Showing 228001 words to 231000 words out of 242549 words

Chapter 77 - UWA UWACE COMPLETE BOOK by Fatty Noor.txt

09 Oct 2025

3342

ciwota a bandakin na maganganun da suke tashi ta kasa tsayawa tayi wankan a nutse.

"Wace ce Anti?" Ta tambayesu rai a hade.

"Anti Laurat matar Daddynmu" Mas'uda ta bada amsa da sauri saboda tsoron tsawar Uwani. Fuuu....Hasiya tayi waje a fusace.

Innayo kuma ta dubi yaran ta nuna musu Zara "wace ce wannan a wurinku?"

Da yake rabonta da haihuwa bayan tayi ta ruguntsumin kwanika shekara biyar ne, babu wadda bata fahimci tambayar ba a cikinsu.

"Mummy ce" "Mummy" " suka amsa tare.

"Na san kuna zuwa Islamiyya. Mene ne hukuncin masu sabawa iyaye har su sanyasu kuka? Ina Allah zai saka shi?" Tayi tambayar ga manyan.

Maryam da Mas'uda sai da suka zaro idanu a tsorace sannan suka ce "wuta"

Uwani na jin haka hantar cikinta ta tsirga.
"Mu dai mun roki gafara kuma ance an yafe mana ko Zara?"

Zara ta murmusa don idanun Uwani sosai suka bayyana tsoratar da tayi. Innayo ma sai da tayi murmushi sannan ta ce da yaran idan ba wutar suke so ba kada su kara yin abin da zai bata mata rai.

A hankali suka shiga matsawa jikinta. A karo na biyu Salima ta sake nuna musu kanwarsu. Ba bata lokaci suka tafi. Tun suna dan ja baya har suka ware. Ganin haka Innayo ta ce da Zara sai ta tashi tsaye wurin dawo dasu turbar da ta dace. In ba haka ba nan gaba ba za ta iya tankawarasu ba. Kanta ta sake tunawa da yadda tayi ta ta rayuwar. Cikin rashin gajiyawa ta sake bawa Innayo hakuri.

A waje kuma Hasiya ce tsaye akan dakalin gidansu tana fuskantar Alh. Unaisu.
"Saboda ka kara aure sai ku koyawa yara tsanar mahaifiyarsu? Kaga irin kukan da Zara take yi kuwa? Hakkinta ba zai barku ba." ta kare da goge kwallar tausayin yayarta.

Alh. Unaisu ba shi da zabin da ya wuce yin murmushi bayan ta gama magana. Dalili kuwa shi ne tunawa da labaranta da ya kan ji daga Zara tun ma kafin su yi aure. Tana yawan fadin masifar Hasiya musamman idan aka taba nata. Bai taba zaton za ta damu da damuwar Zara ba duba da rashin jituwarsu. A nan dole ya godewa Hajiyan Fatakwal da ta zama sanadiyar komawar Zara gida.

"Dariya ma na baka?" Hasiya ta tambaye shi a hasale da taga yaki magana.

" Yi hakuri Hasiya kuma ina so ki saurareni game da Laurat da kin zuwana"

"Don kana auren yayata bani da hurumin son sanin dalilin karin aurenka. Rashin zuwa kuwa ni ban san me ya hadoku ba. Matsalata shi ne komai lalacewar uwa ko uba babu ruwan dayan wurin dasawa yaran kiyayyar dan uwansa."

Jajirtacciyar mace ce kuma kaifi daya babu karya ya ayyana a ransa. Sannan ya zauna ya yi mata bayannin duk abin da ya faru har zuwa yanzu. Domin kara horar da Zara da karya lagonta Hajiyan Fatakwal ta sanya shi mikawa Laurat uwargidansa yaran. Zaman Zara ne tuntuni yake karya matsayinta tunda ita bata haihu ba. Shi yasa da wannan damar da ta samu ta fito da makirci kala kala tana juya kan jama'ar gidan. 'Ya'yansa da masu aiki kamar su kwanta mata saboda yadda take kyautata musu. Suka daina ganin girman kowa sai yadda ta ce. Hajiyan Fatakwal na ganin haka ta ce zama bai ganta ba. Da alama da abubuwan da take yi ba wai da kisisina ta dogara ba kadai ba. Shi ne ta ce ya dawo da matarsa tunda yaran ko su yanzu basa gaisarwa sai ta amince.

Tare suka koma ciki. Zara na jin muryarsa gabanta ya fadi. Ta tashi da sauri za ta shige daki. Alh. Unaisu da nasa saurin ya tareta zai karbi jinjirar ta karkace gefe guda tare da rankwafawa da nufin hana shi.

"Bana son sakarci Zara."
Cewar Innayo tana kallon kafafunsa da ya shigo mata har nan da takalma.
Kafar ya bi da kallo shi ma ya koma da baya ya cire takalman. Da ya dawo ya zauna Zara taki mika masa 'yar ta kuma ki kallonsa. Sai ma yaran da ta cewa su shige dakin su jirata.

Shi ma din sai bai bi ta kanta ba. Innayo ya fara gaisarwa sannan ya dora da ban hakuri akan rashin waiwayo iyalinsa.

"Matsayin aurenku nake son sani kafin komai." Shi ne abin da ta ce da shi.

Sai da ta fada ya auna ya ga lallai fa dole ayi tunanin ya daina auren.

"Aure yana nan Innayo. Ku gafarceni akan abin da ya faru" nan ya fada mata abin da ya sanar da Hasiya a waje "zancen da nake muku Hajiya ta ce kada na koma gida ba tare da Zara ba. Ta karbi kuskurenta na hukunta ta ta wannan hanyar akan abubuwan da take ganin halayya ce da bata son jikokinta su koya. Gyara ba zai yiwu da banzatar da matata a cikin halin danyen jego ba."

"Mu kam tsakaninmu da Hajiyarka sai godiya domin kuwa dawowar Zara gida ta haifi d'a mai ido." Inji Uwani.

Innayo sai ta yi musu inkiya da su basu wuri tana mai cewa "gata nan ku sasanta amma babu inda zata tafi yanzu kamar wadda bata da gata" ta kalli fuskar Zara don ta gani shin amsarta ta sami karbuwa ko kuwa son bin miji zai sa ta nuna bacin rai.

Suna hada ido murmushi da alamun godiya ta yiwa mahaifiyarta. Innayo ta cigaba da cewa "yadda ka bamu hakurin wulakanta min rayuwar 'ya da wasa da lafiyarta, zan so Hajiyar taka ita ma ta zo. Zara ta jima tana bata min rai tabbas, amma duk inda bacin raina ya kai akan halayyarta ba zan taba zuba ido ina kallo ana cin zarafinta ba. 'Yar talakawa ce ka aura amma darajarta tafi karfin in baka ita haka sikau kamar kwanakin da suka gabata basu faru ba."

Kai ya gyada tare da cewa "to" da saurinsa. Zai tashi Innayo ta ce a bashi jaririyar.
Zara ta dora masa ita a cinya tana aika masa da mugun kallo. Innayo dauke kai tayi don ko yaya dama ya dace Zaran ta nuna bacin ranta ko don gujewa maimaici idan yaga kamar bata damu ba.

Kurawa yarinyar idanu ya yi har sai da yaji kwalla ta taru.
"Allah Ya baki hakurin jinkirin ganin wannan rana Ummulkhairi. Allah Ya rayaki Yasa ki yi koyi da halin mai sunanki"

Innayo, Uwani, Salima, Hasiya da maijego Zara duk sai da suka yi mamakin wannan irin karamci da ya yiwa Innayo. Wasu cikinsu ma irin Hasiya da Uwani basu zata ya san ainihin sunanta ba. Ita kuwa Zara murmushin da tayi mai hade da dariyar farinciki su kadai suka yi nuni da cewa ta gama yafewa mijinta.

Su Innayo fita suka yi aka basu wuri. Ya kara bata hakuri da nuna mata cewa shi da ita da Hajiyarsa duk sun yi kuskure a baya. Sannan ba a gyara barna da wata barnar.

"Ba jimawa zan yi ba. Ga wannan ki rike. Anjima zan dawo da duk wani abu da ya dace ace nayi tun farkon haihuwar. Na baki dama ki zabi ranar da kike so ayi taron sunanta a gidan nan. Sai anyi za ki koma."

"Na cancanci haka kuwa Daddyn Mas'uda? Laifukana ga mahaifiyata suna da tarin yawa." Ta furta cikin kuka.

"Ki dauki duk abin da zamu yi yanzu a matsayin lallashi da ban hakuri ga Innayo."

"Kai kuma me kayi banda guje min da kayi..?"

"A bar tada zancen gudun nan mana maman Khairi."

Ai kuwa alkunyar da ya kira sunan 'yar tasu dashi ya matukar burgeta har sai da ta sake yin murmushi.

"Nima da laifina sosai. Ban cika masoyi ba tunda ban damu da daidaita tunaninki akan mahaifiyarki ba."

Bayan tafiyarsa Hasiya ta kebe da Zara kafin su tafi asibiti. Maganganun da ta saba yi mata a baya ta kara maimaitawa. Sai dai wannan karon sun sami gurbi mai kyau sun zauna a zuciyar Zara.

"Miji abokin rayuwa ne kuma mahadin rayuwa. Duk wanda Allah Ya zaba miki a matsayin miji, ki sani cewa alakar ta zarce ke da shi da 'ya'yan da zaku haifa. Aure haduwar dangi shida ce. Naki na uwa da uba, nasa na uba da uba, sai kuma abokan arzikinki da nasa. Idan aka sami matsala tsakaninki da guda cikin nasa ko shi da naki, wajibi ne sai ya taba jindadin rayuwar auren mutum. Musamman abin da ya shafi dangi domin su kawaye ko abokan arziki ana iya canjasu. To amma fa duk wanda kika kawo a matsayin makusanci na jini ko na abota, dole ke ce za ki nunawa miji ko shi ya nuna miki mahimmancin dayan a gare shi. Wanda ka mutunta, abokin zamanka ya tayaka mutuntawa. Wanda ka tozarta ko ka wulakanta, wani sai ya fiki ci musu zarafi. Cikin mutanen da na ambata, UWA ita ce tubalin komai. Innayo uwa ce a gareki. Ina fata kin gane me nake nufi."
"Mun gane, kuma mungode."

Tare suka juya suka ga Uwani. Ta karaso ciki ta dubi Hasiya,

"Meye za ki bata shawara ita kadai banda ni?"

"Allah Ya huci zuciyar metiron" cewar Hasiya tana dariya.

"Kin raina ni. Amma muje zuwa. Ba ciki gareki ba? Allah Ya kaimu ranar fafe gora in..."

"Kada ma ki karasa..." Innayo ta shigo cikin dakin ita ma "idan ki ka ci zalin auta rama mata zanyi la'ada waje"

Dakin kaurewa ya yi da dariya kafin kuma su tashi cikin hanzari su cigaba da shirin zuwa asibiti.

***
Tunda Abbati ya san Asabe ta tafi wurin Munzali, Alh. Rabi'u na tafiya ya haye sama. Wanka yake son yi ya dan gasa jikinsa. Dukan da ya sha a police station da fadansu da Shazali sun sa jikinsa yin tsami. Su Baaba Mari ma dakunan da aka saukesu suka shiga. Fito da komai fili da aka yi yasa zukatansu sun sami sukuni. Abin da ya rage yanzu shi ne kawai a tabbatar da cewa sun nesanta daga wannan rayuwa har abada.

Takun Abbati bai sa Hanne yunkurin tashi ba har ya hawo. Gabansa sai da ya yi mummunar bugawa da ya ganta zaune da jajayen idanun da kuka ya rina. Cikin mutuwar jiki ya karasa hawa ya zo gabanta ya zauna shima jingine da bango. Muskutawa tayi ba tare da tunanin komai ba sai kyankyamin abin da taji game da shi.

Sanin cewa za ta iya tona masa asiri bai hana shi yin murmushi mai ciwo ba. Da kansa ya ja jiki ya sake bada tazara a tsakaninsu.

"Zamanki a nan ya nuna min cewa kin ji komai"

"Naji" ta bashi amsa a dakile.

"Ki saki ranki Hanne. Babu sauran bacin rai ko fargabar da ta rage min a dalilin wannan abu. Duk abin da za ki yi ba komai bane illa tishi akan wanda iyayena suka yi. Allah na sabawa, fargabar ko Ya karbi tubana ya danne duk wani abu mara dadi da ya sameni a sakamakon abin nan"

Gashi dai a hankali yake maganar, amma kalamansa ba karamin haushi suka bata ba. Ta tashi tsaye tana masifa.

"Kana nufin bacin raina ba shi da mahimmanci a wurinka? Kodayake dama ba tun yau na san cewa ba ka sona ba."

Tsareta ya yi da ido ya ce "tsakaninki da Allah ke kina so na?"

Bata zata zai yi mata irin wannan tambayar ba. Sai ta sami kanta da bude baki tana rufewa. Shi kuwa bai yi mamaki ba.

"Kada ki tuhumi zuciyata don nima ba zan tuhumi taki ba."
Kuka kawai ta fashe da shi. Ranta a jagule da bakinciki. Abubuwa da dama ne dankare a zuciyarta wadanda suka haddasa mata bacin rai.

Abbati sai ya mika mata hannu. A zatonsa za ta sake nuna kyama. Sai yaga ta miko nata. Ya rike hannunta suka sauka kasa. Baya son sake kwana da komai a ransa. Idan ta kama duk wani nauyi da hakki ya daidaita shi a yau to zai yi domin gobe ta zama goben dake tattare da budewar sabon shafi. Dakin da su Mal. Sa'idu suke ciki ya kwankwasa tare da yin sallama. Mal. Inuwa ne ya amsa don shi Mal. Sa'idu har ya soma gyangyadi. Suna ganinsu tare suka tashi zumbur kowa ya zauna.

"Abbati fada mata kayi?" Mal. Sa'idu ya tambaye shi yana hankalinsa a tashe "me ya kai ka? Wannan sirrin ai tsakaninka da Allah ne"

"Baba ku yi hakuri." Ya rufa mata asiri bai ce tsayuwa tayi ba bayan ance su tashi ita da Habu.

Zama suka yi akan kafet suna fuskantar gadon da su Mal. Inuwa suke kai a zaune. Abbati ya dubi Hanne ya nuna mata iyayensu,

"Tsayin shekarun da muka dauka a matsayin ma'aurata bisa biyayyar iyayenmu bana jin akwai wanda ya taba damuwa da son sanin ainihin bukata da burinki. Yau gashi kin san abu mafi muni a kaina. Ina so ki yiwa kanki adalci a gaban wanda ya hadamu auren nan ki fadi abin da yake ranki"

"Kamar yaya?" Ta tambaye shi saboda kanta ya kulle ta kasa fahimtarsa.

"A wane matsayi ki ka dauki aurena a da da yanzu?"

Sunkuyar da kai tayi. Mal. Inuwa ya ce kada ta cuci kanta suna sauraronta. Kasa magana tayi har lokacin. Sai da Mal. Sa'idu ya hada da jan idonsa mai sa ayi ko ba a so sannan ta magantu a tsorace.

"Na so auren nan duk da cewa hadamu aka yi. Nayi ta kokarin ganin cewa mun zauna kamar wadanda suka yi auren soyayya amma ban samu ba. Babu abin da na nema na rasa a gidan nan. Sai dai kai da nake zamanka duk kokarinka na sauke hakkina bai hanani jin kamar nesa muke da juna ba. Ra'ayi da tsarin rayuwarmu duka ba iri daya bane. Ko hira muke akan abu daya fuskar da muke kallonsa ta bambanta. Shi yasa tun ina kokarin ganin na shawo kan matsalar har na hakura."

"Ba laifinki bane. Laifin rayuwar da nake yi ce wadda ta hanani ganin aibun nawa tsarin. A ganina ci, sha da sutura da sauran 'yan abubuwan da nake yi sun isa su gamsar dake" cewar Abbati.

"To wai ni yanzu mene ne matsalar? Banda tashin hankalin jin mummunan sirrin mijinki kina son rabuwa da shi ne?"

Sunkuyar da kai tayi da sauri. Abbati ya roki Mal. Sa'idu da ya sassauta mata domin tana da damar nuna bacin ranta. Mal. Inuwa kuma ya ce ta fadi abin da take so shi kuma ya yi alkawarin tsaya mata.

"Babu farinciki a cikin gidan nan. Zaman hakuri kawai muke yi cikin wadata amma kowa rayuwarsa daban. Kudin shi ya rikeni har na kai yanzu. Amma tunda na san silar samuwarsa, wallahi gara min rayuwar kauye da nan. Don Allah Baba ina rokon arzikin komawa gaban iyayena. Zamanmu a lokacin da ban san sirrinsa ba ma bai yi min dadi ba balle yanzu?" Ta daga kai a hankali ta kalli Mal. Sa'idu "Baba ku gafarceni. Abin da naji ba zai taba fita daga zuciyata ba. Ba zan iya zama gida daya da Yaya Abbati da Munzali ba. Zuciyata cikin zargi za ta dawwama matsawar zan gansu a inuwa daya. Nayi imani kuma ba zai taba barin Munzali a kan kowacce mace ba."

Kimamin mintuna biyar ne suka wuce kafin Mal. Sa'idu ya ce "Abbati rubuta mata takardarta. Gobe in sha Allahu zamu tafi tare da ita."

Jikinsu duka su biyun ya yi matukar sanyi. Zaman sama da shekara goma duk rashin dadinsa dole mutum yaji wani iri lokacin rabuwa. Rayuwa suka yi babu duka babu zagi. Babu rashin kunya babu fitsara. Sai gidadancin Hanne da wauta da kuma rashin soyayyar Abbati. Amma su biyun babu wanda yake nufin dan uwansa da sharri. Matsalarsu guda ita ce rashin wannan karsashin da zai sa mutum ya shiga ranka ko babu soyayya. A takure suke da juna, kowa yana gwada sauke hakkin dan uwansa a iya damar da Allah Ya bashi. Irin wannan zaman musamman tunda babu yara sai mutum yaji kamar yana kurkuku. Arziki da wadata basa cike gurbin bukatar zuciya na son samun abokin rayuwar da ya dace da ita.

Abbati ya jima da sanin wannan shi ne kuma dalilinsa na amfani da wannan damar wurin sauwakewa Hanne maimakon neman ta zauna. Idan ya zauna da ita yanzu cutar sai tafi ta da. Domin yanzu aure baya gabansa. Akwai abu mai matukar mahimmanci da ya kamata su fara yi kafin suyi tunanin zama da mata.

***
"Baka ganin dazu kayi amfani da kausasan lafuza akan mahaifinka? A haka kake so ka ja ra'ayinsa wurin sauke akidar da yafi shekara arba'in da biyar a kai?"

Asabe ce tayi maganar tana zaune akan kujera yayinda Munzali ya takure a kasa. A haka tazo ta same shi dama.

"Ki gafarce ni amma ko kalmomi na basu dace ba ina ganin bai kamata ki ga laifina ba."

"Haka ne. Bamu koya muku ba sannan bamu kaiku inda za ku koya ba." Da bai ce komai ba sama da kada kansa gefe ta fahimci amsarta tayi daidai. Tambaya take so tayi masa amma tana tsoron kada su karke kamar yadda ya yi da mahaifinsa. Sai da taga yana shirin tashi ta ce,

"Munzali ka fada min tsakani da Allah wane irin so kake yiwa Abbati. Na san ya kyautata maka sosai. Amma anya saboda wannan dalilin kadai ya dace ka fadawa Alhaji maganganun da ka fada dazu?"

Taune lebensa ya yi gami da rufe jajayen idanunsa. Yana ganin idan bai yi da gaske ba da wuya ya wayi gari saboda zafin zuciya. Me yasa kowa yake yi masa wannan tambayar ne? Ko dai abin da suke zargi game dashi gaskiya ne? Shin mene ne ainihin abin da yake zuciyarsa?

"Zan baki amsa idan na nemota in sha Allahu."

"Munzali?"

"Kiyi hakuri Asabe."

Daga haka ya janyo filon guda daga kan kujera ya ajiye akan kafet ya kwanta a kai. Ko minti goma bai yi vmba bacci ya dauke shi.

***
Da gudu Sauda da Mardiyya suka fito tarbarsu Mami Khadija. Mardiyya harda kukan ganin kafar Suhaib.

"Yaya accident kayi ne?" Ta tsare shi da tambaya tana tattaba kafar.

"Buguwa ce Mardiyya"

Sauda ta ce "Da me?"

"Ku muje ciki" Farha ta katse su tana bin bayan Mami.

Tun tasowarsu daga Kano Mamin ta canja. Su duka sun san wani abu ya faru kuma yana da nasaba da babansu tunda suna tashi aka sanar dasu sun fita tare.

Alh. Tahir bai shigo gidan ba sai bayan la'asar. Yanayinsa ya nuna yana cikin tsananin tashin hankali. Bangarensa ya wuce yau bai tsaya jiran kowa fitowa ayi masa sannu da zuwa ba. Sauda da Mardiyya ne kadai ya san ko ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login