Showing 201001 words to 204000 words out of 242549 words
buga a tsorace da ya yiwa sakon fahimtar da ta dace dashi. Tun kafin ya bincika yaji ko akwai wanzuwar haramtacciyar alaka tsakanin su Abbati da 'ya'yansa ya gama shiga tashin hankali. Sanin cewa sun taba yin luwadi duk da a yanzu kunnuwansa sun jiye masa nadama da tubansu kadai ba karamin bala'i ya jefa zuciyarsa ba. Ko shi da zina ta gama bin jinin jikinsa ba karamin kyama yake yiwa wannan nau'in nata ba. Haka ya dinga jin kamar ana sassara adda a sassan jikinsa. Bai san wanne daga cikin masifun da suke gabansa ya kamata ya fara yiwa kukan bakinciki ba. Ganin Abbati a wannan gida da sanin waye shi ko kuwa ganin da Abbati ya yi masa da sanin nasa sirrin?
Kallon kallo da suka tsaya yiwa juna ne ya bawa Comared damar tayar da Shazali ya zaunar dashi akan kujera. Da yaga kallon yaki karewa ne ya dubesu da mamaki sosai.
"Alh. Tahir ko kun san juna ne?"
Yawu yaso hadiya domin bayar da amsa amma ya laluba yaji babu danshi a bakin nasa. Kansa yaso kadawa shi ma yaji ya yi masa nauyi. Comared kawai sai ya ce,
"Shi ne yaron da aka dauko 'yarsu ai domin ya amince da aikinka." Yana gama magana ya juya ga Abbati "wannan haukan da kayi a gidan nan baka ci bulus ba wallahi. Idan kana takama da zafin kai ka tarar da ubangidansa. Sai na daureka igiya tayi rara."
A sanyaye Alh. Tahir ya daga kai ya kalli dakunan dake sama ya ce "Comared a wane daki yarinyar take?"
Wani irin duba Comared din ya yi masa sai dai bai iya yin musu ba ya nuna masa kofar da hannu.
Abbati ya kalla fuskokinsu duka babu digon nutsuwa.
"Daukota ka zo ku tafi"
"A'a Alh. Tahir, bangane ba. Ya zaka sallamesu batare da shawarta ta ba?"
"Nawa ne zai fanshi uba da 'yar Comared? Nawa zan baku ku kyalesu har abada?"
Sakin Shazali Comared ya yi ya taso har gaban Alh. Tahir cike da dumbin mamaki.
"Alhaji ka san shi din da gaske?"
"Da ne a wurina. Iyaka abin da zan iya fada maka kenan"
Kai Comared ya kada alamun ya amince Abbati ya hau saman. A gurguje kuwa ya haye ya bude dakin da aka rufe ta waje amma key na jikin kofar. A tsakiyar gadon ya sameta ta dukunkune jiki tana bacci. Kwalla mai zafi ta zubo masa a lokacin da ya rankwafa ya daukota. Jikinta zafi rau da zazzabi. Yana dorata a kafadarsa yaji dumin zafin yana nasar nasa jikin. Ba shiri ya dagota ya dorata akan kafar damansa da ya dora a bakin gadon.
"Qibdiyya. Bude idonki Papa ne"
Da kyar ta bude idon saboda gajiya, yunwa da kuma aikin maganin baccin da Comared ya dura mata. Yadda kanta yake kifewa da kansa kamar 'yar maye ya sake daga masa hankali. Jikinta yabi da hannu daya ya mammatsa domin son ya farkar da ita. A nan ne kuma yaji ya tabo wani abu mai dan tauri a kugunta A razane ya dan daga rigarta ya ciro shi daga cikin siket dinta. Bakinsa da kyar ya iya hada tambayar wayar waye gareta. Cikin yanayin rashin kuzarin da take ta ce masa,
"Cewa ya yi na baka"
Aljihunsa ya tura wayar ya mayar da ita kafadarsa ya sauka. Idan ta dawo daidai zai tambayeta waye ya bata. Da ya sauko babu wanda ya kalla haka ya fita daga falon. Sai da ya isa bakin motar har ya kwantar da Qibdiyya a baya sannan yaji an ambaci sunansa da murya mai rauni sosai. Gabansa ya yanke ya fadi domin bai san da wane ido zasu kalli juna ba balle har su yi bayanin fidda kai.
***
Minti goma sha biyar da isar Alh. Sadisu Nakano makarantarsu Abdul ta hargitse kamar ana cin kasuwa. Tun daga Principal har Masinja babu wanda bai shiga sahun zagaye makarantar ba ana neman Abdul. Principal din yafi kowa rikicewa don sai yau ya san akwai dan Alh. Sadisun a makarantar.
Tun lokacin da yasa aka kawo shi makarantar dama ya bukaci a boye ko dan waye. Kudin da yake turowa domin kulawa dashi kuwa bai bambanta da wanda wasu iyayen kan yi ba sai ta adadi. Malamin ajinsu wanda kudin ke biyowa ta hannunsa yana isar da sako tare da yin tasa bushashar son rai.
Daya daga cikin masu gadi ne ya ruga ya sanar da Principal bakon da suka yi tun kafin su shigo ciki. Principal din ya tashi da sauri ya shiga kankanta ofishinsa domin yana da labarin zuwan bazata da Alh. Sadisu ya kan yi makarantu. A zatonsa yau sallarsa ce ta kama don yasa rai da samun wani abu mai nauyi daga babban bako. Bai tashi shiga tashin hankali ba sai bayan sun gaisa Alh. Sadisu ya bukaci a kira masa dansa. Dan aike wato Masinjansa ya dawo da mummunan labari cewa wai washegarin dawowarsu makaranta ya koma gida bashi da lafiya. Daga nan aka soma diramar!
Tashi Alh. Sadisu yayi tsaye cikin fushi da kaduwa ya hankada teburin Principal din dake gabansa. Ji kake kiyyyy, ya tafi ya daki bango. Abubuwan da suke kai wadanda suka yi zaman dakin kishiyar da ba a shiri da ita suka rufto kasa.
"Bana son zancen banza da hofi. Yaron wajena nake nema Abdul. SS2 B yake. Sunan form master dinsu Sir Balarabe. Hostel dinsu kuma Sardauna House. Ya ce min a kwanar da gadonsa yake akwai Victor da Faisal"
Jinjina kai Masinjan da Principal suka yi na mamakin yadda ya rike komai da ya shafi dansa. Direbansa da PA da suka zo tare basu dauki hakan komai ba. Saurin rike abubuwa suna daga cikin manyan jarinsa da suka kawo shi inda yake yanzu.
"Ranka ya dade zauna bari naje ajinsu da kaina na kirawo shi. Ina jin sakon ne bai fahinta da kyau ba."
Principal dai bai sami damar dawowa ba sakamakon matsalar da ya tarar. Lokacin ba a tashi daga aji ba. Yana zuwa Monita da sauran 'yan aji suka tabbatar masa da cewa kamar yadda aka bukaci su dawo asabar saboda damina ana bukatar gyara makaranta, Abdul ya dawo amma ba a wayi garin lahadi dashi ba.
"Me yasa ban san labarin nan ba sai yau?" Cewar Principal yana gumi tare da tsare malamar dake ajin tana koyarwa a lokacin.
"Ranka ya dade Mal. Balarabe ya kamata ka tambaya. Nima ban san komai ba"
Tare da Monitan ajin da Assistant dinsa ya tafi staffroom din malamai maza. Yana shiga ya kira sunan Mal. Balarabe sai dai nan take aka sanar dashi baya nan shi da wasu malamai biyu abokansa.
"Bangane ba? Ina ya tafi ana cikin wannan yanayin?"
Wani malami ne ya bashi amsa da cewa "babu yadda za ayi ya zauna alhalin duka makaranta ta dauka cewa dan Alh. Sadisu ya bata."
"To shi ya batar dashi da zai gudu?" Ya tambaya a fusace.
Malaman dai basu ce komai ba tunda basu san me yake faruwa ba. Haka ya koma ofishinsa da yaran nan biyu cike da fargabar yadda zai fara yiwa Alh. Sadisu bayani. A inda ya barshi tsaye ya dawo ya same shi yana kai gauro da mari. Yana ganinsa kuwa ya ce ina Abdul.
"Yallabai ka zauna kaji daga bakin yaran nan. Daga nan sai mu san abin yi."
Rainin wayo Alh. Sadisu ya dauki zancen Principal din. Sai dai kuma ance idan rakuminka ya bata ka duba har cikin hudar allura. Bisa wannan dalilin ya saurari Monitan wanda ya maimaita sak abin da ya fadawa Principal.
"Yanzu kai baka ji kunyar cewa na tsaya jin wannan wasan yaran ba? Cewa zaka yi makarantarka babu tsaro har ana shigowa a sace 'ya'yan mutane. To wallahi banda dana. Kai, ina tsammanin baka gane ni ba ko? Suna na Alh. Sadisu Nakano kuma ko uban mutum ne yake mulkin kasar nan bai isa ya hanani koya masa hankali ba." Ya nuna kofa da hannu "kaje ka nemo maigadin da ya kwana ranar asabar din. Da malamin ajinsu duk inda yake..ku hadu ku nemo min dana"
Da Principal da mataimakansa biyu tare da malaman da suka yi cirko-cirko a kofar ofishin kowa hankalinsa ya tashi. Alh. Sadisu ma dauriya kawai yake domin zuciyarsa tuni ta fara karanto masa sunayen abokan hamayyarsa wadanda zasu iya dauke masa da a matsayin fansa ko garkuwa.
"Sir?"
Kowa juyowa yayi don jin wa dalibin dake matsayin mataimakin monita yake kira. Kai tsaye Principal din nasu yake duba ya ce,
"Ina jin fa ba bata ya yi ba. Tun kafin hutu yawanci da daddare ranar juma'a Sir Balarabe yana zuwa kiran wasu a hostel. Yawancinsu da safe suke dawowa. Wasu kuma sai lahadi..." Ya kalli monitan "ba shi ne muke cewa ko lesson ake musu banda mu ba?"
Da ace kunnuwa suna jin gaibu yau da ofishin Principal dinnan ya cika da bugun zukata. Duk wani mai hankali a cikin wurin tunaninsa ya karkata daidai da na uban yaron da ake nema. Wannan kuwa ba bakon abu bane tunda akan ji labarai makamantan haka a makarantun kwana.
Cijewa Alh. Sadisu ya yi ya daure ya tambayi yaron ko mutum nawa ne suka bar makaranta rana daya da Abdul. Babu musu kuwa ya lissafo masa su biyar.
"Amma sauran hudun duka ranar lahadi suka dawo da daddare. Shi kadai ne Sir Balarabe ya ce gida ya koma"
Cikin karaji da gigita Alh. Sadisu ya ce "A nemo min Balaraben da masu gadi"
"Sir Balarabe ya fita"
"Mal. Bawa maigadi baya nan"
"Malaman dake abota da Sir Balarabe ma basa nan"
Wadannan ne amsoshin da suka biyo bayan umarnin da Alh. Sadisu ya bayar. Da aka gama fada dariya ya kwashe da ita. Wata irin dariya mai dauke da bakinciki da bacin rai gami da tsoro. Kamar yadda ya fara ta kuma a bazata haka yayi dif ya daina lokaci guda. Kallo mai ban tsoro yabi mutanen da suke gabansa sannan ya daga waya ya kara a kunne.
"Ku fara aikinku"
Cikin kankanin lokaci gabadaya makarantar ta kasance a zagaye da 'yan sanda. Wasu suka shigo aka fara yiwa duk mai ruwa da tsaki tambayoyi. Ya kira su ne tun kafin Principal din ya dawo daga binciko masa me ya faru.
Ma'aikatan jarida kama daga na gidajen rediyo zuwa tv suma suka soma dafifi. Alh. Sadisu ya tsaya a kofar ofishin Principal da na'u'rorin daukar magana kala kala a saitin bakinsa ya ce,
"Ba roko nake ba shawara ce. Na bada awa biyu kacal a dawo min da dana inda aka dauke shi."
***
Ayaah, Murja da Ummita ne suka tashi daga gaban mahaifinsu da Abdulkarim bayan sun gaishe shi. Kafin su fita ya sake jajantawa Ayaah abin da ya faru jiya tare da shawara gareta da 'yan uwanta akan tsare mutumci saboda gurbacewar zamani. Bayan sun koma wurin Anti Hasiya aikin gabansu suka cigaba. Ayaah kuwa kusa da antinta ta koma ta kwanta ta rufe ido.
"Dalla can tashi, ai kin san yau kece da wanke-wanken safe"
Baki Ayaah ta turo ta tashi rai a bace za ta soma gunaguni Anti Hasiya ta ce ta koma ta kwanta.
"Haba Murja! Yanzu har kin manta abin da ya sameta jiya kike kira mata wanke-wanke? Duka duka yaushe garin ma ya waye?"
Murja da Ummita suka dubi juna suka bushe da dariya. Karfe goma shadaya harda minti bakwai. Shi ne Antinsu take cewa yaushe gari ya waye. Sannan bata tashi ba Ayaah da Murja suka yi fada kamar zasu ari baki a kofar bandaki. Ita kuma tana tasowa ta cigaba da lallabata.
Labarin fadan suka bata ta koma yiwa Ayaah kallon tuhuma. Amma da yake ba a cinyeta da baki sai da ta magantu.
"Dauriya ce fa kawai nake Anti amma har yanzu ban dawo daidai ba. Kuma bana son ki shiga damuwa shi yasa nayi kokarin dawowa daidai."
"Yanzu tsiwa ce daidai dinki Ayaah? Allah nagode Maka" cewar Anti Hasiya tana dariya.
Raharsu suka cigaba da yi cike da so da kaunar juna. Anti Hasiya ta dubesu daya bayan daya ta sake mika godiyarta ga Allah. Irin wannan zaman na ahali daya kuma da zuciya daya tayi ta buri. Sai gashi lokaci guda Allah Ya amsa addu'o'i'nta. Kan yaranta ya hadu sannan ita ma ta sami rabon da zata kira nata. Uwa uba an Abbas yana shirin samun lafiya da yardar Allah.
*
"Ina ta sa ran jin ka tambayeni me yasa na nacewa gidanka naji shiru"
Abdulkarim ne ya yiwa Honourable tambayar bayan sun gama gaisawa sannan ya fada masa daren yau ake bukatar kwantar da Abbas a asibiti. Washegari ake sa ran yi masa aikin da safe. Likitan da zai jagoranci aikin ya iso Kano.
Da yake Honourable ya fishi kwarewa a sakin magana sai cewa ya yi "Wata kake so cikin 'yan matan gidana ko?"
Yadda ya yi maganar kai tsaye ya bawa Abdulkarim mamaki domin bai yi maganar da kowa ba sai zuciyarsa. Zaro idanun da ya yi ba tare da ya ce komai ba yasa Honourable bude baki.
"Don Allah wai da gaske kake?"
Kwarjini Honourable ya yi masa fiye da kullum amma ya san ranar wanka ba a boyon cibi. Tunda dai Ummita ba za ta aurar da kanta ba dole ne ya fadawa mahaifinta.
"Da gaske nake"
Honourable ya gyara zama yana dariyar kunya da takurar da yake gani a tattare da Abdulkarim.
"Murja dai an kawo kudinta. Ya rage Ayaah da Ummita"
Abdulkarim ya dan tura hularsa baya kadan ya ce "Umminmu din nake so. Allah Yasa wani bai rigani ba. Kuma don Allah kada ka sako zancen shekaru wallahi da sauran tafiya kafin nayi hamsin ma."
Dariya sosai ta kama Honourable. Farincikinsa ba zai misaltu ba. Wato da gaske bayan kowane tsanani akwai sauki. Sai dai wani hanzari ba gudu ba...
" Abdulkarim anya baka yiwa Ummita nisa ba. Ba batun shekara nake maka ba. Ina nufin a zamantakewa ta wayewar rayuwa da arziki. Ina jin tsoron kada ku sami rashin daidaito a dalilin ..."
Dakatar dashi Abdulkarim ya yi ya nuna masa rashin jindadin furucinsa.
"Ka sanni kafin na zama wannan Abdulkarim din. Duk abin da na samu a sakamakon kusanci da kai ne a lokacin da nima ban dace da kusantar mutum irinka ba. Amincewarka nazo nema domin na nemi soyayyarta. Ba zan so ayi mata fin karfi ba saboda wani abu da na samu na takaitaccen lokaci"
Fuskar Honourable dai babu komai cikinta sai annuri. Tashi ya yi ya ce masa idan sun gama shiri anjima zasu tafi asibitin zai kira shi.
Abdulkarim sai ya shiga rudani ya ce "maganar Umminmu din fa?"
Wata dariyar Honourable ya sake yi
"Naga dai yanzu ba lokacin tadi bane da rana tsaka amma dai bari na turota kwashe kwanuka."
Kunya ce ta kama Abdulkarim amma abinka da manya sai ya fuske. Ba jimawa kuwa yaji sallamarta a kofar falon. Da ya amsa ya yi zaton zata shigo amma shiru har kusan minti biyu. Ga alamun tsayuwarta a bayan labule yana gani amma taki motsi. Babu mamaki babanta ya fada mata yadda suka yi. Banda haka me zai hanata shigowa don yana ciki?
"Nifa dan gata ne a gidan nan. Idan baki shigo da kafafunki ba ko Ayaah na kira zasu hadu da Murja su daukoki a ka"
Ja da baya tayi cike da tararrabin me ya kamata tayi. Bayan kusan sakan talatin ta matso jikin labulen ta damke shi da hannu ba tare da ta bude ba ta ce,
"Ni wallahi kunya nake ji"
Murmushi ya sami kansa da yi ya taso ya dawo bakin kofar ya tsaya ta yadda suke iya ganin shatin juna. Ummita bata ma san ya iso wurin ba sai da taji amsarsa a kurkusa.
"Banda abinki idan baki ji kunyata ba ai sai ki sa na fara kokwonton zabina"
A wautarta ji tayi amsar tasa bata cika ba.
"Ni kadai ce mai jin kunyar?"
"A iya sanina dai mata sun fi son namiji mai karancin kunya akansu."
"Wai naga kamar 'ya nake a wajenka"
"Wai idan kin dauka kallon 'ya nake yi miki ki ajiye."
Hannu kawai Ummita ta kai ta rufe bakinta saboda murmushin da ta kasa daina yi. Gabadaya nauyinsa take ji sannan tana mamakin yadda ya sake abinsa ya ma manta ita wace ce. Duk da cewa ba yau ta fara sanin soyayya ba, wannan tazo mata da salo mai girman da yafi karfin shekaru da tunaninta.
Zurfafa da tayi a tunani ya bashi damar kallon irin tsayuwar da tayi. A jikin kofar ta dan jinkina sai gefen labulen da ta rike amma taki budewa. Kusa da inda hannunta yake ya kama bata lura ba sai ganin fuskarsa tayi ta bayyana a gabanta. Ja tayi da baya zata gudu ya girgiza kai wanda yanayin fuskarsa da tayi mata kwarjini ta hanata kin bin umarninsa.
"Gajiya nayi da hirar bayan labulen kamar wani mara gaskiya"
"To ka koma zan shigo na zauna"
"Na yafe. Zan dawo anjima idan za a kai Abbas asibiti."
"To Allah Ya kaimu." Ta furta da azama tana son tafiya.
"Dawo Aminatu ban sallameki ba tukunna."
Dagowa tayi a hankali da niyar kallonsa ta kasa. Ya san mamakin sunanta da ya fada take yi. Shima ya yi mamakin rashin mantawa. Kodayake bai taba manta duk abin da ya shafi Honourable ba.
"Nace ba, wai nayi miki kuwa?"
"Innalillahi ..." Furta tare da rufe fuska tana dariya kasa-kasa.
"Ya kike ja min Innalillahi? Nayi?"
Dariyar dai ta cigaba da yi cike da kunya ya ce "in dauki wannan kunyar a matsayin amincewarki kenan?"
Da ka ta amsa masa.
"Nagode Ummi-ta. In sha Allahu ba zan baki kunya ba daga ranar da zama ya hadamu a inuwar aure."
Kafin ta daga kafa har ya fito. Kunya bata barta tayi masa sallama ba.
I just published "42" of my story "UWA UWACE...". https://www.wattpad.com/1221353933?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=BatulMamman17&wp_originator=OAnyjBkYebmtwXfikQ2gExZ08J47W5rzKWjy6t9da0IA7fmudaAWLyyy%2BRSKqIo%2BqhsMo27LctTWW83%2BNlZI7Y0o1BXRgBOlazLJnfP8XBOylR4Ue7I09hup3DQsxy4j
UWA UWACE...42
Batul Mamman💖
***
Kan Abbati a kasa ya kasance har Alh. Tahir ya isko shi a bakin motar. A bakinsa wani irin daci yake ji mai naci domin duk yadda ya kai ga hadiyar yawu yaki wucewa. Halin da ya tsinci kansa baki ba zai taba iya fada ko ya kwatanta ba. Zuciyarsa ce kawai take harbawa fiye da ka'ida. Bai ga wata maraba tsakanin sanin sirrinsa da Alh. Tahir ya yi ba da Farha. Tunda uba ya sani, me zai hana 'yar ta sani? So ya yi su rabu asirinsa a rufe. Gara ta dinga tuna shi a matsayin mayaudari akan fasiki...fasikin ma kuma manemin maza.
Firgici da tashin hankalinsa ko kusa basu kai rabin abin da Alh. Tahir yake ji a dukkan gabbansa ba. Ko tafiyar da yake ba zai iya cewa