Showing 105001 words to 108000 words out of 242549 words
ba in Allah Ya so."
Babu sallama ta fice abinta. Mahaifiyar Salihi bata tsaya nemansa ba tunda ta san lokacin da ya ranta da dalilin da ya hanashi biya. Ranta dai ya baci sosai. Sarkar zinarenta ta karshe da maigidanta ya bata kafin rasuwarsa ta dauko daga ma'ajiyarta. Kai tsaye gidan Dillaliyar unguwarsu ta nufa. Haka ta bata sarkar jingina ta karbo bashin dubu dari uku. Da Salihi ya zo da yamma ta kulle a leda ta bashi.
"Idan Allah Ya hore maka da wuri ka kawo kudin na maidawa Dillaliya."
Sunkuyar da kai ya yi cike da kunya da takaicin Uwani. Karshe ma yaji kamar zai zubar da kwalla. A tausashe mahaifiyarsa ta ce,
"Kada ka bari zancen nan ya tsaya maka rai. Maganar guda ce. Ba zan saka ka saki matarka ba amma indai ka haifu za ka kara aure. Ka nemo 'yar masu mutumci ka aura (haka kawai 'ya'ya su dinga janyowa ana aibata dattakon iyayensu)."
Ya nuna mata ya haifu kuwa. A cikin wata guda ya hada kudin nan ya kai aka karbo mata sarkarta. Tayi ta saka masa albarka kuwa. Bayan wata uku ya ce su tura kauyen 'Yar gaya ya sami mata.
Ita da 'yan uwansa basu kyamaci 'yar kauyen da ya kawo ba. Yarinya ce mai saurin shiga rai da faram faram da jama'a.
Matsalar farko da suka fuskanta shi ne rashin samun kwarin gwiwar fadawa Uwani zai yi aure har aka yi. Tsoron tashin hankalin da za ta yi masa yake ji. Sai gashi ya buge da rokom Ummule tayi hakuri har ya sami damar fada. Gida ya kama mata a wata sabuwar unguwa. Daga office yake biyawa amma bai taba kwana ba. Haka take ta hakuri.
Aurensu na da wata biyu barayi suka haura mata cikin dare. Tsananin firgita da tayi yasa ta suma. Sun kwashe kayan kallo da kudi amma basu tabata ba. Koda ya iso gidan bayan anyi masa waya daga makota tana da zubar jini. Ashe ciki gareta basu sani ba har ya zube. Musabbabin rigimarsu ta yanzu kenan. Ta roki ya raba musu kwana a kalla barayin da aka san 'yan unguwa ne zasu ga namiji na kwana. Idan ba zai iya ba kuma za ta koma gidansu. Da kyar ya lallabata da alkawarin zai fadawa Uwani yau ya tafi.
Yana fita Ummule ta zari mayafi tabi bayansa a adaidaita sahu. Ba za ta yarda ta zauna tana cutuwa ba. 'Yancinsu ita da dan cikinta take neman karewa.
*
Samari ne su hudu cikin wani tafkeken daki wanda ya wadata da kayan alatu. Daki ne wanda uku daga cikinsu suke haya a ciki a matsayinsu na daliban jami'ar Bayero. Uku a cikinsi babu wanda zai kai shekara ashirin da biyar. Tun daga suturarsu da ta juyawa mutumci baya har zuwa wayoyin hannuwansu za ka san 'ya'yan masu hannu da shuni ne. Kawunansu babu kyawun gani kuma wai nan duk a cikin gayu ne. Cikon na hudun nasu dan saurayi ne wanda da alama sun girme shi. Shi riga da wando na yadi ne a jikinsa. Ko kadan babu alamun shashanci tare dashi sai damuwa shimfide a fuskarsa. Daya daga cikin samarin ne ya tsaya a gabansa yana magana yana jejjefa hannuwa kamar mai rapping. Wandonsa ya kusa gwiwa sai na cikin da ya bayyana cikin wani salon wulakanta kai mai suna ass-down.
"Oh boy ya ka ke mana yawa ne? Nifa gaskiya bana son eh-yane, ai ka gane. Kawai idan maiko ba zai samu ba ka ware. Clique (kungiyar abokai) dinmu ba na yawa-boys bane."
Tashin hankali ne ya kara bayyana a fuskar yaron da yaji sauran suna cewa ya tafi. Ya matsantawa kansa son yin abota dasu saboda duk makarantar babu masu tashe irinsu. Kowa ya sansu kuma yana shakkarsu. A gidansu shi da 'yan uwansa tamkar babu wanzuwarsu. Mahaifiyarsu neman kudi tasa a gaba. Babansu bashi da katabus sai tsoronta. Gashi bata nuna musu shiga dangi ba. Basu saba da kowa ba balle su ji dadin mu'amala da makusantansu.
Yara kala kala ne. Akwai masu son ayi feeling presence dinsu idan suna waje. Suna son a yaba musu ko ayi musu fada. Su dai ka nuna ka san dasu kuma suna da mahimmanci a wurinka. Idan suka kasa samu a gida sai su fita. Irin haka ce ta faru da Mubasshir Salihi. Rayuwar gidansu babu dadi. Daga karatu sai karatu. Tun suna yara idan suka fara wasa Uwani ke hanawa tayi ta fada har suka daina yi da junansu. Yanzu shiga dari fita dari sai dai ka samesu kowanne rike da waya kamar ibada.
"Nawa zan kawo to?" Ya tambayi mai yi masa magana.
"Contribution ne kawai na daidai kudin gidansu mutum.." sauran suka kwashe da dariya "kada dai ka kawo kasa da 50k domin zamu tafi da babes. Ka san mata da son ayi musu barin kudi."
"Shike nan, zan kawo."
Fita ya yi da rawar jiki kada a fasa zuwa yawan bude idon da suka shirya zuwa Tiga dam dashi. Yana fita suka kwashe da dariya suna tafawa. Mubasshir ba ajinsu bane. Za dai su tatse shi da kyau su yar ne kawai.
Babur dinsa ya hau wanda da kyar da sudin goshi Uwani ta saya masa. Shi ne danta na fari. Yana level one.
Ya san yau aikin kwana gareta. Kannensa mata duka ukun suna makarantar kwana. Da mukullinsa ya bude gidan. Kofar dakinta a kulle da mukulli. Guntun tsaki ya yi ya dauko spare wanda abokan nasa suka sa ya yanka. Ashe ga ranarsu nan. Hankalinsa a kwance ya dinga sauke mata akwatuna yana bincike saboda bai sa ran dawowarta yau ba. Babansu ma kwanakin nan idan tana da aikin dare baya dawowa da wuri. Wani envelop ya samu a can kasan wardrobe dinta ya dauko ya zazzage akan gado. Bai san ko nawa bane don yawan bandiran da ya gani. Ga kuma kananun box din sarkar gwal guda uku. Dariyar shakiyanci ya yi da ya kwatanta bawa duk yarinyar da za a hada shi da ita a Tiga da ita matsayin kyauta. Ya san sai ya doke ragowar abokan nasu wurin samun fada da kulawa.
Mubasshir yana dakin Uwani yana barna ta iso gida. Tana gyara parking Salihi ya iso. Jira yake ta gyara motar shi ma ya ajiye tasa sai ga adaidaita sahu ya tsaya a jikin katangarsu. Ummule ce ta fito ta nufi motarsa tana cewa ya bata dari uku ta biya mai adaidaita sahu.
Uwani da ta dawo gida da bakincikin abin da ya faru a gidan Innayo sai ta tsaya tana kallon ikon Allah. Yarinyar da ta fito daga adaidaita sahu murmushi take yi. Salihi kuwa a firgice yake!
UWA UWACE...21
Batul Mamman💖
Assalam alaikum wa rahmatullah wa barakatuhu.
Da farko ina godiya gareku masu kira da turo sako ta sms da whatsapp, wattpad da facebook. Nagode da shiruna bai sa kun manta dani ba. Allah Ya sakawa kowa da alkhairi. Na so sai na kammala labarin nan gabadaya zan sake post amma yawan tambaya da kuma rashin sanin me ya boyeni yasa ni fito da iya abin da ya samu. Duk da haka ina mai baku hakuri domin daga wadannan shafukan zamu sake wani zangon kafin cigaba. Addu'arku nake roko don Allah. Akwai abu da ya tunkaroni, ina rokon Allah sa'a da salama a cikinsa. Allah Yasa a dace. Allah Ya biyawa kowa bukatunsu na alkhairi. Ina muku SonSo.
***
A zuciye Uwani ta isa gabansu tana muzurai. Kafadar Ummule ta riko ta yadda dole sai da tasa ta juyo suka fuskanci juna. Bata cire hannun ba ta nunata da dayan.
"Ke bariki ma fa iyawa ce. Naga kuma kamar baki iya ba tunda kin yi shuka a idon makwarwa. Idan sadaka ko taimako ki ke nema me ya hanaki tambayata ina mace 'yar uwarki? Ai mu biyu ne a wurin. Don tsabar is.. sai ki bi namiji?"
Dama Ummule tana fita daga adaidaita sahun ta gane Uwani. Akwai hotunanta a wayar Salihi. Kafadarta ta gotar hannun Uwani ya koma lilo.
"Akan me zan nemi taimakonki bayan ga mijina..."
Uwani ta kan ji ana cewa kunne ya toshe na 'yan dakiku sakamakon jin zance mara dadi. Ashe gaske ne. Daina ji ko gane komai tayi na wani lokaci sai kalmar miji dake neman mazauni a cikin kwanyarta.
Karfin hali Salihi ya yi ya ce "Uwani. Ummule. Ku shiga ciki muyi magana bai dace ana jin muryoyinku a waje ba."
A haukace Uwani ta isa bakin karamin gate din nasu wanda mota bata shiga, shi yasa suke ajiye motocinsu a waje. Tare shi tayi da hannuwanta biyu ta soma masifa ido rufe.
"In ta shiga Allah Ya ..."
"Kar ki karasa tsinuwar nan. Gida dai nawa ne kuma ku duka matana ne" cewar Salihi yayinda ya matso zai cire hannuwan da tasa ta tare hanya. Duhu ya mamaye unguwar sai hasken kwayayen fitilu. Su ukun duka babu wanda ya yi sallar magariba saboda ta riskesu a titi. Ga isha an soma kira. Baya son makotansu masu zuwa masallaci wani ya ga abin da yake faruwa a kofar gidansa.
Kallon baka da hankali Uwani tayi masa kafin ta iya hada labbanta ta ce,
"Su waye matan naka? Aure kayi da gaske ban sani ba?"
"Na ce miki mu shiga ciki ko" ya ce yana dan daga murya.
Mubasshir na cikin tura kudi a aljihunsa yaji muryoyin iyayensa kamar suna fada. Da sauri sauri ya tattara komai ya mayar inda yake. Aljihunsa kam bandiran dubu dai-dai guda uku ya tura. Ga sarkar da ya dauka daya. Ya kuma rufe mata daki kamar ba a shiga ba ya fito.
"Wallahi kayi kadan Salihi. Amanata ka ci? To ka je ka tambayi malamai wannan auren bai dauro ba tunda ban sani ba balle na amince."
"Ki ce kawai idan ki ka tsine masa za ta kama shi." Cewar Ummule, haushin lallabawar da Salihi yake mata a wannan yanayin da suke cik na kara kamata.
"Kar ki yi min rashin kunya! Bani da kyau wallahi" Uwani ta ce a harzuke kamar za ta kai mata duka.
Akan ce idan babba ya yada girmansa sai yaro ya taka ya hau. Ummule ba mai takalar rigima bace amma bata ga dalilin ragawa haukan da Uwani take musu ba.
"Daidai nake dake. Gidan mijina ne saboda haka a matsa min na shiga."
"Wanda ya auroki ma bai isa ya shiga ba."
Shi dai hankalinsa ya gama tashi saboda bai iya hayaniya ba. Da kyar ya cire hannunta ya janyeta suka shigo tare da Ummule. Ita haushi da tausayi ya bata. Yadda yake bin Uwanin a hankali har ta soma tara musu mutane ya kular da ita. Banda tana gudun bacin ransa da tuni ta hankadeta kowa ya huta.
Suna shiga suka ci karo da Mubasshir wanda rashin gaskiya ya fito a fuskarsa baro baro. Amma da yake suna tare da damuwa su duka babu wanda ya kula. Muryar Uwani a sama tana ta zazzaga masifa ba ji ba gani.
"Kaga Salihi ka sallami yarinyar nan kafin na illata ta."
"Mu illata juna dai" cewar Ummule tana jijjiga kafa.
"Kaji ko? A gabanka take yi min rashin kunya."
Ihu ne kawai bai yi ba amma kansa ya dauki chaji sosai.
"Uwani ki saurareni kiji."
"Anki a saurareka din..."
Mubasahir sai yaji wani iri. Mahaifinsa take yiwa magana haka a gabansa.
"Mama don Allah kiyi shiru..."
Dama a wuya take sai kawai ta janyo shi ta kai masa duka a gefen fuska ko ta huce. Ransa kuwa ya baci . Ta kara yiwa kanta bakin fenti a idonsa.
"Munafukai daga kai har uban naka. Saboda baka damu dani ba ko a jikinka an kawo 'yar shila da sunan kishiyata."
Bata tsaya kallon fuskar dan nata da miji ba bayan ta kira su munafukai ta harari Ummule.
"Idan ma dadiro kuke yi ya miki ciki a waje ake son kawo min cikin gida ne to kunyi karya."
Dama kallo daya ta fahimci Ummule tana da ciki. Sai da ta gaji da masifar don kanta ta
nufi dakinta ta soma dauko akwatuna tana budewa. Saboda gudun bacin rana da cin amana irin ta da namiji take ta tanadi. Gininta a Zawaciki filasta kadai ya rage da fenti. An kawata gidan sosai ya dace da zamani ta kowace fuska. Gida ne dan madaidaici wanda ta kudurta niyar komawa idan bai yi musu gyara a nasu na yanzu ba. To ashe mai gabadaya ya tasarma yi. Ajiyayyun kudadenta za ta dauko ta bayar a gama komai cikin watan da ake ciki. Tana ganin idan ta tashi daga shi har kurar da ta kwaso matarsa za tafi karfinsu.
Akwatin da kudaden suke ta durkusa ta bude kudi suka ce daukarmu inda kika ajiye mu!
***
Bayan tafiyar Uwani da aka idar da sallar Magariba wasu makotansu Innayo suka shigo. Zama na mutumci ne tsakaninsu shi yasa suka shigo tambayar ayyukan da take so su tayata na sunan gobe. Kafin ma ta fada musu babu taro suka fahimci halin da Zara take ciki. Sun tausaya mata sosai kuwa. Da yake Innayo ba mai yawan magana bace bata taba zaman sukar 'ya'yan nata ba. Sai dai wanda ya gani da idonsa ya fahimci irin zaman da suke yi. 'Yar hira suka taba yayinda su Hasiya suka gama kimtsa komai suna shirin tafiya.
Innayo ta fito raka bakinta kenan adaidaita sahun da ya dauko 'yan sakon gidan Salima ya tsaya a kofar gidan. Ihsan da kuka ta fito ta fada jikinta. Gabanta ya yi mummunan faduwa. Dago Ihsan din tayi daga jikinta hankali a tashe.
"Ina Salima? Me ya kawo ki da magaribar nan? Kukan me kike yi?"
Ihsan ta kasa magana sai shesshekar kuka. A tsorace take ko mutuwar gaske mahaifiyarta tayi.
Daya daga cikin 'yan rakiyar ne ya yi mata bayani. Kuka ne ya kwace mata, nan da nan idanunta suka dinga zubar da kwalla. Bata ga ranar hutu akan lamuran 'ya'yanta ba. Kuma tana tsammanin wannan ranar ba za ta taba zuwa ba. Daga ranar da mace ta fara amsa sunan uwa to har abada sunanta kenan. Da damuwar Zara ta wuni, bakincikin Uwani ga kuma tararrabin halin da Salima take ciki ya risketa a farkon dare. A yadda ta fito rakiyar nan haka ta kutsa kai cikin adaidaita sahun da ya kawosu ko cikin gidan bata koma ba. Silifas ne a kafafunta sai hijabin da tayi sallah wanda da shi makotan suka risketa. Hannun Ihsan kawai ta rike tana karanto addu'a a zuci suka koma cikin adaidaitan.
Su Hasiya sai ganin wadanda Innayo ta fita rakawa sun dawo su kadai suka yi. Kusan a tare suke rige rigen fada musu abin da suka ji da gani. Maimuna har ta soma kuka Hasiya ta tabata. Sai da matan suka fita ta sanar da ita yadda suka yi dazu.
"Duk da haka Hasiya idan kuma na gaske ne fa. Ni dai ki zo muje."
*
"Ban gane wannan sabon shishigi da ku ka soma yiwa matar nan ba ke da Munzali."
Ummakati shiru tayi ta dafe kanta da hannu daya kamar mai ciwon kai tana sauraren Asabe. Tun shigowarta dakin take ta yi mata fadan zuwan da tayi da magariba kamar dole. Sannan ana karo karon kudi ita ma ta dauka ta bayar ko shawara da ita bata yi ba.
"Tunda kin bawa banza ajiyata ai gara ki tashi ki tafi"
Asabe ta furta cikin fushi. Bata ga dalilin wannan binbini da Innayo ta fara yiwa yaranta ba. Ta dade da sanin darajar daukar ciki da haihuwa take ci a wurin Munzali amma bata gabansa. Ummakatin da take mace kuma cikin rufin asiri ita kuma bakar rowa gareta a nata tunanin. Amma don neman suna ta dauki kudi ta bawa Innayo.
Gatse ne ko shagube, kalaman ba suyiwa Ummakati dadi ba. Tayi bayanin har ta gaji amma Asabe taki yarda. Surukarta ta ninka Asabe a komai ma. Ga rigima ga fitina. Dan nata ma tsoronta yake ji. Kuma a haka kiris take jira ta saka shi sakin Ummakatin saboda wai gidan da ta fito bai yi mata ba. Daga Alh. Rabi'u har Asabe babu mai daraja a idonta.
"Ki yi hakuri."
Tsaki Asabe ta ja tana mai cigaba da sakin maganganu.
"Bani abin da kika kawo min ki tashi ki tafi kafin babanku ya san kin zo don cewa zai yi sai mun raba. Ko yana ina lokacin da nake fadi tashin gina ku ban sani ba."
"Hmmm" Ummakati ta furta a hankali hannunta a jikin zip din jakarta. Dubu biyar din da ta lalube aljihun mijinta ta dauko ta mika mata. Idan bata bayar ba ta san watan kwasar bakincikinta ne zai tsaya. Har gida za ta dinga zuwa tana zubar da mutumci a gaban jikoki da babansu. Ba za ta yarda cewa Asabe ta manta da yadda suka tashi babu kulawarta ba. Banda tsarewa ta Allah da ta dade da shiga duniya kamar kawarta da suka yi 'yammatanci tare.
A hanyarta ta fita ne ta tsaya yiwa su Innayo sallama. Nan ta ji abin da ke faruwa a bakin Maimuna. Ta ce su taso su tafi tare. Ayaah kawai aka bari a dakin ta kula da Zara da jinjirarta.
Asabe da ta san ba sauraronta Ummakati za ta yi ba ko ta ce kada ta kaisu sai cewa tayi,
"Yau dai ranar ta Innayo ce. Ana ta ganin bacin rai akan 'ya'yan da ake cika mana baki a kansu. An gama gulmata akan tarbiyar 'ya'ya sai gashi sune da arzikin da ake ci. Munzali ya sakar muku bakin aljihu yanzu gashi motar Ummakati za ku shiga. Duk wani asiri kuma da surkullen mutum zai yi ya gama ne. Kurkuwarmu kurrrr....." ta bisu har soro tana fada.
Dama can ba ayi musu tarbiyar mayar mata da magana ba ballantana kuma yanzu da 'yarta take wajen. Hasiya da Maimuna sai suka kama bakunansu. Murja da Ummi su ma basu tanka ba. Yaran Maimuna kuwa basa wurin. Su aka tura shigo da adaidaita sahu kafin shigar Ummakati dakin.
A zaune suka sami Salima da suka isa gidan. Fuskarta a kumbure ta sha kuka. Mata kuwa harda wasu mazan sun cika 'yar tsakar gidan babu masaka tsinke. Kowa bayanin abin da ya sani yake yiwa Innayo.
"Mama ku ma kun yi sakaci tunda abu ne na shekara da shekaru. Ba don tana da tsahon rai ba ma da tuni labari ya dade da shan bamban."
Matar da tayi maganar Innayo ta duba ta jinjina kai. Tabbas da laifinta. Duk da Salima bata fada ba amma ta jima tana hasashen hakan saboda irin