Showing 225001 words to 228000 words out of 242549 words

Chapter 76 - UWA UWACE COMPLETE BOOK by Fatty Noor.txt

09 Oct 2025

3355

muryar Munzali da ta karade falon cikin rauni, karaya da bakinciki ya mayar da martani ga zargin da mahaifinsa yake yi musu.

"Ba zan janye kalamaina ba. Abbati ya isa dani. Haihuwata ce kadai bai yi ba amma duk wani abu da ya kamata uwa da uba su yiwa d'a ya yi min. A kuma matsayinsa na ALMAJIRI" Alh Rabi'u ya fuskanta da tambaya "ka taba sanin cewa da ina karami ina yawan fama da ciwon namoniya (pneumonia)? Duk lokacin da ya tashi Abbati ke jinyata. Ita Asabe ai ta sani. Ya nemo kudi ta kazamar hanya ya kaini asibiti. Bata taba son sanin a ina yake nema ba tunda ba ita yake tambaya ba."

"Ke, yaushe aka yi haka ban sani ba?"
Ya tambayi Asabe a zafafe.

"Ban sani ba" ita ce amsar da ta bashi.

"Kun gani ko?" Ya nuna iyayen nasa yana girgiza kai "Abbati ne ya kaini makarantar boko ta yaki da jahilci. Yasa muka koma zuwa makarantar dare duk da mun san cewa mu din masu aikata laifi ne. Sannan tuban da muke hanyar yi shi ne dai sila kuma jagora. Ya yi min komai wallahi. Ya cancanci girmamawa da mutuntawa. Tunda ya ce na tafi gida kuma zan tafi domin wannan almajirin yana da iko da ni" yana kaiwa nan yasa kai ya fita ko waige babu.

"Malam ina neman izinin yin magana"

Abbati ya kai idanunsa ga Baaba Mari ita kuma tana fuskantar Mal. Inuwa. Kai ya gyada mata da sauri sauri don ya san zancenta a kullum abin duba ne.

Asabe da Alh. Rabi'u ta yiwa magana da cewa "Da farko ina son baku hakuri akan duk wani abu da Munzali da Abbati suka yi wanda ya bata muku rai. Abu na biyu kuma ina son tunatar da mu duka cewa zama iyaye ba a ciki da haihuwa bane kadai kamar yadda Munzali ya yi ta nanatawa. Shiriya da 'bata ba a hannun iyaye yake ba. Amma akwai kokari da dagewa. So, kulawa, sawa da hanawa duk namu ne. Su din basu isa su gyara mana 'ya'ya ba. Amma kuma aikatasu yana kosar da zuciya. Yana sanya nutsuwa da kwanciyar hankali domin mutum ya san idan ya koma ga Allah yana da hujjar da za ta cece shi daga azabar tozarta amana."

"Ni wallahi na karbi laifina Maman Abbati. Zanyi duk abin da ya dace domin gyara kuskure na"

"Ki je wurinsa" Abbati ya ce da ita da farinciki.

Tana fita Alh. Rabi'u ya fita kamar zai tashi sama yana faman hardewa da babbar riga.

***

An fi ganin nisan daren da washegarinsa bawa yake da burin aiwatar da wani aikin da dole sai an jira gushewar daren. Haka mutum zai kwana zuciyarsa tana azalzalarsa da son ganin lokaci duk bayan gilmawar hannun agogo. Wani zai iya kwana yana buga tsaki da k'wafa. Yayinda mai wayo yake dauro alwala ya gana da Mahalicci. Idan hakan bai samu ba ayi ta tasbihi da tahmidi ana neman agajin Maiduka wurin ganin safiyar ta zo daidai da burin mai jiranta.

Mami Khadija a wannan dare bayan sun dawo daga ofishin 'yan sanda ko tunanin kwanciya bata iya yi ba. Duhun dare shi ya bawa Alh. Tahir mafaka ya sami damar sabulewa tuhume tuhumen da suke dankare a kokon zuciyarta.

"Ina da magana da kai" ta ce a lokacin da ta ga yana shirin ficewa daga gidan bayan sun kawosu shi da Comared.

"Ba a nan ba Khadija. Ki yi min alfarmar mu jira gari ya waye mu koma Kaduna"

Rokonta yake. Taji hakan a muryarsa ta kuma gani a yanayinsa. Ba don ta so ba ta amince saboda rufin asirinsu tunda akan ce bango ma yana da kunne. Kwana tayi sallah da jan ambaton Allah har aka kira Assalatu. Nan ma bayan tayi sallah tayi wanka gani tayi rana taki fitowa da wuri. Ba ita ta sami salama ba sai da motarsa ta shigo gidan ya nemi da ta fito su tafi.

"Ba zan bar su Farha su taho su kadai ba saboda tukin Lilu"

"Magana zamu yi kawai na dawo dake"

Ta kula gudun rigima yake. Jikinsa ma duk ya yi sanyi. Sannan ga dukkan alamu yadda bata runtsa ba shi ma haka ya kwana. Ba musu ta bishi. Matan gidan wadanda tuni suka karbi uzurin da Suhaib ya basu na jiya cewar Lilu ya bi saurayin Farha ne ba tare da yiwa Mamin tasu bayanin dalili ba. Shi yasa hankulansu suka tashi. Sai da suka je suka samu 'yarsa aka sace kuma basu dawo ba sai da aka ganta. Shi yasa yau tsokanar Mamin kawai suka dinga yi akan za ta bi mijinta cikin raha ba tare da tayar da zancen jiyan ba. Da zasu tafi har dakin samarin taje ta dauko wayar Danliti dama Suhaib ya cire lock din.

Gidan Comared ya tafi da ita kai tsaye. Suka shiga har falon da Abbati da Shazali suka duku akan boye Qibdiyya.

"Ina ne nan? Me yasa ka kawoni?" Ta tambaya rai a hade tana karewa hargitsin wurin kallo.

Wuri ya nuna mata ta zauna sannan ya bude baki ya fadi abin da yake jin shi ne rufin asirinsa da na su Abbati. Karfin kalaman da ya zube mata sun tafi akan boye laifin matasan ne wadanda zuwa yanzu ya amince da cewa komai na Allah akwai manufa. Wala Allah rufa musu asiri akan yakinin da ya samu na tubansu zai iya rage masa nasa nauyin.

Ya fara da tuna mata shi waye ta fannin mu'amala da mata. Ya cigaba da cewa ya zo gidan ne jiya domin haduwa da 'yan matan sai ya gamu da Abbati.

Katse shi tayi a firgice ta ce "Innalillahi. Kaddai su ma din..."

"Ko kusa" Alh. Tahir ya sami kansa da wani irin karfin gwiwa "kinsan Abbatin ma almajiri ne. Irinsu yawanci babu gata da kulawar babba a kusa. A nan suka hadu da shi wannan Shazalin dake unguwarsu Munzali. Abinka da kuruciya da rayuwar da abinci ma sai ka roka. Bai wahala ba wurin jan ra'ayinsu ya hadasu da manya aka dinga sakar musu kudi suna kasuwanci. Sai da aka bari kudin ya zauna musu sannan aka bijiro musu da irin aikin Shazali na kawalcin maza da mata. Da suka ki amincewa ne fa Shazalin ya dauke musu yarinya. Shi ne abin da ki ka gani jiya"

Mami ta dinga salati da hailala
"To amma kana da tabbas akan basu taba yi ba"

Tunawa yayi da irin rantsuwar da Abbati ya yi da kuma fushin da ya yi akan gara mutuwarsu da su komawa tsohuwar sana'arsu. Sai ya sake zabo kalmomin da zasu kwantar mata da hankali sannan a lokaci guda basu kaucewa abin da ya ji ba.

"Khadija wallahi Abbati bai san ina cikin gidan nan ba da farko. Amma ya yi ta rantsuwa akan gara ya rasa komai akan ya sabawa Mahaliccinsa."

Ajiyar zuciya tayi. Wani abu da ya kwana a wuyanta ya sauka ba tare da ta farga ba. Ta mika godiyarta ga Allah a fili da zahiri da Ya sanya basu cikin masu sabon Allah.

Alh. Tahir shi ma hakan ce ta kasance dashi. Zuciyarsa ta amince da tafiya da sirrinsu Abbati kushewa. Ba komai ya janyo hakan ba kuwa sai ganin cewa izina ce abin da ya faru jiya a gare shi. Kazamin mazinaci irinsa bai isa ya tserewa abin da ya shuka ba. To Amma Allah Buwayi Ya dubi zuciyar uwar 'ya'yan da su kansu Ya kangesu daga zinar. Shin wannan bai ishe shi godiya ba? Da kunnuwansa yaji kalaman tuba da nadamar Abbati. Idan ya hana shi 'yarsa ya san wane irin fasikin za ta hadu dashi? Rayuwarsu curarren zare ne mai wahalar warwara. To amma idan mutum ya nutsu zai gane cewa Allah Shi ne Gwani mai jujjuya lamura domin su dace da rubutun kaddarar allon kowane bawa.

"Ya ganka a nan din?"

Muryar Mami ta sauka a gare shi cike da alhinin amsarsa.

"Ya ganni. Ya kuma alkawarta min ba zasu taba tayar da maganar ba." Wata kwalla yaji ta cika idanunsa ya ce "kinga irin abin da ki ka jima kina fada min duk ya faru ko? 'Ya'yana sun san ko ni waye sannan maneman 'ya'yana ma sun sani"

An dawo inda ya dade yana mata kaikayi. Wayar Danliti ta damka masa bayan ta bude sakonnin da suke musaya shi da Jiddo. Jijiyoyin wuyansa suka tashi suka firfito saboda bakinciki.

Ta fara magana da fada masa zargin da ama yiwa Lilu na bata Qibdiyya. Da tsoron da take kada watarana gangan ta zama gaske. Sai ta koma batun Jiddo
"Tonon asirin wani ba abin kirki bane. Ban taba tunanin yin haka ga kowa ba. To amma ina gudun yadda kaddara ta fada mata nima wata rana za ta zo ta riskeni. Duk wata kamewata da yawan nasihar da nake yi maka ai ba iyawata bace. Ko kadan ban fi karfin Allah Ya jarabceni da aikata wani na'u'i na alfasha ba. Musamman na zina ko danginta wanda kubuce musu yake da wuya. Shi yasa na zabi ka sahale min wannan auren d..."

Mikewa ya yi ba shiri ya ce "Haba Khadija? In kina yiwa Allah ki bar maganar nan zan tuba"

Mami Khadija ta tashi ita ma "Allah Ya haramta zama da fasiki. Aurenmu tuntuni ya dace a raba shi domin in tsira da mutumcina. Zaman nawa me ya haifar banda kwaye maka baya a idon 'ya'yan cikinka?"

"Na tuba"

"Bukata daya ce yanzu ta rage a tsakaninmu. Ina rokonka arziki ka barni in yi maka idda mu rabu a mutumce. Zan yi bakinciki mafi girma da muni ace na mutu ka sanya hannu wurin sakani a makwancina a matsayinka na mijina. Haka kuma zan yi shi ace ina zaman yi maka takaba alhalin baka kasance cikin masu kunyar mummunan aikinsu ba"

Shiru ya yi na dan lokaci maganar ta sami kowace kusurwa a jikinsa ta shiga. Sannu a hankali ya daga kai ya dubeta ya ce,

"Tsanar da ki ka yi min har ta kai haka?"

"Ko kusa. Me zai sa na tsani mijina uban 'ya'yana? Mutumin da ya kyautata rayuwata da ta 'ya'yana da dukiyarsa da soyayya. Kyamar halinka nake yi domin duk dadin mu'amalar mu ta gidan duniya akwai ta lahira. Wadda zata nuna ina mutum ya nufa bayan an kare wannan gajeruwar rayuwar da bata da tabbas. Ina tsoron kada jindadin more rayuwa yasa in daina ganin aibun laifinka harma zuciyata ta daina yi masa kallon haram."

Kuka take yi. Kuka sosai. Ta durkushe akan gwiwoyinta ta daga hannuwa gareshi. A dimauce Alh. Tahir ya tayar da ita tsaye ya yi nufin rungumeta don lallashi amma ta kame jikinta wuri daya.

Jikinsa ya kara yin sanyi. Yaushe rabonta da amince masa a matsayin miji? Shi kansa ya manta.

"Ki yi shiru"

"Ka taimakeni ka sauwake min."

Kamar wani mahaukaci ya dubeta ya ce "Khadija wallahi zan tuba. Ke na ma tuba. Astagfirullah"

"Don Allah. Ka dubi darajar mai cikakkiyar daraja SAW. Ka raba ko igiya daya ce a tsakaninmu don Allah"

"Nace miki na tuba" ya furta hawaye na sauko masa. Bai taba sanin zafin soyayyarta ba sai a wannan gabar "ta yaya zan rayu babu ke? Ta yaya zan zuba ido ki zama mallakin wani?"

Mami Khadija ta daure ta kamo hannunsa ta rike tamkar suna musabiha.

"Ban san gobe ba. Bani da masaniya akan gaibu. Sai dai ina rokon Allah Sarkin Sarakuna. Idan akwai sauran zama a tsakaninmu, kada Ya bani ikon sake aure har na koma gareshi. Ya baka ikon tuba wanda ya cika dukkan sharudda. Ya tsayar da digadiganka akan siradil mustaqim. Ya tasheka cikin bayin da Ya aminta dasu. Ya kuma sake hada aurenmu a aljannah. Amma a duniya kam na gama auren nan in sha Allahu."

"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" a gabanta ya durkushe yana nanata wannan kalma sannan da kyar bayan ta soma fitar da rai ya ce "na sake ki saki daya. Don Allahn da kika sa na sake ki kada ki auri wani. Ki jirani. Ko a duniya ko a lahira zan tuba. Wallahi na tuba. Kai...me ya kaini? Wannan wane irin zalunci na yiwa kaina?"

Jikinta ya dauki rawa da jin kalmar sakin. Ta jima tana nema. Ashe duk dauriyar da take tunanin tana da ita bata kai ta kawo ba?

"Ina da gida a Kabala zan baki. Ki jira a gyara takardun in sanya sunanki kafin ki tashi."

"Nagode"

"Batun yara fa? Na san ke zasu bi. Da wuya su zauna a inda nake. Ina nufin ya zanyi in dawo da koda rabin ko kwatan mutumcina a idonsu?"

"Ka tuba. Allah zai yi maka sauran indai dominSa kayi."

Bai san shi dan gata bane kuma asararrarre sai yau. Yau ne ya nutsu ya saurari Khadija. Yau ne kuma igiyar aurensu ta sami targade.

Ya Allah Ka shafe mana kurakuran da suka gabata. Ka hanemu aikata wasu. Amin







47

Iyalin Innayo sun tashi da alhinin aikin da aka yiwa Abbas. Kowa yana farinciki da jin cewa anyi aikin cikin nasara. To amma duk wanda ya ganshi bayan ya farfado a daren jiya cikin magagin ciwo sai ya tausaya masa. Hasiya tayi kuka tamkar ranta zai fita. Kiran sunayensu yake yana rokonsu da su cire masa ciwon da yake ji. Duka sai gwiwoyinsu suka yi sanyi.

Da wuri 'yan dakin Innayo suka gama shiri zasu tafi dubiya washegari. Hasiya ma man ta taho da sassafe saboda bata yarda ta bar asibitin ba. Da tursasawar Honourable ta taho gida yin wanka tunda nan din yafi kusa da asibitin akan gidansu. Uwani ta riga kowa gamawa. Ta sami wuri ta zauna ta kira Munzali. Muryarsa ta dakushe ba ma a jinsa sosai.

"Kira nayi inji jikin Qibdiyya da naka. Jiya ban wuni cikin kwanciyar hankali ba. Kuma Innayo ta ce akwai sirrin da bai dace mu ji ba ko don mutunta juna shi yasa bamu zo ba".

" 'Baram'barama" cewar Zara dake zaune a dakin tana shayar da diyarta "Hasiya taho ga Metron Uwani tana sakin baki"

"Da yake Hasiyan uwata ce ko? Wai me yasa ku ka raina ni ne?" Uwani ta hau ta da masifa ita kuwa sai dariya.

Tun bayan faruwar lamarin nan sai yau Munzali ya yi dariya. Dariya harda kyakyatawa. Da furucin Uwanin da abin da Zara ta ce duka ya ji. Ya kuma kara kaunar Innayo domin hakika ta karramasu da ta basu damar adana sirrinsu ga mahaifansu kadai. Sai da ya gama dariyar ya ce

"Jiki da sauki. In sha Allahu zan kawota wurinku yau ki dubata sai ki fada min abin da ya dace mu yi."

"Kai ni fa anyi suspending dina. Ranar da muka kai ka ma sai da na barar da girmana wurin roko.Ka kaita na kudi kawai a dubata a sirrance. Irin asibitinmu ai da baki ma za a dinga nuna ni idan na koma aiki. Dama kuma can ba kaunata suke yi ba balle an sami abin gorantawa."

Wata dariyar ya yi sannan ya tambayeta Innayo. A bakinta yaji batun aikin da aka yiwa Abbas. Shi ne ma ta bashi shawarar ko asibitin zai kai Qibdiyya tunda na kudi ne kuma ta yaba da likitocin. Da alkawarin zuwan nasu suka rabu. Ko tashi bata yi ba daga wurin Zara tana ta yi mata tsiya suka ji sallamar 'ya'yan Zaran.

Wayyo dadi! Zara ta kusa sakin jinjirarta saboda tsananin farinciki da taji Salima tana cewa "marhabin da su Maryam, maza ku shiga ciki ki ga kanwarku"

'Yan matan Zara su hudu suka shigo falon Innayo suna ta rab'e-rab'e a jikin bango. Yanayinsu ya nuna sam basu so shigowa ba. Duk da haka Salima ta cije ta dinga cewa

"Ku shiga mana"

Taku daya biyu a daddafe suka sake jan burki. Zara ta taso ta tsaya a gabansu da farincikinta. A zatonta wallahi suna ganinta zasu rufeta don murna. Sai taga sun sake jan tunga an rasa mai fara zuwa jikinta. Wani irin kallo ma suke yi mata mai kama da kyama. Kwala taji ta taho mata ta kuma kasa tareta. Innayo ta kawar da kanta gefe kawai don 'yarta ba karamin tausayi ta bata ba. Sai ta tuna mata da lokutan da ita Zaran take yi mata haka.

Cikin bacin rai Uwani ta daka musu tsawa bayan ta gama karantarsu da kanwarta. A ranta ta kissima irin bakincikin da zata ji idan nata 'ya'yan suka gwada yi mata haka. Ta sake jinjinawa hakurin Innayo.

"Kun wuce jikin uwarku taji duminku kun ji nata ko sai na taso muku?"

Jiki na rawa kuwa suka tafi wurinta amma a bayanta suka labe saboda tsawar Uwani ba don farincikin d'a ya ga mahaifiyarsa ba.

Karamar da yake babu hankali sai cewa tayi "hummm, Mummy ba kya wanka ko?"

Mai bi mata kuma ta ce "ba Aunty ta fada mana a gidansu Mummy ba..."

Mas'uda ce babbar, ta sa hannu ta buge bakin kanwarta tana mai cewa "ba ta ce kada mu fada ba?"

Ta dubi mamanta ta tabe baki "tare da Daddy muke. Ya ce ki zo." Ta kuma ce da kannenta "ku zo mu koma mota"

Salima ta hadiye nata fushin ta ce "ku zo ga kanwarku ku ganta. Sai mu ga da wa take kama"

Maryam har ta fara murna ta soma takawa wurinta sai ta fasa.

"Karaso mana"

"Aunty ta ce kada mu taba komai a gid..."

Mas'uda ta janyo hannunta tana gargadinta "ba ta hanaki surutu ba? Ni ku zo mu tafi kafin mu fara warin talauci"

"Ke???" Uwani ta yi musu tsawa a karo na biyu.

Zara sai kuka. Jikinta har rawa yake. Ta ruga gaban Innayo ta durkusa akan gwiwoyinta.

"Wane mutum Innayo? Waye zai buga kirji ya ce ya zama sanadin hawayen iyayensa kuma ya gama da duniya lafiya? Ki yafe min. Ki yafe daga kasan zuciyarki don girma da isa da tsarkin Mulkin Allah. Nayi miki rantsuwa idan yaran nan suka gwada min abin da nayi miki na sati guda zuciyata za ta buga. Kaicona. Ba zan iya addu'ar cewa Allah Yasa yarana su ji kaina kamar yadda nayi miki ba"

Hawaye Innayo take ita ma. Ta rike hannuwan Zara ta ce "na yafe muku ke da 'yan uwanki tun kafin ku roka. Babu komai a zuciyata game daku sai fatan alkhairi da albarkar rayuwar duniya da ta lahira."

Da hannu ta yafito 'ya'yan tasa suka zauna a gefen mahaifiyarsu. Da har sun fara matsawa don kada jikinsu ya gogi nata Uwani ta watsa musu kallon ku shiga hankalinku. Ana haka Hasiya ta fito daga bandaki daga ita sai daurin kirji. Fiye da rabin jikinta duk kumfa. Bala'i ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login