fada masa wanda aka kawo yayi ikirarin tuba. Kuma hakan ne ma ya zama dalilinsu na dauke 'yar amininsa wadda bata da maraba da matsayin 'yar cikinsa. Zai iya yin komai dominta. Sai kuma kwatsam yaji ya ce Munzali. Sannan ya kara da ambaton tuba da zantuka masu taba zuciya. Irin zantukan da ya saba jinsu da kalamai masu tasiri fiye da na Abbati daga matarsa. Amma a yau ne kadai ya fara shiga hankalinsa. Harbawar zuciya da gudun jininsa a cikin jijiyoyi ya dadu. Ya san suna Munzali da Abbati da kuma kasancewar Munzali uba ga wata yarinya da bai rike sunanta ba. Matasan samarin dake shirin zama surukansa. Idan ya fita Abbatin da ya kasance saurayin Farha na farko zai gani?
Bai san yadda aka yi ba ya iso kofar dakin zai murda Comared ya kama hannunsa.
"Alhaji kada ka fita don na fuskanci dan iskan yaron nan zai iya bamu matsala. Idan yaga fuskarka bai mana aiki ba tabbas zai iya tona mana asiri. Kuma yadda zuciyarsa take a kusan nan mu kanmu bamu san me zai mana ba. Ka jira in kira security."
Fizge hannunsa ya yi ko amsa bai iya bawa Comared ba ya fita. A halin da ya sami Shazali da Abbati bai san lokacin da ya kwalawa Abbati kira ba bayan ya gama razana da ganin da gaske shi din ne.
"Abbati sake shi kada kayi kisa"
Bai san waye ya yi magana ba amma wuyan Shazali da yake neman shakewa yana maganganu a zauce don duk tunaninsa da gaske ana can ana cin zarafin Qibdiyya ya saki farat daya. Idanunsa hawaye suke fitarwa ya tashi a firgice da tsanar aika-aikan da yaso yi ba don an dakatar dashi ba. Da kakkausar murya ya nuna Shazalin dake kwance sannan ya juya ga mutane biyun da suke tsaye a hagunsa.
"Kai ne mutum na farko da ya fara sakamu cikin wannan masifa Shazali. Kuma har yanzu ka kasa hakura ka barmu mu koma ga Allah. Idan wani abu ya sami Qibdiyya wallahi zaku ga rashin ...."
Bai sami damar karasa maganar ba a sakamakon ido hudu da suka yi da Alh. Tahir. Idanuwansa ne kadai suka kara girma a yayinda wani kololon abu mai daci ya taso daga cikinsa ya tsaya masa a wuya. Cikinsa ya kulle tamau har sai da shiga da fitar iska cikin hancinsa suka soma wahalar dashi. Kafafunsa da yake umarta da su zaga dakunan gidan su nemo Qibdiyya sannan ya fita kuwa suka ki motsawa.
'Zina 'yar aike ce. Duk inda ka turata zata dawo ta isar maka da sako. Bana yi mana fata domin dawowarta gidan nan ba zai taba zama alkhairi ba. Sai dai ina so ka sani koda tayi batan kai da sannu wata rana za a sami mai nuna mata hanya. A lokacin ko bata tuna cikakken sakon ba saboda shudewar lokaci, sallamarta kadai zata hargitsa tunaninmu. Na barka lafiya!'
Ga Alh. Tahir kuwa, wannan sakon na Mami Khadija wanda ta tura masa tun washegarin ranar da Yumna ta fallasa komai ga Farha ne ya dawo masa tar. Ko batan wasali bai yi ba wurin tunano kalmomin daki-daki tamkar yanzu yake karanta su. Hantar cikinsa ta