Showing 231001 words to 234000 words out of 242549 words

Chapter 78 - UWA UWACE COMPLETE BOOK by Fatty Noor.txt

09 Oct 2025

3410

tsaya zasu iya fitowa.

Sam bai kula da Mama Nasima dake tsaye a bangaren dinning table da tray a hannu ba sai da tayi magana.

"Diya duk gajiyar ce ka shigo haka babu sallama?"

"Uhm" ya amsa kamar baya so yana mai cigaba da tafiya hanyar dakinsa.

"Ina ka wuce ne? Nayi zaton tare ku ka taso dasu."

Maimakon amsa sai ya tsura mata idanu yana kallonta daga sama har kasa. Ya tuna cin mutumcin da suka yiwa Mami shi da ita a dakinsu. Ya kuma tuna cewa ita ta bayar da shawarar a cirewa Mamin mahaifa kuma ya karba. Tirr da Allah wadai ya yiwa kansa. Tabbas yana daga cikin bambancin halittar namiji da mace son tarayya da mutum sama da daya. Hakan iko ne da ayar Ubangiji SWT. To amma shi wane irin mutum ne da bai san kawaici ba? Me zai sa ya yi masha'arsa a cikin gida da matarsa da 'ya'ya? Be tsaya nan ba duk gatan da Allah Ya yi musu na damar karin aure amma yake yawon bin mata kamar bunsuru.

"Lafiya kuwa Diya?"

Muryar Mama Nasima ce ta katse masa tunani. Ya yi firgigit ya dubeta sannan ya ce ta fita ta kirawo Mami Khadija da Jiddo.

"Kayi musu waya mana" ta ce tana dan murguda baki.

"Ki fita ki yi abin da na saka ki kafin na fito daga wanka"

Da wane bakin zai yiwa Mami magana shi da ita a waya?!

Cikin minti ashirin ya gama kimtsawa sannan matansa duk sun hallara a falon. Ya dauko takardu biyu wadanda ya rubuta ya mikawa Jiddo daya, Mami Khadija ma daya. Mama Nasima ta cika fam da ta tabbatar biyu ne.

"Ina tawa? Alhaji me yasa sam baka son yin adalci ne?"

Za ta kara magana Jiddo ta kwarma wani irin ihu wanda ya fita har wurin masu gadi. Ta tashi tana rawar jiki ta kawo masa takardar gabansa ta saketa a kasa.

"Wallahi, na rantse, wallahi babu inda zani." Ta nuna kanta "ni za ka saka? Ni din? Ko don kaga bana haihuwa?"

Da sauri Mama Nasima ta koma ta zauna nata jikin ita ma yana rawa. Ta kalli Mami Khadija a fakaice amma ta kawar da kai don bata ma son sanin me takardarta ta kunsa.

Sai da Jiddo ta gama hargaginta sannan Alh. Tahir ya zaro wayar Danliti daga aljihunsa.

"Ki godewa Allah baki haihu ba don da yau babu abin da zai hanani bawa danki wannan wayar" ya fada yana mika mata.

Hannu ta noke ta ce "wayar waye?"

"Na zata za ki fini sani. Amma tunda da alama kin manta bari na bawa yayarki Nasima ta karanta"

Kafin ya rufe bakinsa ta karbe wayar.

"Whatsapp za ki bude. Ki nemo sunan da aka sa Kaduna account"

Jikinta ya fara sanyi ta nemo sunan. Tana bude chat din gabanta ya yi mummunan faduwa. Ba hirar ta karanta ba. Hoton farko da idonta ya kai gareshi kirjinta ne tsirara da ta turawa Danliti.

"Na shiga uku na" ta furta a dimauce tana kallonsa "wallahi. Kaga ni. Ban san..."

"Adana zancenki don ba zai min amfani ba. Ina fata dai kin tuna waye"

Nan fa ake yinta. Samari nawa ne suka yi irin wannan hirar dasu? Ai ba za su kirgu ba. Don sun fi wadanda tayi mu'amalar zahiri dasu.

Mama Nasima dai jiki sai bari yake. Ta gama firgicewa don ko ba a fada ba ta fara harbo inda jirgin ya dosa. Dama ta jima tana zargin Jiddo tana yawo sai dai bata da shaida ko guda.

Jiddo tasowa tayi tazo gaban Alh. Tahir tana kuka ta fara cewa sharri ne ake son yi mata. Jikinta ne ta yarda amma bata san waye ya dauka har ya tura ba. Rainin wayon nata ya sosa masa zuciya kuwa. Yana son nuna mata bacin ransa sai ya tuna ba shi da wannan hurumin. A takaice ma ya san cewa sakamako ne ya soma girba tun yanzu. Ya ma godewa Allah da ba 'yar cikinsa bace da bai san inda zai tsoma ransa ba. Janye kafarsa ya yi daga rikon da tayi masa ya ce

"Idan kin gama ganin sakarcin naki bani wayar domin ana bukatar amfani da ita wurin gurfanar da Danliti makanike a kotu"

Kiris ya rage ta kwarma ihu lokacin da ta maimaita sunan da karfi.
"Danliti? Kotu? Wallahi ni dai babu ruwana ko me ya yi"

Tsaki kawai ya yi. Bai kara tanka mata ba ya dubi Mami Khadija da Mama Nasima.

"Khadija ga sakin da kika bukata kamar yadda na alkawarta miki zan yi. Alfarmar da na roka ta ki zauna kafin komai ya kammala na gidan kawai nake nema"

"In sha Allah" ta bashi amsa gami da mikewa.

"Me za ki ce da yaran?" Ya tambaya a raunane.

"Idan ka gama ka same mu a falona"
Ficewa tayi abinta don bata bukatar sanin ragowar me zai tattauna da sauran matansa.

Tana fita Mama Nasima ta cigaba da tsuma. Ita dai ta san indai ba mazan da ta sani kafin aurenta ba, babu wani da namiji da za a danganta ta dashi. Daga ranar da ta haifi Mardiyya ta san cewa gantali ba nata bane. Shi ne ta fada neman kudi ka'in da na'in. Laifinta guda a yanzu wanda shi ma tana ganin namiji zai iya saki dominsa. Shi yasa ba bata lokaci ta zamo daga kan kujera ta hau bashi hakuri.

"Me kika yi ke kuma?" Ya ce da dan murmushi. Ya dade da sanin tana yi. Yana dai kawar da kai ne saboda ganin damarsa.

"Kudi" ta ce tana zufa " idan kayi ajiya ina dauka Diya. Ina maka lalube a jaka da walet.

"Tashi ki tafi."

"Ni dai babu sakin ko? Idan ka sakeni ina zani?"

"Babu. Jeki Nasima. Ina bukatar hutu."

Ai ko bai ce ba dole ta fita. Bata son jimawa kada a fito da dalilin sallamarta. Ita da shi duka sun manta da Jiddo dake sharbar kuka. Sai da ta tafi ya ce da ita,

"Duk abin da na saka a bangarenki da wanda na baki ki tattara ki tafi dasu. Wannan shi ne abu na karshe da zan iya yi miki"

***

Su Farha ne zaune a kasa iyayensu akan kujera sun yi jigum. Alh. Tahir ya rasa me zai ce. Mami Khadija sai da ta tabbatar ba zai iya magana ba saboda tsoron halin za zasu shiga sannan tayi magana.

"A matsayinku na musulmai masu hankali na san kun san kaddara. Wannan kaddarar ita ce ta kawo mu wannan rana da aurena da mahaifinku ya kare."

Sauda da Mardiyya suka fashe da kuka. Su Suhaib da suka san dalili su ma babu wanda zuciyarsa bata kadu ba.

"Mami me yasa? Don Allah ku yi hakuri ku koma" cewar Mardiyya.

"Ya Suhaib ba za ka ce komai ba kana jin abin da take cewa" inji Sauda.

Alh. Tahir sai ya hau gumi. Tunaninsa abin da zai ce shi ne dalilin da ya san yaran zasu yi ta tambaya. Mami Khadija ce tayi belinsa da dabaibayin da ya zargowa kansa tun farko.

"Aure zai yi. Kun kuma san cewa ba haramun bane. Wacce zai aura din ce dai nayi rantsuwar ba zan taba zama da ita ba. Yakumbo kuma ta ce tunda har ya yi magana da iyayen yarinyar ita ma bata yarda a janye ba. Rabuwarmu ita kadai ce maslaha a yanzu."
"Wace ce?" Sauda da Mardiyya suka tambaya a tare.

Farha wadda amsar Mami ta farantawa rai domin bata son kannenta su san halin babansu ce ta bada amsa.
"Yumna ce. Kawata Yumna"

Sauda da Mardiyya ko kallon uban basu sake ba suka fice daga falon suna kuka. Mami Khadija ta dubi su Lilu da ko tari basu yi ba ta ce,
"Ina rokon arzikin ku rufawa mahaifinku asiri a wurin kannenku. Fushinsu yanzu na dan lokaci ne zai wuce sabanin idan suka san abubuwan da ku ka sani"

Daga nan ta fada musu zancen tashi da zasu yi bisa umarmin baban nasu. Basu ce masa komai ba suka tashi suka fice su ma.

"Na gode Khadija. Na gode kwarai da gaske. Ina fatan Allah Ya yi miki sakayya da mafificin alkhairi"

Dakinsa ya koma yana tunanin yadda zasu kwashe da iyayensu idan suka ji sakin. Ran kowa zai baci to amma wuyarta a kwana a tashi, komai me wucewa ne.

***

Gwaggo Jummai mahaifiyar Hanne kuma kanwa ga su Mal. Sa'idu ta shiga ta fito don a mayar da aurenta da Abbati abu yaci tura. Sati guda kenan da komawarta gida. Da ta kasa shawo kan 'yarta ta amince a gyara auren sai ta koma wurin yayyenta. Goyon bayan da taga sun bawa Hanne ranar da tazo gidan ya dagula mata lissafi. Abin har ya kaita ga fitowa tsakar gida tana yada magana.

"Anje an gama kullo munafunci an kaso auren 'yata."

Nan da nan tsakar gida da cika ta jama'ar gidan. Dama tun dawowarsu Baaba Mari da fitowar zancen mutuwar auren ake ta kus-kus a kowacce kusurwa. Don ma ita Gwaggo Jummai ba a gidan take ba. Da bakinciki sai ya kusa buga mata zuciya. Da Hanne ta koma gida tayi ta kokarin samun Abbati a waya sai dai bisa umarnin Mal. Sa'idu baya dauka. Yace masa ya bari su zasu yi mata bayani ba tare da tonon asirinsa ba. Suna gudun kada ya fadi wani abin da zai iya darsa mata zargi. Ko kuma ta tilasta masa mayar da auren saboda ganin girmanta. Sai taki zuwa gidan amsa kiran yayanta. Kullum tana faman kiran Abbati. Ga Hanne taki cewa komai. A takaice ma dai tafi walwala. Ga uban kayan abinci da kudi da ya bata. Zuciyarta fes tunda ta san aurensu kam ko a lahira bata muradinsa. Zaman wa da kanwar yafi mata dadi.

Cikin rumfarsa Mal. Sa'idu ya ce ta dawo su yi magana ta ki.

"Ba zan shigo a ninke ni baibai ba. Ni gabadaya zantukan da kuke yi kai da Yaya Inuwa basu da ma'ana. Ai na jima da sanin Deluwa tana son saka 'yarta a gidan Abbati. Kuna fakewa da rashin haihuwarta bayan ni na san kwadayi ne da hassada."

Deluwa tafa hannuwa tayi don dama itama a matse take da son sanin dalilin sakin. Da canjin da ta gani farat daya a wurin murdadden maigidanta.

"Bana fada da kanwar miji Jummai. Ba don haka ba da kin ji ta wuraren da 'yarki ta gaza har Abbati ya kasa zama da ita."

"Zan saba miki Deluwa" ya fada yana yi mata kallon da yasa ta rufe baki ba shiri. Kanwarsa ya kalla da 'yan ganin kwaf ya ce "rabuwar auren bata da alaka da kowa a gidan nan. Hasali ma 'Yashshafa da kike magana a kanta na riga nayi mata miji"

Deluwa ta san bashi da labarin Sha'aib (Suhaib) na Kaduna. Shi yasa cikinta ya wani murde da taji me yace. 'Ya'yan 'yan uwansa maza da suka rage babu wani mai dan romon da za a sha a cikinsu. Magana ta so yi ya ce tana kara bude baki a bakin aurenta. Haka ta cije lebe ta bar wurin cikin bacin rai.

Tafiyarta ke da wuya Hanne ta shigo. Bata san fitar Gwaggo Jummai ba sai da kaninta ya fada mata. Shi ne ta biyo sawu. Ta iske sun koma rumfar Mal. Sa'idu. Hakuri dai suke ta bata taki yarda saboda har yanzu bata ji kwakkwaran dalili ba.

A yau yawan kallon Hanne ya yi mata rana. Zama tayi ta dubi iyayenta. Mal. Inuwa duk ya fita hayyacinsa saboda tsoron kada karshe Mal. Sa'idu ya rasa zabin da ya wuce fada mata gaskiya. Baaba Mari kuwa dama ko uffan bata ce ba.

"Gwaggo ki yi hakuri. Sakin nan ni na nema. Munje asibiti likita ya ce akwai wani abu a jininmu wanda ya sa da matukar wuya mu haihu tare. Masu irin jininmu basa zama da juna. Shi yasa nake yawan bari. Ya so.mu cigaba da zama. Ni kuma gaskiya ina gudun cinye kuruciyata babu d'a ko daya"

Tunda ta bude baki sai yanzu wani abu da ya tokare wuyan Mal. Sa'idu ya sauka.

A take fuskar Gwaggo Jummai ta koma kalar tausayi. Ta girgiza kai tana cewa "ban san abin haka yake ba. Yaya ku gafarce ni. Tabbas lalura idan ta shafi haihuwa maslaha ake nema. Amma me yasa baki fada min ba?" Ta kare da tambayar Hanne.

Hanne bata yarda ta kwashe laifin karyarta ba. Idan bata gyara zancen ba zasu dade Gwaggonta tana mita. Nuna mata tayi basu dade da yin gwajin ba. Abbati yaki yarda ya saketa da ta nema. Shi ne ya kira iyaye don ayi sulhu. Su kuma suka goyi bayanta.

Gwaggo Jummai ta dinga bada hakuri. Da Baaba Mari ta tashi har daki ta bita tana ta rokon tayi hakuri akan kalaman da ta dinga yi. Ita kuwa da ta san cewa ita ce ta karu da abin da ya faru, da wuri ta nuna komai ya wuce. Bayan tafiyarta ta kira Abbati ta sanar dashi. Ta kuma jaddada masa ya yiwa Hanne godiya sannan ya cigaba da tuba.






***
48


Zaune yake gaban likita na goma sha uku cikin jerin likitocin da ya ziyarta domin magance matsalarsa. Amsa yake nema don ya san a wane babi zai ajiye lafiyar kwakwalwa da tunaninsa.

Ya gama bayani tsaf akan yadda ya dauki Abbati da zargin da mutane makusantansa suke yi masa kamar yadda ya yiwa sauran likitocin. Ya kare da cewa,

"Bayani nake so a mahanga ta addini. Idan bani da rabon samun rahama ne saboda irin tunanina gara..."

"Subhanallahi" cewar likitan da sauri "Munzali wannan magana taka bata dace da dan musulmi ba. Ni ba malamim addini bane. Amma tabbas har yau ban bar gaban malamai ba. Na kuma godewa Allah da malumanmu na yanzu suka kasance masu ilimin boko wanda yake taimaka musu wurin warware matsalolin da suke tafe da zamani. Idan za ka iya gobe ka zo nan da la'asar. In sha Allah zan kai ka wurin Dr. Abdallah Saraki. Kawu ne kuma siriki a wurin abokina Dr. Huzaifa."

Tun bayan zaman nan da aka yi a gidan Abbati sati biyu da suka wuce, sai yau Munzali ya yi murmushi. Da ya tashi zai tafi likitan nasa ya ce su taho tare da Abbati da iyayensa.

"Hakan ne zai sa kowa ya sami gamsuwa akan amsar da zai baka"

Yana shiga mota ya kira Abbati. A lokacin shi kuma yana cikin ofishin Alh. Sadisu. Kiran na shiga ya dauka da sauri.

"Munzali lafiya dai ko?"

"Lafiya kalau. Kana gida ne?"

"Ina office din Alh. Sadisu ne. Yanzu muka dawo daga duba Abdul"

Munzali yaji kunya ta kama shi. Ba irin lallashi, fada da nasihar da Abbati bai yi masa ba amma kememe ya daina yarda ko zaman minti biyar suyi a wuri daya. Abbati ya yi fushi sosai saboda ya fuskanci akwai abin da yake boye masa. Shi kuma baya son fada saboda a take Abbatin zai soke masa zargin. Gashi zuciyarsa ta riga ta fara rawa akan maganganun iyayensa. Ya zama wajibi ya san me yake ciki.

"Kwatanta min wurin zan zo na same ka"

Minti ashirin ya kaishi. Suka zauna tare da Alh. Sadisu. A yau godiya mai tarin yawa ya sake yi musu sannan ya koma kan batun abubuwan da yaji a police station din.

"Kuna ganin da gaske zaku iya dainawa? Nayi bimcike ance da wahala rabuwa da wannan dabi'ar. Idan Abdul ya tashi a haka ban san yadda zan yi ba"

Munzali bai yi kasa a gwiwa ba ya fada masa shirinsu na zuwa asibiti a Italy. Rashin zuwa a duba lafiyarsu da kuma neman hanyar rabuwa da lalurar har abada ba karamin kalubale bane ga tubansu. Ita wannan dabi'a tana tattare da matsaloli da yawa ga lafiya. Ciki kuwa harda kasa jurewa rashin samun biyan bukata ta inda aka saba. Wannan abu ya kan fi karfin furtawar baki da yakinin zuci. Wani duk dauriyarsa idan abin ya ciwo shi sai ya biya bukatar yake jin dadi.

"Abdul yaro ne. Sake komawarsa ba abu bane mai wahala. Mafi a'ala shi ma ka kai shi asibiti" inji Abbati.

Godiya ya yi musu da zasu tafi da alkawarin tsaya musu a duk lokacin da suke da bukatar taimakonsa.

"Magana nake son muyi Abbati." Munzali ya ce da suka fito waje.

"Dama jikina ya bani tunda ka kira. Ka gaji da yajin ne kazo biko da kanka?"
Da sauri Munzali ya ce "don Allah ka bar amfani da kalmar yaji da biko kamar wasu mata da miji"

Abbati na jin haka ya gano inda matsalar take. Motarsa ya bude suka shiga ya tayar. Gida ya wuce kai tsaye. Yanzu babu kowa daga kuku sai Maigadi. Iya Kande bata dawo ba tun tafiyar Qibdiyya gida.

A waje suka zauna wurin wasu kujeru da 'yar rumfa. Munzali ya fadawa Abbati dukkanin damuwarsa.

"Na san za ka iya cewa ba komai bane. To amma hankalina ba zai taba kwanciya ba. Don Allah gobe ka zo muje wurin malamin."

Kamar uwa da d'a. Tausayin Munzali ya kama Abbati sosai. Don gudun kara masa damuwa sai bai yi masa yadda ya saba ba idan yana cikin yanayi mara dadi. Lokutan da yake yi masa fada ko nasiha da rarrashi har sai ya sauko.

"Allah Ya kaimu goben. Dama nima ina son yi maka magana akan mu nemi fatawa kan dukiyarmu. Goben sai muje masa da komai muji me zai ce."

Munzali ya mike zai shiga ciki. Abbati ya kai hannu zai taba kafadarsa don ya tsaya sai ya fasa.

"Munzali."

Juyowa ya yi fuskarsa duk ta rame kamar ya dade yana ciwo.

"Ina so ka sani cewa ko yaya makomar alakarmu ta kasance gobe ba zan taba barinka ba"

"Ko da ya tabbata wannan kazantar bata barni ba"

"Zama da kazanta fa sai ka so. A matsayin kani kuma amini na daukeka. Banda an riga an dasa maka wani irin tunani a zuciyarka da na fada maka matsayinka a wurina. Yanzu kuwa ina magana za ka iya tsoron kada nace gobe zan kawo sadaki"

Murmushi suka yi a tare sannan kowa ya nufi gidansa.

***

Washegari basu hadu da safe ba. Munzali ya tafi gida dauko su Asabe. Ya sami gidan a cike makil. Larai da su Fati sun zo dukkaninsu kwai da kwarkwata. Gaban Innayo ta zauna ta roki gafararta na rashin kyautawa da tasa 'ya'yanta yi mata. Ta karbi laifinta kamar yadda 'ya'yanta su ma suka karba. Aka yafi juna tare da alkawarin sabunta zumumci.

Hasiya ce kadai bai samu ba. Hakan ya yi masa dadi domin yana jin kunyarta saboda rashin samun sukunin zuwa duba Abbas. Uwani kuwa tana jin muryarsa ta fito ta tare shi a gefe. Mita ta soma yi masa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login