Showing 111001 words to 114000 words out of 242549 words
yasa shi yanke shawarar zurfafa tunani da bincike.
Tashi ya yi ya gyara zaman babbar rigarsa.
"Ba dai tafiya ba? Bamu tattauna maganar da ka ce mai mahimmanci bace ba ma" Cewar Alh. Bala shi ma yana tashi tsaye.
"Kada ka damu zan kira ka a waya. Ina da appointment ne da naso mantawa dashi gashi har lokaci ya kusa."
"Au tohhh..." Alh. Bala ya ce yana sakin fuska "ai na zata zuwan dan anacen can ne ya bata maka rai."
Minista bai ce komai ba har suka fito waje. Alh. Bala kuwa sai zuba masa surutu yake yana ta kwantar da kai kamar ya durkusa masa.
*
Da Masinjan nan ya fito bai iya komawa wurin Honorable Habu ba. Zaman jiran bai dame shi ba. Ya zabi ya fadawa zuciyarsa aiki ne ya yiwa Alh. Bala yawa ba wai da gangan yaki ganinsa ba.
Tashin wasu security da sassarfa suna komawa wurin jerin wasu bakaken motoci da ya samu a wurin yasa shi kallon hanya. Farinciki ya wadatu a fuskarsa yayinda ya yi tozali da Alh. Bala. Da sauri ya tashi yana son yi masa magana kafin ya shiga mota. Da ya tashi sai yaga ba shi kadai bane ya nufi Alh. Bala din da wanda suke tare. Sai kalaman fadanci ake ta zubawa ana cewa
"Allah Ya kiyayeka"
Da dai ya gane ba da ubangidansu suke ba sai ya kalli abokin tafiyar sosai wanda shi ma kallonsa yake yi. Baki ya hangame sai kuma dariya da murna suka hana shi magana.
Ministan ne da kansa ya ambaci sunansa cikin wani irin shauki da kewa.
"Habu Kansila? Honorable Namu? Kai ne?"
Honorable ya dinga gyada kai har suka cimma juna. Hannuwansa Minista ya rike yana ta murmushi.
"Abdulkarim kaine haka?"
Sunkuyar da kai ya yi na kunyar rashin kyautawarsa kafin ya ce,
"Naji kunya sosai Honorable duk da dai wallahi na nemeka sosai bayan dawowata aka ce ka bar unguwar. Laifina shi ne na rashin mayar da hankali wurin binciken inda ka koma din."
Alh. Bala sai yaji kamar an sare masa gwiwoyi. Alamun sanayyar dake tsakaninsu barazana ce a gareshi. Hanyar da suka baro ya nuna da hannu yana kiransu.
"Ku zo mu koma ciki don da alamu kuna bukatar zantawa cikin sirri."
Minista Abdulkarim Mamman Diso bai bashi amsa ba sai nunawa Honorable motar da zasu shiga ya yi.
"Bismillah. Kodayake ban tsaya naji uzurin da ya kawoka nan din ba."
Honorable ya kalli Alh. Bala ya kawar da kai
"Wanda nazo gani bai saurareni ba"
Da haka Minista ya gane shi ne wanda yazo ganin Alh. Bala.
A motar suna tafiya Minista yake sake bashi hakurin yankewar zumuntarsu. Ba abokai bane domin kuwa Honorable ya girme shi nesa ba kusa ba. Lokacin da yake ganiyar cin zamarsa ne su Abdulkarim suka fitini unguwa. Rashin kudi ya hana iyayensa tura shi makarantar gaba da sakandire. Kafin wani ya kai zancen kunnuwan Honorable Habu shi ya gani da idanunsa. Har gida ya tura aka kira masa iyayensu maza ya ce zai dauki nauyin karatunsu shi da abokansa su uku. Haka kuwa aka yi. Suka sake JAMB cikin ikon Allah shi kadai ya haye. Yaji dadi sosai ya biya masa kudin karatun. Abokan masa kuma ya basu jari.
Rayuwa tayi ta tafiya har ya kammala digirinsa na farko. Honourable Habu ya soma cuku cukun nema masa aiki sai ya sami tallafi na zuwa kasar waje karo karatu. A can ya zauna ya yi masters da Phd. Kuma nan ne dai ya hadu da dan wani mai bawa shugaban kasa shawara. Da taimakonsa aka sama masa aiki ya fara yana dawowa. Ya nemi Honorable Habu a ranar da ya sanya kafarsa a unguwarsu Diso sai ya sami labarin ya tashi. Da zuci zucin ya kara nemansa ya koma Abuja. Daga nan kuma kujiba kujibar duniya da kai kawo suka dauke masa hankali. Sai gashi sun sake haduwa a inda bai yi zato ba.
"Ina su Abbas kuwa? Ya gama karatu yanzu ko?"
Tambayar sai ta zama fami ga Honorable. Nan ya labarta masa halin da suke ciki.
Abdulkarim sai ya kara jin haushin kansa. Bai ce masa komai ba amma tuni ya gama yanke shawarar irin taimakon da zai yiwa Hoborable da iyalinsa.
***
A gidan Alh. Tahir kuwa Mami Khadija ta cigaba da shirye shiryen bikin autansu. Mama Nasima kuma ta matsawa Mardiyya lamba da tambayar yaushe Munzali zai dawo.
"Kinga ya tafi kafin mu samu ayi maganar da ta dace. Ni ba so nake kuyi ta batawa juna lokaci da hirar waya ba." Ire iren zantukanta kenan kullum.
Ita kuwa Jiddo ta shiga tsaka mai wuya a wurin kawaye. Karyar da ta zuga musu akan hadin kai da jindadi da ta samu a wurin Danliti makanike ce take neman tarar da ita. Mutum biyu cikinsu kuma harda shugabarsu a ciki sun nemi ta hadasu dashi. A cewarsu harka da talakawa marasa galihu tafi dadi. Komai kika yi musu yanzu sai su ji kamar duniya babu kamar ki. Ladabi da biyayya da kuma bin hanyoyin farantawa mace sai kin zaba kin darje. Sannan uwa uba sun fi rike sirri.
Zancen da ake yanzu dai shugabar tasu tana son yaje Abuja ya sameta sati mai zuwa. Mijinta zai yi tafiya kasar waje kuma tana da yakinin da daya daga cikin 'yan matansa zai tafi. To ita ma ta kirkiri tata tafiyar ya kuma amince. Nan kuwa dan gidan holewa ta saya ba tare da saninsa ba inda take kai kwartayenta. Dubu hamsin ta turawa Jiddo ta ce ta bashi ya yi kudin mota.
Jiddo ta rasa inda za ta saka kanta. Tun ranar da ta tura masa hotuna bai kara nemanta ba. Ta saka masa kati na dubu goma babu godi bare na gode. Yanzu kuma har shugabar wadda ake yiwa lakabi da Sarauniya ta fara cewa idan ma taki hadasu ne saboda tana kishinsa zasu saita mata zama. Ai ta san dokarsu babu rowa. Kowacce tana da damar neman saurayin 'yar uwarta. Shi yasa ma suke fadawa juna yadda ta kaya ko wata za ta so.
Uban gayya Alh. Tahir kuwa yana cikin fushin Yakumbo. Ya tsayar da duk wata magana ta auren Yumna saboda abin da tayi masa. A yadda ya tsara idan an fasa akalla nauyin Farha zai ragu a ransa har ya samu su yi magana. Rabin hankalinsa a kwance yake tunda sauran 'ya'yansa babu wanda ya canja masa fuska. Ya san bata fada ba. Ita kadai ce dai har yau bata yarda sun hadu ba. Motsin motarsa ma idan taji daki take shigewa ta kulle kofa.
Yakumbo kuma tayi rantsuwar idan bai auri Yumna ba to ya shirya ganin bacin rai domin babu shi babu ita.
A can wani bangare na zuciyarsa wanda soyayyar 'ya'ya ta rinjaya sai yake jin gara fushin Yakumbo akan na 'ya'yansa. Yakumbo uwa ce. Uwa kuwa a saninsa za ta iya jure komai kuma ta hadiyi komai domin 'ya'yanta. Idan ta kama ya yi mata kuka ne ma zai yi don ya san za ta yafe masa ta janye zancenta.
*
Dan madaidaicin akwati mai taya hudu Farha ta daga ta saka a booth din motarta. Idanunta ta kai kan motar Abbati wadda take lullube a wurin ajiye motocin gidan taji zuciyarta ta harba. Zai yau zai zo gidan daukar motar amma ba zai sameta kamar yadda tayi masa alkawari ba. Sakon da ya turo mata jiya da daddare ta sake maimaitawa a cikin kanta a hanyarta ta zuwa wurin Maminta.
(Zan zo mu yi magana Ya Farha. Maganar baki da baki kafin nayi shirin daukar mataki na gaba wurin mallakawa Auwal muradinsa. Kin mamaye ko'ina a tare dani. Allah Yasa kina tuna ni ko sau daya ne a rana.)
Wani abu mai kama da ana yiwa mutum yawo a ciki taji ya tsirga mata a lokacin don dadi. Ita kadai ta dinga zuba murmushi tana kuma jin kunya kamar yana gabanta. Ashe sunansa Auwal ta fadawa kanta kamar da wani take. Sai da ya soma fitar da rai da samun amsa sannan tayi masa reply.
(Ban san Auwal ba shi yasa bana tunaninsa)
Da wurwuri ya sake turo mata wani
(Amma dai kin san Abbati?)
Kasa rubuta komai tayi tana dariya kasa-kasa.
A bangaren Abbati shirunta sai ya dame shi. Shi fa kaifi daya ne baya son jan rai. Kiranta ya yi kai tsaye ta dauka da wayar da kusa tsinkewa.
"Ya Farha baki san Abbati ba?"
Yadda ya yi tambayar da damuwa yasa ta fasa cigaba da ja masa rai.
"Na san shi." Ta rage murya sannan ta kara da cewa " Kuma ina tunaninsa kullum."
Ajiyar zuciya ya saki tare da lumshe idanu
"To ai ni ne Auwal din. Suna na na gaskiya na fada miki."
Bata san lokacin da tayi dariya ba har tana tunanin ko dan fari ne. Dariyar da ta dinga kurdawa ko ina a cikin Abbati tana saka shi daukar dumi. Tun yanzu yake fatan idan ya sami Farha Allah Ya bashi ita har aljanna. Da wata irin murya mai dadin amo da tsayuwa a rai ya ce
"Ina sonki Ya Farha"
Yadda ya dauke numfashi yana jiran amsarta haka ta dauke nata saboda girman lafazinsa. Ta dade kwarai da cire rai da jin wannan kalmar a kanta.
"Kin barni da faduwar gaba."
"Nima nawa gaban faduwa yake" ta bashi amsa da dukkan gaskiyarta.
"To yanzu ya za ayi kenan? Da sai nan da kwana uku zan zo daukar motata amma na fasa. Tunda gabanki na faduwa gobe zan zo in sha Allahu."
Kunya ta ji ta sake yin shiru har sai da ya tambayeta me yasa bata son yi masa magana sosai. Bai san hira irin wannan gabadaya bakon abu bane a gareta. Kawar da zancensa tayi ta sako wata hirar daban.
"Yaya su Baaba? Don Allah ka ce ina gaisheta."
Sai da ta yi dariya ya ce "ba damuwa don kin bagarar da zancen. Gobe kinga sai ki bani amsa muna kallon juna. Kinga ni na huta tunda dama ba iya fada zan yi a gabanki ba don nima ina jin kunya. Baaba kuma tana lafiya. Zuciyata tana ninka son mai mutunta Baaba. Ki gaishe min da Maminmu."
Katse wayar ya yi ya barta da murmushin da masana zasu gane na sabon shigar soyayya ne.
Sai dai nishadin da take ciki bai dade ba ya rugurguje. Alh. Tahir ne ya kirata sau biyu bata daga ba sai ya kira Mami Khadija ya fada mata sako ta bata. Suna gama magana kuwa ta kirata ta sanar da ita.
"Abbanku ya ce ki same shi a falonsa goma na safe."
Kuka ta soma tun kafin ta gama jin sakon.
"Mami don Allah..."
Daurewa Mami Khadija tayi domin ta san abin da zata fada mata shi ne daidai.
"Wasan buyar da kike dashi ya isa haka. Kije kiji kiran me yake miki"
"Mami?" ta furta da kyar saboda kukan da yaci karfinta.
"Sai da safe Farha."
Ita ma kukan ne ya taho mata shi yasa ta katse kiran.
A daren Farha ta hada kayanta a akwati. Gari na wayewa ta karasa shiryawa. Ita ta tashi Mami Khadija da ta shiga dakinta.
"Gidan Mama zan tafi na zauna har a gama bikin Kawu."
Ta san za a rina dama. Farha can be stubborn idan abu bai yi mata ba.
"Da izinin wa za ki tafi?"
Zubewa tayi a gaban gadon ta marairaice mata.
"Don Allah ki barni in tafi Mami. Idan naji zuciyata za ta iya daurewa inyi magana da Abba zan dawo." Tayi maganar kwalla na zubo mata.
"Au...bama ki da niyar dawowa in an gama bikin kenan?"
"Please Mami"
"Naji. Allah Ya tsare. Kada dai ki manta duk dadi ko rashinsa ba a canjawa tuwo suna."
Kai ta gyada ta mike. Har ta fita bata bar fassara kalaman Mami na karshe ba. Jinjinawa mahaifiyarta ta tayi domin ta fahimci ko da bata fadi me ta gani ba ita ma ta san ko meye. Ita kam bata son fasiki kuma bata jin zuciyarta tana da kwarin daukar cin amanar namiji. Kofa a bude take yayi aure amma banda yawon bin matan titi. Bata fatan abin da zai zo ya gifta har ya sata hakurin zama da mazinaci!
UWA UWACE...23
Batul Mamman💖
Amrah Auwal Mashi da Phary BB ina muku sonso domin Allah.
(Ga duk masoyan Uwa Uwace, masu hakuri tare bibiyar shafukan da nake posting dinsa ina godiya. Dubun gaisuwa a gareku baki daya. In sha Allahu na dawo kenan sai mun ga kwal uwar daka akan labarin nan.....lets go!)
***
Da mukulli Jiddo ta rufe kofarta bayan mai yi mata aiki ta fita ta shige daki. Missed calls din Sarauniya sun fi goma. Sai sakwanni wadanda tun bata bude ba ta san kwanan zancen. Surutu ne da zagi duk akan rashin hadasu da Danladi. Kayanta ta cire bayan ta rurrufe tagogi ta haye gado ta dauki hotuna kala kala wanda muninsu yafi na farko. Ta dai tabbatar bata hada da fuskarta ba. Wayar Danladi ta kira yana gani bai dauka ba sai kawai ta tura hotunan tare da sakon magiyar ya amsa gayyatarta. Ta kara da fada masa nemansa da Sarauniya take yi.
(Ta bani dubu hamsin na baka kayi kudin mota zuwa Abuja. Ladan aikinka zai iya fidda kai daga talauci. Ni da kai duka zamu karo da abin da za ta biya. Sai naji shawarar da ka yanke.)
A kwance yake ya gama karewa hotunan kallo ya karanta sakon nata. A gigice ya tashi har ya barar da dan kofin silba din da matarsa ta ajiye masa ruwa a ciki. Dubu hamsin kuma kudin mota kadai?! Hannunsa kaikayi ya kama yi yana son kiranta amma wata zuciyar ta hana. Wai kada ya nuna mata shi din kwadayayye ne.
Jiddo kuwa da ta tabbata yaga hotunan sai ta kira shi. Da irin salonsu na gogaggun mata take masa magana.
"Danladi mata aka sani da jan aji amma sai gashi lokaci guda kana ta dagula min lissafi. Shin ko dai abin da na turo bai burgeka bane?"
Sai da ya hadiyi yawu da kyar saboda muryar ta tuna masa irin hotunan sannan ya dan yamutsa fuska ya amsa mata kamar ba ya so.
"No ba haka bane. Kawai ina busy ne."
Jiddo ta murmusa. Dan hannu ne babu tantama. Kyale shi za tayi ya ja ajin sannan ta fadi bukatunta.
Danladi ya gama kwanakwanarsa ya mika wuya. Ba wai son zuwa ne baya yi ba tun farko dama. Kawai dai yana tsoro ne ganin cewa matar manya ce. In bai manta ba, motar da ya gyara musu da kayan jikinta babu alamar talauci ko kadan a tare da ita.
"Ku sa min rana amma banda satin nan."
"An gama" cewar Jiddo cike da nishadi.
Jan shi ta dinga yi da hira har ya dan saki jiki. Suna gama wayar hankalinsa ya karkata kan Ayaah. Ita ce irin macen da ya dade yana muradi. Irinsu Jiddo sai dai aje aci kudi kawai a dawo. Ayaah kuwa su ake kashewa kudin idan akwai su. Dakin matarsa Raiha ya shiga tana zaune da yaransu biyu tana basu kunu.
Aikin sa yana kawo masa rufin asiri daidai gwargwado amma saboda karya da yawon bin 'yan mata ya kasa wadata gidansa. Yau tashi suka yi babu ko sisi a jikinsa sai makota ta shiga ta karbo bashin kunu. Shi ne suka sha da safe, rana da kuma yammacin yanzu da ya gama sanyi kalau.
"Wani abin kake so ne?"
Ta tambaye shi a ladabce ganin ya tsaya a bakin kofa yana ta binsu da kallo.
Tabe baki ya yi kafin ya ce "bani darin da na baki dazu zan dan fita."
Danne zuciyarta tayi ta ciro darin daga cikin riga ta mika masa. Bai ce mata komai ba ya juya abinsa. Ludayin da take bawa yaran kunu taji ya mata nauyi ya sabule daga hannunta saboda bakinciki. Dan kudin da ya bata take cancanawa za ta saya musu awara suci mai dan nauyi da daddare shi ne ya karbe.
Kamar kiftawar ido da bude shi don ko gyara zama bata yi ba ya sake shigowa ya wuce dakinsa. Katin naira dari ya siyo ya saka a wayar ya dannawa Ayaah kira. Yaci alwashin yau zai fara dorata akan manufarsa. Ba zai bar gidansu ba sai ya rungumeta.
*
Wanki take ta kunna rediyo tana sauraron wani shiri da akeyi a tashar Freedom mai suna Sabon Shafi. Shirin yana burgeta matuka domin ana hira ne da mata da suka yi fice a fannoni daban daban. Burinta wata rana ace za ayi hira da Hajara Habu Danmalam, fitacciyar....
Tunaninta ne ya katse ba tare da ta gama tsara matakin da take son kaiwa a gaba ba sakamakon shigowar waya. Daga kai tayi kan dan dakalin da suke ajiye guga inda wayar take taga sunan mai kiran. Da sauri ta goge hannunwanta da zanin jikinta ta amsa kafin ta katse.
Sai da tace hello sau hudu Danladi bai amsa ba. Yana jin ciwon tafiyar kudinsa a banza amma dole ya hakura idan yana son cin wannan yakin. Wani jan numfashi ya yi kamar wanda ya yi muguwar gajiya sannan ya kira sunanta da kwantacciyar murya.
"Ayaahhhh. Me na yiwa mata suke guduna haka?"
Daburcewa tayi da salon maganarsa. A lokaci guda kuma kalamansa suna tayar mata da hankali. Duk yadda akayi matarsa ta kuma guma masa wani abin.
"Mata har nawa ke gudunka?"
"Wadda kika sani dai ta gidana, sai kuma ke da na daukeki wata babbar jigon rayuwata. Kwana nawa baki ji daga gareni ba amma ko dan tes dinnan ya gagara ki ji lafiyata."
Kanta yayi gingirin kamar an dora farantin kwai tana tsoron ya fado ya fashe. Zuciyarta kuwa shawagi ta dinga yi mata a kirji saboda tsananin farinciki. Da tattausan lafazi ta soma bashi hakuri. Da ya san katin yana daf da karewa sai ya katseta.
"Na san dai ina takura miki da matsalolina amma don Allah I am sorry. Bana son Mom ta sani. Ke kadai zuciyata ta amince ta dinga fallasawa sirrinta. Idan kina gida zan zo da anyi magariba."
Cikinsa a take ya bada wani sauti kamar yana rokon shi ma a kaishi gareta ya sami abinci. Shu'umin murmushi ya yi ya dan daga murya,
"Dalin, kin dafa min indomie din ne?" Ya dan yi jim kadan "naji. Allah Ya baki hakuri. Idan na fita zan nema. Kina son wani abu ne na taho miki dashi?" Ana fara warning na yanzu kudin zai kare ya ce da Ayaah "sorry na barki ina magana. Idan nazo zan kiraki."
Mace mai tunani za ta fassara hirarsu Ayaah da cewa Danladi (Dani) ya cancanci a tausaya