Showing 147001 words to 150000 words out of 242549 words
suka yi masa. Comared ya gyara zama yana shafar gemunsa.
"Wannan Malamin da na kira shi ya dorani a harkar nan. Naki fada maka ne kawai saboda naga kamar kana kyamar abin. Magana ta gaskiya wani aiki aka yi min shi ne yace na nemi namiji. Washegari aikin ya ci to amma abin ya zarce...." Ya kare da shu'umar dariya.
Alh. Tahir ya kada kai "kace ya hadani da mata goma ni dai akan namiji guda."
Wata dariyar Comared ya yi domin aikinsa kenan. Dariya kamar dan akuya.
"Ai kuwa ka makaro domin kuwa namiji ya ce ka nema ranar laraba kafin rana tayi zawali. Indai kayi yadda ya ce da kanka za ka nemeni. Zai aiko da magani da zaka hada kafin kayi abin."
Hula Alh. Tahir ya cire ya shafi sumar kansa wadda ta fara samun bakin furfura. Ko kadan baya son auren Yumna musamman saboda abin da ta nunawa Farha. A bangare daya kuma ko yana shan giyar wake ba zai so tsinuwar Yakumbo ba. Sau daya dai don ya nemi namiji ba zai rage shi da komai ba. Yana tunanin abin yaji tsigar jikinsa ta mike har amai na neman taso masa. Wayarsa ya dauka ya tashi yana yi musu sallama.
Comared ya dakatar dashi daga tafiya "bari nasa ayi maka booking wanda ya san me yake yi tunda kai sabon shiga ne" waya ya dauka ya sake kira sai ga mai kuftar da ya shige dakinsa ya fito.
Zubewa ya yi kamar mai rokon gafara a gabansa "Yallabai kana da wata bukatar ne?"
Kofar dakinsa ya kalla ya hadiyi yawu "yaron da ka kawo daga gani ya yi kawai. Kwararre a harkar nan nake so kayi min booking ranar laraba mai zuwa. Ina son irin wanda idan sabon kamu ya samu gobe da kansa zai koma. Daga aljihuna kadai zan baka dubu dari biyar. Shi kuma uban gayyar ba mai rowa bane. Ka sa rai da farin gani."
Shazali ya saki murmushi har hakoransa suka fito. Ya san inda zai samo musu kalar wadanda suke so. Shi da yake da shaidar da zata tarwatsa musu rayuwa, dolensu su zo ko sun ki ko sun so.
I just published "30" of my story "UWA UWACE...". https://www.wattpad.com/1069890589?utm_source=android&utm_medium=com.whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=BatulMamman17&wp_originator=YYjueliRY%2Fur%2FdO5hYF6vB8QgjdvACtjcuW8JNTTky0CZQly4P%2B0Nqj0vZ7rPuLcyWAm9XBuv2o4lHOPXPp57ixksHVniR4WoKc4ZZoxJWeL3q9OW0OjNxfh6EOncFdV
UWA UWACE...30
Batul Mamman💖
Innayo da 'ya'yanta sun karrama su Mami Khadija fiye da zaton Munzali. Shi ya kawo duk wani abin ci da sha to amma bai kai rabi rabin kyautatawar su Salima garesu ba. Farha tana ganin jaririyar Zara ta karbeta. Mardiyya da Sauda suka karaci nacinsu suka hakura. Uwani har lokacin tana daki ko lekowa a gaisa bata yi ba. Duniyar ce take ta hajijiya da ita. Bata da lokacin kanta balle na wani.
Lokacin da suka shigo Murja tana ta sauri sauri ta kai karshen kitso biyun da ya rage musu, saboda haka kan Zara a bude yake. Suna sallama ana gamawa. To bayan sun zauna an gama gaisawa Sauda ta dinga taba Mami Khadija har sai da Innayo ta kula da hararar da Mamin take yi mata. Da hannu ta kira Saudan fuskarta dauke da murmushi. Bakin da gani sun baiwa kalmar 'babu' hutun shekara da shekaru ma. Amma babu alamun wulakanci ko girman kai. Mama Nasima ce ma dai ta hadiye rashin gamsuwarta ta hanyar kama bakinta tana jiran tabbatacen bayani game da gidan da matar dakin.
"Zo ki fada min me kike so ake hanaki kamar ba dakin mamanki ba."
Mami Khadija tayi saurin cewa "don Allah kar ki biye mata."
"Sai dai a tari gaba."
Yadda Innayo tayi maganar sai ya basu dariya. Sauda na tsoron batawa Mami Khadija wadda bata daina hararta ba, sannan tana kunyar badawa Innayo kasa a ido.
Su biyun duka idanunsu na kanta. Ta kalli wannan ta kalli waccan ta dukar da kai. Farha da Mardiyya da ma su Zara da Ayaah wadda 'yan matan suka burgeta ana ta dariya. Mama Nasima kuwa cin magani take rai a bace sai ga Munzali ya shigo. Sauda ta hau murmushi da ajiyar zuciya.
"Yauwa don Allah taimakeni."
"Da me?" Ya amsa yana dube duben fuskokin mutanen dakin.
Mami da Innayo ma sai da suka yi dariya wannan karon. Salima ce ta labarta masa me yake faruwa.
"Saboda haka ka taimaketa idan ba haka ba daya daga cikinsu zata hukunta ta."
Halin rashin nutsuwar da yake ciki bai hana shi biye musu ya yi murmushi ba.
"Nima dai babu ruwana. Kawai ki kwato kanki don duka ina tsoron fushinsu."
"To ke kinji, kin kama kafar wala" cewar Mami Khadija da murmushi.
Sauda ta turo baki ta soma cewa "Ai don dai ba Mar....."
Kafin ta gama shi da Mardiyya sun kama kansu domin cikin sauri suka dinga cewa ta fadi abin da take so. Nan da nan dakin ya sake kaurewa da dariya. Sai da suka nutsu ne ta fada musu kitson da ta gani ne ya burgeta.
Ayaah ta mike da sauri tana cewa "bari na kirawo miki wadda tayi."
Sauda ta kalli Mami ita kuma ta ce ba za su jira ayi mata kitso ba.
Munzali na jin haka ya ce "Mami ba a waje za a nemo mai kitson ba. 'Yata ce ita ma. Bari su zo na gabatar muku dasu" ya kare maganar da murmushi.
Zara da Salima harda Innayo ne suka hadu suna rokar alfarmar Mami ta bari ayi kitson. Murmushi kawai tayi domin nauyinsu ne ya kamata ta kasa kafewa akan bakanta. Halayyarsu ta burgeta matuka don daga uwar har 'ya'yanta sun iya saka bako yaji kamar a gida yake. Shi yasa ta ce ba hanawa tayi ba sai dai da kunya zuwan farko su zauna ayi kitso.
"Duk gida ne Hajiya kuma na fahimceki sosai. Amma don Allah ki bari ko manya tayi mata. Ki ajiye dalilin zuwanku ki dauka mu daku daya ne."
Mami Khadija ba yadda ta iya da furucin Innayo wanda tayi cikin sigar rarrashi da sanin ya kamata. A dole ta ce ta hakura amma fa manyan za ayi kuma tun wuri Innayo ta sani cewa idan sun je gida sai ta yiwa Sauda fada.
"Ba zan hana wannan ba. Amma dai kar kiyi da yawa. Na tabbata jin da tayi kamar tana tare da 'yan uwanta ne yasa bata boye abin da take so ba. In wani gidan ne ita ma ba za ta soma ba ko Saudatu?".
Sauda ta gyada kai tana kallon kasa. Farha ta tashi ta ce bari ta fadawa Suhaib. Saudan sai ta bita aka bar Mardiyya da ta karbi baby din Zara da Munzali tare da sauran mutanen falon.
Mardiyya kunyar kasancewar Munzali a wurin ta hanata sakat. Sau biyu suna hada ido. Murmushi yake mata wanda a kasan ransa yake jin zai iya zama na bankwana. Tunda Shazali ya kunno musu wuta yanzu basu san iya inda zata tsaya ba. Don kada kowa ya fahimci kallon me suke yiwa juna sai ta dubi Zara ta tambayeta sunan baby.
Kafin Zara ta san me za ta ce mata Mami Khadija ta sako tambayar waye babba tsakanin Munzali dasu Salima. Ba kuma haka kawai tayi ba sai don ta kawar da hankulansu daga tsakin da Mama Nasima take yi jifa jifa. Sautin na yanzu yafi karfi shi ne tayi tambayar da dan karfi ita ma. Har kasan ranta bata da niyar idan sun zo ta zake da yawa tunda ta san halin abokiyar zaman nata. Kar ta ce surukanta ne Mamin take shige musu. Kyawun mu'amalar 'yan uwan Munzalin ya bata sha'awa amma ta kula ba haka bane a wurin mai shirin zama surukarsu. Yatsine yatsine take ta yi da tsaki na gajiya da kosawa daga zamansu. Dalilinta kenan na jan maganar kitson da Sauda ta nuna mata kawai don kada su kunyata kansu.
Munzali ya nuna mata Salima ya ce ta girme shi amma Zara kanwar bayansa ce. Ai fa nan suka soma musu da Zara akan waye babba har ya hakura ya karbi kankantarsa.
*
Da Ayaah ta fito kiran Murja samunta tayi tana waya. Gira ta dage tana yi mata dariyar shakiyanci saboda gane wanda ake wayar dashi. Mahiru ne saurayin da ya kai kudin aurenta.
"Haba nifa naji shiru daga kaiwa baki abin sha baki dawo ba ashe ashe..."
Sallama Murja tayi da Mahiru tayi dariya "gulmammiya indai ba labe ki ka yi min ba me ki ka ji na ce da zaki gane da wa nake waya?"
Ayaah ta rausayar da kai hannunta daya akan kugu ta ce "gani nayi kina ta bin bango kina malalewa kamar ruwa irin abin nan na Indiyawa a lambun soyayya. Na ce duk yadda aka yi Yaya Mahiru ya fadi abin da ya susuta Murjanatu 'yar Baba."
Haushi ya kama Murja da Ayaah ta kwatanta irin tsayuwarta a jikin bangon harda waka.
Iska ce ta debi maganganunsu har falon Asabe saboda sun fi kusa da wurin. Lilu ya kama dariya harda rike ciki. Suhaib ya kai masa duka yana nuna masa alamar ya yi shiru da dan yatsa. Shi ma hirar nishadi ta sanya shi har yaji yana son ganin fuskar mai tsokanar.
"Kai fa baka da kan gado wallahi."
A lokacin wakar da Ayaah take yi ta shiga kunnuwansa sai da ya murmusa. Gyara zama ya yi yana saurarensu tare da kallon Qibdiyya da Lilu yana biye mata kamar yaro dan uwanta. Waka take abinta babu kyakkyawan kari. Duk baitin da yazo kanta take fada.
"Sai ruwa ruwa na malaleeeee. Ashe ruwan bana ya ci su Murjaaaa. Kinsan ya dade yana sonki ruwa na ...."
"Zan malale bakinki a wurin nan" cewar Murja a fusace tana galla mata harara sai kuma ta kama dariya "murya kamar gogen tsumma."
Ayaah ta sha kunu tsiwar ta motsa ta ce "kin dai fada ne kawai don kiji dadi amma ke kin san muryata da dadi. Idan ina magana Dani kasa dauke ido yake daga kaina."
"Waye kuma Dani kamar wani arne?"
Furucin Murja kenan domin yau ta fara jin sunansa. Ran Ayaah in yayi dubu kuwa a take ya baci. Maganar tayi mata zafi don sai da taji kwalla na neman kwace mata. Dani din nata ake kamantawa da arne.
A bangaren su Suhaib ma sai suka hada ido da jin kalmar Murja ta karshe da shirun Ayaah. Ba tantama ya da kanwa ne. Sai da Farha ta fito tana tambayarsu inda su Lilu suke sannan Ayaah ta fadawa Murja sakon da ya kawota.
Rashin sanin da mutane a kurkusa dasu ya sake bawa Ayaah haushi da Murja ta nuna falon Asabe. Da suka fito bayan gama jin bayanin Farha suka fito Ayaah ta basu baya tayi hanyar kofar gida da waya a kunne. Danliti ne ya iso yana neman karin kwatance. Basu ga fuskarta ba har suka karasa ciki wurinsu Innayo.
***
Mami Khadija bata son barin 'yan matan dasu Lilu kadai a gidan. Sannan take taken Mama Nasima tun farkon zuwansu ya nuna mata zasu iya samun matsala akan jiran kitso. Cije lebe tayi ta rasa me zata ce da Innayo ba tare da ta bata mata rai ba.
To ita ma Innayo din duk ta karanci rudanin da Mami Khadijan ta shiga. Ita kadai a zuciyarta ta yabawa wannan uwa. Tunanin maslaha ta tayata inda bayan dan nazari na kankanin lokaci ta bude baki tayi musu magana.
"Munzali ko zaka bisu da Murja sai Ayaah ta rakata. Kitson mutum daya dai na san kafin Magariba in Allah Ya so sun gama. Ko kuwa? Kunga sai a sami zumunci sosai tsakaninsu ko?"
Kai Mami Khadija ta daga ta kalleta da murmushi sannan tayi mata godiya sosai.
"Haka ne. Nima ba zaman kitson ne bana so ba amma kinga ..." tana son cewa su matsayin dangin mata suke kuma gashi ko iyaye maza basu gana ba. Ita da tun farko bata goyi bayan zuwan ba kuma harda Mardiyya bai kamata ta assasa dadewarsu ba.
"Karki damu duk na fahimta. Bari ta kirawo kanwarta sai su biku tare."
A lokacin Lilu ya bukaci Suhaib ya bashi mukullin mota yana da chakulet zai daukowa Qibdiyya. Nan ta soma tsalle. Munzali ya ce shan zakinta ya yi yawa kada ya dauko. Da ido Lilu ya yiwa Suhaib alamar ya taimaka ya dauko masa. Shi kuma sai ya sami kansa da biye masa yabi bayan Murja da ta fito kiran Ayaah.
***
Turare Danliti ya sake mitsikawa a hannunsa yabi jikinsa ya shafe sannan ya sako kai soron da Ayaah ta shiga bayan ta hango shi. Tuni ya ce mata a bakin titi ya ajiye mota saboda ya zata layin nasu mota bata shiga. Ita ma a ciki hijabinta ta gyarawa zama tasa hannu ta dan goge fuska. Idanun iyayenta da bakin dakin Innayo ne suka hanata sabunta kwalliya domin tarbarsa.
A tare suka sakarwa juna murmushi da ya shigo. Idanunsu sarke da juna kunya duk ta kamata.
"Baby kin yi min kyau sosai."
Kalman da Suhaib yaji kenan da ya tunkaro kofar. Can ya baro Murja tayi cikin gida tana ta kwala kiran Ayaah. Bai san wace ce ba amma zuciyarsa ta bashi abokiyar fadanta ta dazu ce wadda aka ce zasu tafi tare.
Fari tayi masa da ido sannan tayi godiya.
"Na gode Dani."
'Dani?' Suhaib ya ambaci sunan a ransa yana mai tuna abin da ya hada 'yan uwan rigima. Curiosity bai barshi ya cigaba da tsayuwa inda ya dakata ba. Yanke shawarar wucesu don yaga fuskokinsu su biyun ya yi. Murmushi ya bayyana akan fuskarsa da ya ayyana me Lilu zai yi da shi ne ya fito. Ya daga kafa zai cike tazarar dake tsakaninsa da kofar soron sai yaji abin da bai zata ba. Muryar mai suna Dani ce take fita a raunane cike da makirci irin wanda ba kowa zai gane ba.
"Baby yau ma ina cikin damuwa. Shi yasa ma kika ga na matsa sai mun hadu." Bai kuma jira jin cewarta ba don ya kula ta fara yi masa kallon tausayin nan ya dora da "wai ko kinsan yanzu matar nan ta daina zuwa shimfidata sai na biya?"
A saukar aradu maganar ta shiga kunnuwan Ayaah da Suhaib. Ita nauyi da kunya ne suka kama ta gami da fara jin haushin me yasa hirarsa bata wuce irin wadannan maganganun. Suhaib kuwa zuciyarsa yaji ta soma tafarfasa. Ya yiwa zina da duk wani ma'abocinta mummunar tsana. Salon hirar nan kuwa ba komai bane illa dauko hanyar bude kofar da za a iya fadawa gareta. Yarinyar da yaji muryarta kila ba za ta wuce sa'arsu Sauda ba ita ake fadawa wadannan kalamai. Jikinsa har yana tsuma don bacin rai ya iso daidai bakin kofar amma sun juya masa baya sannan yaji amsarta.
Muryarta har raurawa take yi saboda an kure rashin kunyarta ta ce "Dani ina ga ba ni ya kamata ka fadawa wannan matsalar ba. Gara dai ka kaiwa magabatanku a nemi mafita."
Danliti ya gane ta fara jin tsoro daga muryarta ya yi murmushin gefen baki. Da tsoron wanda bai hana cigaba da soyayya ake samun kan irinta. Sake kwantar da murya ya yi abinsa harda langabe kai.
"Wa zan fadawa matsalata bayan Mum idan ba ke ba? Ita kuma saboda bata kasar bana son yawan tayar mata da hankali. Kece dai wadda nake shirin aura nake ganin ya dace ki san matsalolina tun yanzu domin ki tanadi hanyoyin magancesu."
Maganar tasa tana fita ne daidai da takunsa da yake ta kusanto shi gareta. Idanun Ayaah sun yi wuri wuri amma ta rasa me ya hanata ja da baya. Tausayinsa take ji har kokon ranta tana kuma gudun kar ya nemi wata idan taki taimaka masa. Bata yi aune ba ta ji shi daf da ita har tana jin dumin numfashinsa.
"Baby ko dan huk (hug) ne don Allah in samu domin na rage zafi. Ina tsananin bukatar mace. Jiya na tura mata dubu dari ta ce ya mata kadan. Ni kuma shi ne naji haushi ban sake yi mata magana ba. Kudin bai dame ni ba amma na gaji da rainin wayo."
Sai ga Suhaib yana tafa hannuwa kamar mace saboda tsabar mamakin da ya sarke shi. Bai taba ganin dan is... kamar wannan mai sunan arnan ba. Duk da haka ya tsaya yana son ganin irin tarbar da Ayaah zata yiwa yunkurinsa domin ya san matsayin da zai ajiyeta. Duk abin da ake yi ko fuskarta bai gani ba har yanzu.
Akan idonsa ta ja baya kadan tayi magana kamar mai shirin kuka.
"Ka kara hakuri. Ba ka ce idan Mum din ta dawo za a turo ba? Ka bari ayi auren."
Hannu ya daga yana son shafa fuskarta ta goce da sauri. So yake su wuce wannan matakin ya sami yadda yake so. Yawancin mata wuyarta a sami kansu na farko. Daga basu da zabin da ya wuce amincewa a gaba saboda gudun kada a ki aurensu. Ya dade da yadda da wannan shi yasa yake cin karensa babu babbaka.
Cikin muryar dake nuni da tsantsar karaya da neman agaji ya ce
"Har sai wannan lokacin Ayaah? Idan na shiga wani hali kafin nan ba laifinta bane ita kadai har dake. Naki ma yafi nata domin zuciyata da gangar jiki duka ke suke so. Nayi zaton zuwa yanzu nafi karfin komai a wurinki. Ashe ni kadai nake haukana. Yadda na daukeki daban da matsayin da kika bani."
"Ba haka bane. Kai ma ka san ina sonka."
"To ki nuna min a aikace. Ki mantar dani bakincikin da matata take kunsa min. Ki cire tsoro a ranki domin wallahi ko raina ki ka nema zan iya baki. Sannan kada ki manta dama ya halatta na ganki tunda maganar aure ce tsakaninmu. Gani babu hijabi balle mayafi. Hakkina ne kike neman dannewa Baby. Kin yi min adalci kenan?"
Runtse idanu Ayaah tayi da ya sake daga hannu zai shafa fuskarta. Bata so ko kadan amma zuciyarta ta gama aminta da halatta haramun din da yake neman yi. Ba zina zata yi ba. Nutsuwar da yake nema kawai take son taimaka masa ya samu.
Suhaib bai san lokacin da ya iso gabansu ba. Danliti da ya gama sakawa ransa cewa daga shafa fuskar zai zarce da koya mata wani karatun daban sai ji ya yi hannunsa ya makale a iska. Daga kai ya yi yana kallon gefen fuskar mutumin da ya rike shi a firgice.
Ayaah kuwa da taji shiru bai taba ta ba sai ta bude idanunta a hankali. Nan suka yi ido hudu da mutumin da bata sani ba. Kwayar idonsa tamkar maganadisu aka zuba saboda yadda ta kasa dauke nata. Mugun kallo yake yi mata mai kama da na tsana. Zuciyarta sai da tayi wani irin tsalle don tsoratar da tayi. Suhaib ya kuma ware mata