Showing 117001 words to 120000 words out of 242549 words

Chapter 40 - UWA UWACE COMPLETE BOOK by Fatty Noor.txt

09 Oct 2025

3370

ya duka ya daukosu. Hannu kawai ya zura a aljihun ya mayar dasu sannan ya kama zip din zai ja sai yaji ya rike yaki motsawa. Jibge kayan hannunsa ya yi ya juyo da jakar yadda zai ga zip din da kyau. Abu ne kamar takarda ya makale yasa taki zuguwa. A lokacin da ya zube kayan hannunsa akan gadon ne wayar Alh. Tahir wadda yake amfani da ita wurin kiran 'yan matansa ta fado daga aljihun babbar rigarsa. Lilu bai kula ba ya gama gyara zip ya kwashe wayoyin da yazo dasu a hannu ya yi gaba.

Alh. Tahir bai tashi sanin wayar bata nan ba sai dare bayan Jiddo mai girki a ranar tayi bacci. Hankalinsa kuwa a take ya tashi. Ko a office ba zai so barinta ba saboda gudun fadawa hannun da zai ji kunya, ballantana kuma gida. A daren nan wurin daya saura ya fita yaje motar ya dudduba tunda ya san a hanya ma ya amsa waya da ita.

Motsin wucewarsa Lilu yaji a lokacin yana kallo ya tashi ya leka taga. Ya yi mamakin me Abban nasu yake nema a mota a daren. Kamar ya fita tambayarsa sai yaga ya koma. Laptop dinsa ya kashe ya kade bargonsa ba tare da kula da wayar da ta fado daga kai ba ya haye gado ya kwanta.

Wurin karfe tara ya fito zai tafi makaranta yaga Alh. Tahir tsaye da jallabiya ga direbansa yana ta bankade mota yana dube dube. Karasawa ya yi ya gaishesu duka.

"Abba me ake nema ne? Jiya ma cikin dare na ganka kana duba motar nan."

Murmushin dole Alh. Tahir ya yi saboda kada ya nuna ya damu da wayar.

"Babu komai jeka abinka" ya ce masa. Shi kuma direban ya ce "wayar Alhaji" a lokaci guda.

"Abba ka duba. Jiya duka wayoyinka na kawo maka daki."

Kamar gaske Alh. Tahir sai ya saki fuska "bari naje na duba. Sai ka dawo."

Ana rufe gate din gidan ya dawo da idanunsa da suke nuna tsantsar bacin rai ga direbansa. Hankalinsa ya matukar tashi.

"Idan wayar nan ta fada hannun wani saboda sakacinka a bakin aikinka."

Direba cigaba da bincike ya yi yana mamakin wannan abu. Shi ko kalar wayar ba zai ce ya sani ba amma an dora masa laifin batanta.

Ana gobe zasu tafi Kano Mami Khadija ta kafa sharadin duk wanda bai gyara dakinsa ba babu inda zai je. Kamun amarya ne wanda aka hada da mother's eve da dinner za ayi a Kanon. Babu mai son a barshi da kallon hotuna yana cizon yatsa. Ita kanta ta san da wa take dama. Lilu ne dakinsa sai tayi da gaske yale gyarawa. Alh. Tahir ya so masu aiki su dinga gyara musu ta ce sam bata yarda ba. Tana barin wurin ya fice daga gidan. Shawarma ya siyo guda biyu manya manya da robobin yoghurt ya shige wurinsu Sauda. Mardiyya ce ta fara jin kamshin shawarmar ta tashi da murna za ta karbi ledar ya boye abarsa.

"Kun dai ji me Mami ta ce. A gyara min palace dina a ci dadi. Bari na saka muku yoghurt din a fridge kafin ku gama."

Da gudu gudu suka bi bayansa. Wasu kaya ya dauka a leda ya tafi dakin Suhaib ya shirya. Dinner din gidansu abokinsa ya tafi.

Sauda ta fada toilet aka bar Mardiyya da uban shirgin kayansa. Tana cikin ninki taci karo da waya a kasan gado. Lilu bai san da ita ba balle ya kula da faduwarta. Daukewa tayi ta jona masa tunda taga chaja a jikin bango. Da suka gama aikin ta kunna masa kafin ta fita. Shi kuma da ya dawo ko bi ta kan wurin bai yi ba ya kwanta saboda gajiya. Da safe bayan sun gama shiri sun dauki hanya Yumna ta dinga kiran wayar.

***





0UWA UWACE...24


Batul Mamman💖



Shafin na Baaba Jummai (Minna) ne. Ina godiya tare da turo tawa dubun gaisuwar da fatan alkhairi.




***

Flashing ya kai shida Danladi ya yiwa Ayaah. Tsabar kwarewa wasu a ciki ma bata jin karar wayar sai dai taga haske kamar walkiya ya bace. Hakura tayi da son dauka ta kira shi da kanta. Abin da ya fara cewa yana daukar wayar shi ne,

"Gaskiya kuna da matsalar netwok a unguwar nan. Zuwana nan na kira ki ya fi sau goma. Har na fara tunanin turo yaro a kira min ke tunda ba zan iya tafiya ban ga murmushinki ba."

Da sanyin murya ya yi magana. Cikin wani irin yanayi mai sa mutum ya ji kamar ya aikata gagarumin laifi. Ayaah taji babu dadi ta shiga bashi hakuri duk da a bangare guda tana cike da farinciki game da kalamansa. Da ya nuna mata kamar komai ya wuce sai ta ce ya ajiye mota a bayan layinsu za ta zo nan ta same shi.

"Yanzu Babanmu ya kira Anti cewa yana hanya tare da bako. To ban sani ba ko bakon da zai kai ciki ne ko mai tsayawa a soro. Kuma kaga baku taba haduwa ba zai fi kyau ku hadu yana shi kadai."

Cije lebe Danladi ya yi ransa na kuna. A soron nan nasu mai dan duhu ya so ya fara koya mata gurbatacciyar soyayyarsa. Gashi bai sami motar da tayi masa a garejin ba. A ina zai sami wannan damar idan suka hadu a filin Allah? Da muryarsa da ya kware wurin kwantarwa domin ya sanyawa 'yan mata tausayinsa ya yi mata magana.

"To babu komai Ayaah. Ba zan so na takuraki ko na sanyaki cikin yanayi mara dadi ba. Banda zuciyata da ta kasa sukuni saboda tunaninki da na hakura sai lokacin da kike so na zo."

Numfashi taja wanda ya bashi damar yin murmushin samun nasara tun kafin ta furta ta bakinta. Yadda yaso haka ta ce za ayi. Duk da tana jin nauyi haka ta daure taje ta fadawa Hasiya za tayi bako. Murmushi Antin tasu tayi gami da 'yar tsokana.

"Gilashi zan saka domin na tantance ko ya cancanci zama surukina. To amma wani hanzari ba gudu ba. Ki bashi hakuri ya jira zuwa gobe. Kinga Babanku yana hanya da bako."

Ko kadan Ayaah bata son batawa Dani rai. A tunaninta zai fassara rashin sauraronsa daidai da abin da yake fada mata matarsa tana yi. Zai shiga damuwa idan basu hadu ba kuma bata son haka.

"Anti ko inje gidan Mal. Tasi ya sameni a can sai na bashi hakuri tunda ya riga ya zo?"

Katangarsu daya da ta gidan Mal. Tasi din. Yadda ta marairaice fuska sai Hasiya ta amince. Dakin Abbas ta koma suna hira da Murja mai bashi abinci. A zuciyarta take tunanin lallai Ayaah tana son bakon nata. Za ta sanar da Honorable tun wuri ayi binciken da ya dace.

Ayaah kuwa da saurinta ta sake kiran Dani ta fada masa inda zasu hadu. Ba haka yaso ba amma ya fiye masa waje. Tana cikin gaisawa da matar Mal. Tasi tare da fada mata abin da ya kawota taji sallamarsa. Wani iri ta dan ji tunda ta zata zai kirata ne. Da babu alaka mai kyau tsakanin gidan da nasu kuma ba ayi mata izini ba haka zai zo kenan? Ta tambayi kanta. Haka nan dai ta tashi da ledar da ta sako madaidaicin filas din da ta zuba masa abinci. Tana doso soron kamshi ya dinga hawa kanta. Yau ma turaruka 'yan duri ya bulbula sai dai hannu ya so zarcewa. Kamshin ya yi yawa har yana neman sakawa mai shaka mak'ak'in wuya.

Suna hada ido ta manta da komai sakamakon murmushin da ya sakar mata. Yana da nashi kyawun amma babban abin da ya zame masa jari bai wuce yanayin jikinsa ba. Ga tsayi ga kaurin da bai kai a kira shi kiba ba. A idonta gani tayi kamar ya fad'a. Haushin matarsa ya kamata. Ta yaya mace za tayi sake mijinta ya dinga ramewa saboda rashin kulawa da abinci?

"Mom dina tana gaishe ki"

Rausayar da kai tayi gefe tana murmushin jindadi ta ce "ta sanni ne?"

Dariya ya yi mata yana mai cewa babu wani abu nasa da mom din bata sani ba.
"Idan ta dawo daga Dubai har gida zamu je ki gaisheta."

Ayaah sai tayi murmushi. Ina ita ina zuwa gaishe da uwar saurayi? Ba Anti Hasiya da Babansu ba ko su Anti Fati da kakarta Larai sai sun kusa yankata. Yawo ba tarbiyarsu bace. Idan ya sake tayar da zancen a gaba za ta kirkiro hanyar fitar da kanta don babu inda za ta je.

Ledar hannunta ta mika masa ya dinga godiya da shi mata albarka. Harda cewa wai ya akayi ta san yana jin yunwa? Filas din wan can karon da na yau ya yi mata alkawarin kawowa duka a washegari.

Wurin karbar ledar ne ya samu ya hada da hannunta ya matse. Gabanta taji ya yi mummunar faduwa taja hannun da sauri amma ta kasa kwacewa saboda ya rike gam. Ja ta sake yaki saki sai ma wani irin shafawa da ya dinga yi a hankali yana mai bin kwayar idanunta da kallo da nasa da suka yi alamun tausayi. Ilahirin jikinta babu inda baya rawa kamar mazari. Cikin dabara ya rage tazarar dake tsakaninsu.

"Ki dago ki kalleni Ayaah" ya ce a kasalance.

Kasawa tayi sai girgiza kai da take yi tana son cewa ya saketa. Danladi sai ya saka yatsunsa biyu ya dago kanta. Runtse idanu tayi da sauri taji ya yi karamar dariya.

"Kunya ki ke ji? Gashi ni kuma mutum ne mai son kulawa. Kulawar da na rasa a gida. Ina fata da addu'ar ki cike min wannan gurbin ki hanani tunawa akwai kowacce mace bayan ke. Idan kin amince min zan yiwa Mom magana kawunnai na su zo ganin Baba."

Runguntsumi sunan abin da Danladi ya yiwa Ayaah domin yaji dadin isar da mummunan kudurinsa. A lokacin da yake son bude mata ido da haramtacciyar mu'amala ya kama zuciyarta a hannu ta hanyar nuna mata yana sonta. Banda haka ya hada da maganar aure da mata ke so a wannan zamani. Sannan ya rufeta ruf da ya nuna mata cewa za ta zo gidansa a matsayin mai share hawaye. Wannan tunani ke sanya mata mugun tausayin namiji da ganin ba zai rayu babu su ba.

Da kyar ta iya mallakar tunaninta ta ja jikinta baya. Muryarta ko fita bata yi sosai ta ce,
"Ka sakar min hannu don Allah. Kaga babu kyau."

"Nima ba zan so yin abu mara da ke ba. Kiyi hakuri" ya ce yana sakin hannun.

Ko sallama bata yi masa ba ta fita daga soron. Ya kwashe da dariya
"Kin kusa samuwa."

Ficewa ya yi abinsa da ledar abinci ya tafi gida. Yana zuwa ya bawa Raiha yana wani cin magani.
"Sai ki saki ran ai. Baki san irin kokarin da nake domin samar muku abinci ba. Don na karbi darin dazu ki ke ta kumbure kumbure. Ki zuba min ku ci sauran"

Bude filas din tayi ta ganshi shakare da abinci sai kamshi yake. Cikinta ya bada wani uban sautin yunwa. Da sauri ta samo faranti ta dibar masa sannan ta taso yaranta tana basu tana ci. Tambayar inda ya samo abincin bai zo mata ba don ta zata sayowa ya yi.

*

A dakin Abbas iyalin Honorable Habu suka hadu ya nuna su ga Abdulkarim wanda tausayin Abbas ya kusa saka shi kuka. Addu'ar samun lafiya ya yi masa tare da jaddadawa Honorable lallai ranar litinin a mayar dashi asibiti. Duk abin da ake ciki a sanar dashi. Hasiya tsabar farinciki sai da tayi kuka. Da zai tafi tayi masa tayin abinci sai ya ce a zuba masa ya tafi dashi. Dan filas din da yake madaidaici mai kyau shi Ayaah ta kai wa Danladi. Aka yi neman duniya aka rasa. Murja sai rantsuwar ta wanke shi take yi. Hasiya ta ce babu komai su bar maganar kada bakon yaji. Na maigidan ta saka a leda aka bashi. Bayan tafiyarsa ne ta rutsa Ayaah a kitchen ta tambayeta inda ta kai shi.

"Lokacin da zaki fita wurin bakonki na ganki da leda da abu kamar shi sai dai ban zata abinci ki ka diba ba shi yasa ban miki magana ba."

Sunkuyar da kai Ayaah tayi. Hasiya ta daure fuska saboda bata so hasashenta ya zama gaskiya ba.

"Na zata mun wuce wannan matakin Ayaah. Kin sani sarai rowa ba halin gidan nan bace amma ba zan lamunci yiwa saurayi girki ba! Wato dalilinki na karbar girkin Ummita kenan? Bai ji komai ba ya karbi abinci a hannunki ko mahaifinki bai taba gaisarwa ba?"

Tuni zuciya ta soma tunzurata. Ba za ta iya jure kalamai marasa dadi a kansa ba. Idan ba a tayata tausayinsa ba ai bai dace a aibata shi ba.

"Anti matarsa ce fa bata girki. Shi ne na zuba mishi ba roka ya yi ba. Bata yi masa komai ko ya roka sai taga dama."

Hasiya sai ta hadiye fadanta ta kirkiro murmushi ganin abin ya girmi abincin da ta bayar.

"Kin kyauta da ki ka taimaka masa amma nan gaba ki dinga tambayata kinji ko? Kuma ki ce lallai zuwa na gaba ya zo mu ganshi."

Ayaah sai murmushi. Tasa hannu ta rufe fuska sannan ta tashi a guje tana yiwa Hasiya godiya. Ita kuwa bayan tafiyar Ayaah daki ta koma ta rafka tagumi. Gabadaya saurayin bai yi mata ba daga jin furucin Ayaah. Maza masu tonawa iyalansu na gida asiri ba mazan kwarai bane mafiya yawan lokuta. Ta kuma fuskanci ya riga ya fara dasa mata wani tunani. Tashi guda idan ta nemi rabasu za a iya samun matsala. Gida za taje suyi shawara da Salima don ta fita fahimtar halayyar yara. Shawarar data bata kwanaki ita ce ta taimaka wurin kara kusantasu da juna.

***

Ginin shopping mall din su Abbati ya yi nisa. Hankali kwance komai yake tafiya yadda suke so. Ga tafiyarsu Italy asibiti tana ta matsowa. A lissafi nan da kwanaki goma sha bakwai zasu tashi. Suna fata idan an dace babu wani abu da zai yi saura a tare dasu na bukatar jinsinsu. A gefe guda suna cike da farincikin daina jin motsin Shazali. Tun zuwan da Munzali ya yi gidansa ya masa dukan nan akan tafiyar Abbati bai sake nemansu ba. A zatonsu an rabu kenan...

Yau ta kama Alhamis suna site din gininsu tare da masu aiki ana ta lissafin kudaden da zasu kawo domin siyan wasu kayan aikin. Hankulansu sun raja'a kan abin da ke gabansu wayar Abbati ta soma ringing. A hannunsa take ya juyo da ita yaga sunan Farha ya bayyana a screen din. A take zuciyarsa ta doka dan tsalle sai kuma ta koma ta kwanta. Tun zuwansu Kaduna da bai hadu da ita ba yake kiran wayarta a kashe. Yau kwana biyar sannan za ta kira shi. Yana son dauka yana jin tsoron me za ta ce. Muryar Munzali yaji wanda ya zuro kai ta kafadarsa.

"A haka dai kamar za kayi abin arziki amma daukan waya ya gagareka. Tsoron me kake ji ne?"

"Ni kar ka kara min tension ka matsa ka bani wuri" Abbati ya bashi amsa yana kokarin matsawa gefe domin yaji dadin amsa wayar.

"Ita ma fa tana sonka"

Tsayuwa Abbati ya yi ya juyo ya kalli Munzali da murmushi kamar Farha da kanta ta fada masa.

"Ai fa na kasheka da dadi to dauki kada ta kuma tsinkewa" Munzali ya ce yana kara yi masa dariya.

"Kaima ka ce wani abu. Bari na sallameta zan gamu da kai."

Gefe ya matsa don idan Munzali ya saka shi a gaba kila hirar ba za tayi armashi da kyau ba. Yana dauka yaji zazzakar muryarta mai taushi tana magana.

"Ya Auwal"

Shiru...Abbati ya sake nutsewa cikin kogin son Ya Farha.

"Ko dai wrong number na kira?" Tayi tambayar da murmushin da yake kan fuskarta tun lokacin da ta yanke shawarar kiransa da sunan gaskiyarsa idan ya dauki wayar.

"Ki ka ce baki san shi ba" Abbati ya fada a hankali da ya rasa me zai ce.

"Na san shi. Kararsa ma na kawo maka"

Sai da ya jingina da bango ya cigaba da sauraron bayaninta. Korafi tayi masa na rashin nemanta ranar da yaje Kaduna a wurin 'yan uwanta. Ta tabbata da ya yi hakan dole zasu kai shi gidan kakaninta. Ita kuma wayarta ce gida na taro aka nema aka rasa a ranar. Ba ita tayi sabuwar waya ba sai da safe kafin su taho Kano. Kin fadawa Alh. Tahir wanda zai saya mata sabuwa a guje tayi. Sai da safen Mami Khadija ta bata kudi ta saya.

"Kina nufin iskar gari daya muke shaka? Shi yasa yau nake jina daban."

"Uhummm. Wane canji aka samu?"

"Iska mai dadi, gari yana kamshi, zuciya kuma sakayau."

Farha sai ta kama dariyar yadda yake magana. Kwatancen inda suka yi masauki ya nema ta ce ba za ta iya gane komai a hanyar ba. Wata 'yar uwarsu ta samu 'yar gidan da suke tayi masa kwatancen. Hira suka yi inda take fada masa daurin auren kanin Maminsu ne za ayi ta kuma gayyacesu. Hoton IV din za ta tura masa ta whatsapp don bata san unguwannin Kano ba.

"Idan kun fita ki dinga kallon hanya tunda zama ya kusa kawo ki."

Kunya kuwa ta kamata ta ce "Ni sai anjima".

"Mu jima da yawa Ya Farha sarkin kunya. Yau dai tunda bikin na yamma ne ba zan zo ba. Amma gobe da jibi kafin ku koma in sha Allahu zan zo."

*

Anyi kamu ranar Alhamis din tare dasu Mami Khadija da suka iso ita da sauran yaran. Ranar Juma'a kuma sai bayan magariba za a tafi wurin dinner. Farha ta sami Lilu tayi masa famfo akan ya tambayi Mami ko zasu sami kati guda biyu tunda event din card admit ne. Shakiyanci ya yi mata kuwa son rai tana shanyewa sannan ya tafi wurin Mami. Yana gama fada mata zancen da ya tsara ta girgiza kai tana murmushi.

"Dama kai ai ko ba aiko ka aka yi ba nayi tunanin za ka iya nema musu."

Shafa kansa ya yi yana dariya "wallahi Mami don ba ki yi musu kallon kwaf bane amma sun hadu."

"Allah Ya tsareni da yi musu kallon kwaf" ta ce tana mikewa da dariya. Babu wanda ya san irin farincikin da take ciki sakamakon soyayyar da taji akwai a tsakanin Abbati da Farha.

Sun yi sa'ar samun katuna a wadace daga wurin dangin amarya masu shirya dinar. Hakan kuwa ya faru ne saboda suma zasu yi tasu a Kaduna idan an kai amarya. Yadda suka

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login