Showing 180001 words to 183000 words out of 242549 words

Chapter 61 - UWA UWACE COMPLETE BOOK by Fatty Noor.txt

09 Oct 2025

3347

kunkuni ta ce,

"Ni wallahi na zata ma sona kake shi yasa ka taimaka min."

Tun bayan zuwansa Kano a yau sai yanzu Suhaib ya yi dariya. Dariya mara karfin amo amma mai nuni da har cikin zuciya mai yinta yana cikin nishadi.

"Wato kin zata sonki nake?"

Ayaah ta murguda baki da kumburarrun idanunta ta ce
"Dariya ma na baka?"

"Ai dole nayi dariya."

Ance wai mai hali baya fasawa. To Ayaah ma bata manta tsiwarta ba tunda Danliti bai sami damar koya mata hankali ba. Juya idanu taso yi amma nauyinsu ya hanasu bata hadin kai. Sai ma zafi da suka yi wanda yasa ta runtsesu da sauri. Duk da haka bata hakura ba sai da ta ce,

"Ko a nan gaba kaji kana sona kada ma ka fada don ba zan baka hadin kai ba."

"Zamu gani" ya ce yana cigaba da murmushi.

Kofar da aka taba ta danyi kara ce ta kawo karshen maganar tasu. Honourable ne a gaba sai Minista, matan suna biye dasu.

An zazzauna kowa ya fuskanci Ayaah wadda ta rakube a jikin Anti Hasiya. Honourable ne ya soma magana cikin nutsuwar da ya arawa kansa ta dole.

"Kun san zaman me muke yi a nan? Ku dubi girman Allah ku fada mana gaskiyar abin da ya faru."

Ayaah baki sai ya soma rawa. Dauriyar da taso yi ta kasa sai kuka. Wannan yasa Suhaib ya karbi ragamar jawabin daga inda ya sani.

"Suna na Suhaib Tahir kuma a Kaduna nake da zama. Kanwata Mardiyya ita ce Alh. Munzali yake nema..."

Innayo ta gyada kai saboda tun dazu take yi masa kallon sani. Ya cigaba da fada musu ranar da ya fara ganin Danliti a wurin dinner. Sai ya sakaya ya ce matar dan uwansa ce ba matar babansa ba. Irin abubuwan da ya gani da maganganun da Danlitin ya yiwa Jiddo da Ayaah duk ya fada. Akan haka ne hankalinsa bai kwanta ba har ya karbi nambarsa a wurin Jiddo da zuwansa Kano. Dama duka abubuwan da suka biyo baya har ya sami damar kubutar da ita da taimakon Allah.

La haula wala quwwata illa billah. Suhaib yana bayani Anti Hasiya da Larai suna kuka. Innayo ma ba a barta a baya ba domin tabbas ba don tsarewar Ubangiji ba da yanzu suna kukan bakinciki. Honourable kuwa sunkuyar da kansa ya yi kasa. Shi kadai ya san halin da zuciyarsa take ciki. Sam ya kasa magana sai Abdulkarim ne ya dauki matsayin uban. Godiya ya fara yiwa Suhaib sannan ya koma kan Ayaah.

"Saura ke"

"Don Allah ku yi hakuri" ta fara cewa Larai ta daka mata tsawa.

"Za kiyi bayani ko sai na saba miki? Mutuniyar banza mutuniyar hofi."

Idanunta a kasa ta fadi abin da ya kamata ta fada. Tana magana hannunta yana cikin na Hasiya wadda ta rike domin bata kwarin gwiwa. Labarin bai yi mata dadi ba amma kuma bata so tsoro ya hanasu gane bakin zaren.

Kunyar duniya yau Ayaah ta gama sha. Da bakinta take maimaita yadda abubuwa suka kasance a gaban iyayenta da Suhaib. Ko ba a fada ba ita da kanta ta dinga ganin wautarta na yarda da zantukansa baro baro.

Honourable ya dago kai a fusace bayan ta gama magana.

"Taso ki zo nan?"

Suhaib ya kula da bacin ransa sosai. Shi ma zuciyarsa a cunkushe take da takaici amma bai bar tausayinta ba. Yana jin kiran da mahaifinta ya yi mata sai ya mike tsam. Hukunci ya zama wajibi sannan shi din bashi da hurumin hanawa.

"Bari na baku wuri"

Bai jira yaji abin da zasu ce ba ya fita daga falon. Haka Ayaah ta rarrafa gaban babanta ta kama kafafunsa tana kuka. Hakan bai hana shi tureta ba ya daga hannu zai mareta Abdulkarim ya hana.

"Bata kyauta ba amma don Allah kayi hakuri. Mace kamar wannan ta wuce ladabtarwa da duka"

"Inji wa?" Cewar Larai tana face majina "yau ba don yaron can dan albarka ba da yanzu muna cizon yatsa"

"Duk da haka dukan bashi da amfani. Kamata ya yi mu godewa Allah da Ya tsare mutumcinta"

"Sai kuma ayi mata me bayan addu'ar? In kyaleta gobe ma ta bi wani katon banzan?" Honourable ya tambaya cikin fushi.

Kafafunsa Ayaah ta sake dafawa ta ce "Don Allah kayi hakuri Baba ka yafe min. Wallahi ba zan kara ba."

Girgiza kai ya yi da disappointment karara a fuskarsa "kin bani mamaki Ayaah. Kamarki ace kin iya hada baki da namiji ya zo makaranta ya daukeki. To ma wa ya san tun yaushe hakan take faruwa?"

A gigice ta dora hannu a baki tana rantsuwa "wallahi yau ne kadai."

"Kina tunanin zan yarda ne?"

Bata fuska Larai tayi "ban gane ba Habu, me kake son cewa? Tun dazu nake ta bata laifi tunda na san bata kyauta ba. Amma ba zan zuba ido ka jefeta da kazafi ba." Ta juya bangaren Anti Hasiya "dama na fada da sa hannunki akan abin da Ayaah tayi. Banda haka wace uwa ce zata kasa gane irin wadannan abubuwan? Da ace kina kula da marayun nan ai da kin fahimci abin da take yi tun kafin ya yi nisa. Ki bari ki haihu din kafin ki wargaza rayuwar 'ya'yan gidan."

"Maganganu irin wadannan basu dace da gab'ar da muke kai ba Larai." Innayo ta furta cikin lumana. Na farko Honourable Habu suruki ne sannan ga bakonsa. Bai dace magana irin wannan ma ta raso a yanayin da ake ciki ba. Sannan ta gaji da daure zuciyarta kan kalaman Larai akan Hasiya. Tana tsoron kada a kai ta bango ta rama duk su taru su bawa kansu kunya.

Mayar da kallonta tayi ga Ayaah ta ce "ina ji a jikina abin da ya faru yau ya isheki darasi da ishara akan rayuwar da kika so jefa kanki a baya. Ki kiyayi maimaituwar yau din a rayuwarki domin duk ranar da namiji a sami galaba a kanki walau da son ranki ko babu indai babu aure a tsakaninku ya cuceki har abada. Wani tsautsayin kirawo shi ake yi da sakaci. Allah Ya kiyaye gaba."

Amin suka amsa su duka har Larai din. Abdulkarim ya yi murmushi a ransa yana kara yabawa da tsatson da Hasiya ta fito wanda ya yi tasiri akan 'ya'yan Honourable. Dolensa ma ya zage damtse akan Ummita don bai ga wadda ta dace ya nema da gaske ba kamar ita.

Innayo sallama ta yi musu ta ce zata tafi. Honourable sai ya ce yana son su zama shaida akan hukuncin da zai yankewa Ayaah. Jin batunsa Anti Hasiya da Ayaan suka dinga bashi hakuri. Suna cike da tsoron abin da zai ce. Sun san shi mutum ne mai hakuri da kawaici amma bashi da dadi idan ya kai bango. Ummita da Murja yasa Ayaah ta fita ta kirawo masa. Babu bata lokaci sai gasu duka a tare kowacce ciki ya duri ruwa. Fadan baban nasu bashi da dadi ko kadan.

"Ku zama shaida" ya ce dasu Innayo, "ban yarda Ayaah ta sake fita in ba tare da wani daga cikin gidan nan ba. Makaranta ma in sha Allahu ta bar zuwa sai ranakun jarabawa. Shi ma da kaina zan dinga rakata na daukota. Sannan in sha Allahu sati daya da gama jarabawar Ayaah zan aurar dasu. Duk wadda bata da manemi zan samar mata kafin lokacin. Ke kuma..." Ya nuna Murja "ki fadawa Mahiru tunda dama ni suke jira. Ku tashi ku tafi."

Murja ta mike. Ayaah da Ummita suka kasa kwakkwaran motsi. Maganar abin da bai fi wata uku ake ba. Kuma basu da maneman a hannu. Anti Hasiya ma maganar dirar mikiya tayi mata. Ayaah kam tayi laifi mai girma sai dai ko kusa ba za ta yarda ya yiwa yaran nan auren dole ba. Ita da nata mahaifin ya yi mata, Allah ne kawai Ya dubi zukatansu ita da mahaifiyarta Ya daidaita zaman. Sai ya kasance Honourable din ya zarce duka tunaninsu a fagen kyautatawa sabanin sanin da suke tunanin sun yi masa lokacin yana auren A'i.

"Ku tashi mu tafi" ta ce da 'ya'yan nata ganin hatta Ummita ita ma kukan take. Suka bi bayanta kuwa suna tafe kamar kwai ya fashe musu a ciki.

Da fitarsu Honourable ya bawa kowa mamaki da ya yi 'yar dariya. Innayo ma da Abdulkarim sai da suka murmusa. Ita nata ya dace da na Honourable. Fushi ne suke gani muraran Hasiya tana yi na sanya mata yara a tsaka mai wuya. Shi kuwa Abdulkarim na farincikin fahimtar cewa Ummita bata da kowa a hannu yake. Lallai zai ci karensa babu babbaka. Tunda babu wani yaro a hannu da zai masa shigar sauri ya hure mata kunne.

Dakin da suka baro su Maimuna suka shiga, Ummita da Ayaah suna kuka babar tasu ma tana yi. Maimuna ta gaji da rarrashinsu ta koma fada.

"Tunda baku san hakuri ba sai kuyi ta yi. Amma ki sa Ayaah ta cire rigar d'an mutane ta mika masa"

Sai a lokacin ta tuna da rigar. Da sauri ta shiga balle maballan ta cire ta mikawa Murja.

"Don Allah ki kai masa"

Anti Hasiya ta kai mata duka ta kauce

"Amma baki da kirki Ayaah. Mutum ya yi miki irin wannan taimakon amma godiya ta kasa shiga tsakaninku. Tashi maza ki kai masa da kanki."

Hijab ta dora ta fita tana jiyo muryar Larai tana bada labarin abin da ya faru. Duk inda take tunanin ganinsa kama daga tsakar gidan, soro da kofar gida. Bata manta da gargadin babanta ba saboda haka bata yarda ta fita ba. Ciki ta dawo da niyar daukar wayarta ta kira shi sai ta kula da takalminsa a kofar falon. Kenan Baba ne ya sake kiransa ta ambata a zuciyarta. Kamar wadda tayi magana da karfi sai ji tayi Babanta ya kwala mata kira.

Da hanzari ta shiga don yanzu bata kaunar abin da zai bata masa rai.

"Dama rigarsa zan ce ki kawo ashe ma kin dauko."

Abdulkarim sai cewa yayi "muje waje in ganka kafin na wuce Honourable."

Hon. Habu ya dan yi turus sai da ya sake maimaitawa ya mike. Suna fita Abdulkarim din ya ce da Suhaib idan ya fito zasu yi sallah don har biyu da rabi.

Rigar ta mika masa bayan sun fita ta furta kalmar godiya a hankali.

"Ya naga duk kin yi laushi ne? Ko hukuncin da Baba ya ce min ya yanke ne bai yi miki ba?"

Dago rinannun idanunta tayj da sauri ta ce "yanzu sai da ya fada maka zai min auren dole?"

"A'a" ya ce yana mai girgiza kansa "cewa ya yi kawai za ki daina fita har zuwa school sai kina da paper" ya kare da dan murmushi.

"Auren dolen ka ke yiwa dariya ko hanani fita?"

"Kina da rigima" Suhaib ya furta da wani irin yanayi sannan ya tashi tsaye "ni zan wuce. Sai in ce sai mun zo biki ko?"

Shiru tayi bata kula shi ba don ta kula yana jindadin zolayarta.

"Au ba za ki amsa ba?"

"Kana farinciki da auren dolen da za ayi min ya za ayi na amsa?"

Sai da ya je bakin kofa sannan ya juyo ya kalleta cikin ido ya ce "dazun nan ki ka yi warning dina da cewa ko ina sonki kada na fada domin ba za ki yarda ba. Ba don haka ba da na sake introducing kaina a wurinsa a matsayin...." Ya lumshe ido ya budesu a gajiye "idan kin bani matsayin da ya dace na sake gabatar da kaina a wurinsa ki kirani kafin lokaci ya kure mana. Take care."

Har ya fita su Ummita suka shigo bata sani ba don ba karamin kashe mata jiki da zuciya kalamansa suka yi ba.

Sallah ya tsaya suka yi sannan ya ce zai tafi. Ba yadda Honourable bai yi dashi ba akan ya zauna yaci abinci yace ya koshi. Da fitarsa bai zame ko ina ba sai garejin su Danliti. Ogansu ne ya kira shi yana shiga mota zai bar unguwarsu Ayaah.

"Mal. Suhaib muna kara godiya akan taimakon da kayi mana. Dalilin kiran naka kuwa yanzu ba wani abu bane illa wayarsa da nake son baka kafin 'yan sanda su nema."

"Waya kuma?" Suhaib ya furta yana yamutsa fuska saboda son sanin dalili.

Mutumin ya ce "Kwarai kuwa. 'Yan sandan da suka zo basu kula da ita ba sai wani cikin yarana ne ya dauko. Yanzu suka budeta har sun cire lock din ma. A garin bibiyar hirarrakinsa na chatting muka ci karo da hirarsa da wata mata suna kuma yawan ambaton sunanka. Matar har tana cewa idan ka zo Kano ya sake maka kamanni da duka. Shi ne nace gara dai ka zo ka gani kada ya cuci wata"

'Alhamdulillah' Suhaib ya ce yana mai fadada murmushin fuskarsa domin wannan batu ba karamin taimako zai yi masa ba. Shaida ce guda da zai samu ya nunawa Abbansu akan Jiddo. In anyi sa'a yaga cewa matarsa ma tana yin yadda yake ko kusa da kila ya canja hali. Da wannan tunanin ya wuce garejin.

Kafin ya karasa kafarsa ta dama ta soma wani irin tsukku kamar ana cakarta da allura. Da kyar ya iya karasawa sai dai yana fitowa ya kasa takata da kyau. Ogansu Danliti yana ganin yanayin tafiyarsa ya ce,

"Dama na san a rina. Wannan duka da ka yiwa kofar dakin nan da wuya idan baka bugu ba ko targade. Don da karaya ce da wuri zaka fara jin ciwon."

Wasa-wasa Suhaib kasa jan motar ya yi. Shi da ya yi niyar komawa Kaduna a lokacin sai gashi wani aka samu ya mayar dashi gidan kawunsu inda aka yi zaman biki. Abinci ma kasa ci yayi dole suka tafi wani asibitin kashi na kudi. Har x-ray aka yi masa saboda kafar ta fara kumbura ta wurin idon sawu. Dunduniyar kuma tana ciwo. Babu karaya yadda suke tsammani sai tsabar buguwa. Irin leg brace dinnan aka daura masa bayan an yi mata gashi sannan suka koma gida. Matan gidan suna can suna kiran Mami Khadija su sanar da ita shi kuwa ya kira Lilu ya ce ya taho washegari su koma tare.

***

Zara taga ikon Allah zamansu da Uwani bayan fitar su Innayo. Surutai take yi ita kadai kamar wadda ta sami tabin hankali. Kalma ko daya ba za ta iya cewa ta gane ba amma ga bakinta nan yana ta motsi da sauri-sauri. Abin tsoro ya soma bata ta tashi daga dakin ta koma falo. Kafin ta zauna Uwani ta fito tana mai cigaba da maganganunta. Babu zato taji ta ce mata,

"Kiyayyar da kuke min har ta kai a rasa mai tambayata damuwata Zara?"

"Idan na tambaya za ki fada min ne?"

Uwani na jin haka ta dawo kusa da ita ta zauna. Da gaske neman wanda zata saukewa damuwarta take. Innayo din da ta zata har abada ba za ta taba juya mata baya ba yau gashi tana magana taki sauraronta da kyau. Kanta ta dinga dunguri da yatsanta manuni.

"Zara ina ji wadansu notina suna kwancewa a kwakwalwata wallahi. Daf nake da zarewa idan Habibu bai dauki wayata ba"

"Habibu kuma ko Salihi?"

Uwani ta maimaita sunan da karfi "Habibu nace. Ai ce miki nayi kaina zai kwance ba wai ya kwance din ba"

Mikewa Zara tayi "me yayi zafi za ki sauke min fadanki. A kira Habibu lafiya"

Da sauri Uwani ta riko hannunta ta dawo ta zauna. Bata boye mata komai ba cikin matsalolin da suka fuskantota a dan kankanin lokaci.

"Idan na rasa komai wallahi zuciyata za ta iya bugawa. Zara gabadaya rayuwata fa akan yadda zan gujewa rayuwa irin ta Innayo na yita. Sai yanzu bayan na gama shan wahalar har ina hango soma cin arzikin sai komai ya rushe? Meye marabata da Innayo yanzu? Karatun da aikin duka babu riba."

Kwalla ce ta taru a idon Zara saboda ita kanta ta hango tsagwaron rashin hankali a zantukan Uwani.
"Ko kadan baki yi kuskure ba don kin yi fatan gujewa irin rayuwar Innayo. Babu wani mai hankali da zai so bayan ya tashi a wahale ya cigaba da rayuwa a haka. To amma kuskurenmu daya ne ni da ke. Mun so gujewa rayuwar ne mu kadai ba tare da tunanin wadda tayi sanadiyar rabamu da ita ba. Da gumin wa muka rayu? Wa ya ciyar dake? Waye ya kai ki makaranta? Wa ya aurar dake? Addu'ar waye ya zame miki garkuwa tsahon rayuwarki? Sai ace kuma da kika sami dadi ita ce mutum ta farko da kike gudu tamkar ita ta zabawa kanta kuncin da take ciki. Ke din wayonki ne yasa ki ka sami duka nasarorin da kike tinkaho dasu? Idan wayonki ne to ki sake tsallake wannan ramin dake gabanki. Ni dai na dawo daga rakiyar shaidanin da ya taba min zuciya. Uwata ita ce madubin rayuwata. Ranar da kika gane haka kuma ki ka roketa gafara shi ne lokacin da zaki fara ganin haske."

Tun zuwanta gidan ta kula da yadda Zara take neman shiri da Innayo. A zatonta abin na ganin ido ne kadai. Sai gashi taji daga bakinta. Wannan yasa tayi wata irin dariya. So take ta san waye mara hankali tsakanin ita da kanwar ta ta.

"Da bambanci sosai tsakanin matsalata da taki. Baki san juya kudi ba sai dai a dauka a baki. Shi yasa da miji ya juya miki baya ki ka yi saurin laushi a hannun Innayo tunda arzikinta kike ci. Ni kuwa gumina ne. Nafi karfin tozarcin da namiji wallahi."

"Hakka!" Cewar Zara da gatsali.

"Don kin ganni a gida ki ke min magana haka? Hala baki ji na fada miki ina da gidan kaina ba?"

"Kan ki kuma ake ji"

Zara dama ba kyalle bace. Da ta fuskanci Uwani bata da niyyar bin hanyar da take nuna mata sai taji gara a bar maganar kafin su fara fada. Tashi tayi ta fito falo. Uwani sai ta biyota rai a bace.

"Ni kike cewa kaina ake ji saboda ga 'yar macukule ko? Har kina da bakin fadawa wani magana ma ke da kike goyon 'ya mara suna?"

"Wai in tambayeki Uwani. Anya kin taba zama kin karewa Innayo kallo kuwa? Kin ma santa kuwa? Sani na wace ce ita a matsayin 'yar Adam ba na matsayinta na uwa a gareki ba." Shiru Uwani tayi tana sauraron zancen da Zara ta dauko.

"Innayo bata sami gatan uwa da uba ba a dalilin maraici amma mu ta zame mana uwa da uba harda kari. Mu tara ta aurar Uwani. Mata tara wata na bin wata. Ta sadaukar da lafiyarta da jindadinta domin rayuwarmu ta inganta. Amma cikinmu banda Hasiya waye take jindadi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login