Showing 114001 words to 117000 words out of 242549 words

Chapter 39 - UWA UWACE COMPLETE BOOK by Fatty Noor.txt

09 Oct 2025

3412

masa saboda rashin samun kulawar iyalinsa. Da kudinsa da komai amma abinci ma sai dai ya saya. Mai zurfin tunani kuwa za ta tausaya masa da farko. Idan an gama wayar sai ta koma tunanin dalilinsa na fada mata laifin matarsa. Daga nan za ta gane akwai wata a kasa. Sauran binciken zai nuna mata shi abin yarda ne ko akasin haka.

Wankin da Ayaah bata gama ba kenan. Inda Hasiya take tare da 'yan lallenta taje ta durkusa. Sosai alakarsu tana ta gyaruwa yanzu sai dai duk da haka aure Ayaah take so. Ita dai ta bar gidan ta huta da zugar su Anti Fati kannen mamanta da kuma mitar yayyenta. Sannan ta kula baban nasu ba iya biya mata zai yi ta cigaba da karatu yadda take so ba.

"Anti me za a dora ne? Naga yamma tayi sosai."

Hasiya tayi murmushin jindadi. Canjin da Ayaah tayi yana faranta zuciyarta sosai.

"Kin manta yau Ummita ce a kitchen? Kice tayi mana jallof din shinkafa."

Ta zaro dari uku ta mika mata ta ce a siyo kifi a saka a ciki.

Ayaah ta karba harda godiya ta shiga ciki. Mayafi ta dauko ta tafi ta siyo kifin ko Ummita bata nema ba.

Kifin dari biyu da hamsin ta siyo sai alayyauhu da albasa mai lawashi na hamsin. Sauran kayan bukatar duka akwai a gidan. Albasa ma suna da ita sai da mai lawashin take bukata. Wankesu tayi ta yanka tare da alayyahun ta sake wankewa ta ajiye ya tsane. Ta debo wake yadda take bukata ta dora. Sannan tayi jajjagen kayan miya da citta da tafarnuwa ta soya ta tsayar da ruwan abinci. Kamshin ne yasa Ummita lekowa daga daki. Tun dazu take son fitowa dora girkin ciwon kai ya hana. Ta dauka Murja ce ta gama kitso ta zo taimaka mata sai ganin Ayaah tayi. Wani dadi ya shigeta na canjin kanwar tasu tayi mata gofiya ta koma ciki.

Da ruwa ya tafasa Ayaah ta zuba shinkafa tare da waken da ya soma dahuwa su dahu tare. Sai da ta kusa gama turara bayan ta rage wutar ta zuba lawashin da alayyahu tare da kifin da ta ciccirewa kaya. Yau ma kafin kowa ya farga ta dibarwa Dani sannan ta kwashe sauran. Tayi sa'ar gama komai kafin a fara kiran sallah. Sai ta fake da alwala ta samu ta wanke fuska taje tayi kwaskwarima.

*
Honorable yaga ranar taimakawa na kasa a lokacin da bai zata ba. Da suka bar ma'aikatar su Alh. Bala, gidan Minista Abdulkarim suka wuce. Tamfatsetsen gida wanda ko lokacin da yake ganiyar arzikinsa bai taba tunanin mallakar irinsa ba. An kawo masa abinci mai rai da lafiya ga kuma girmamawa ta musamman daga maigidan. Matarsa tana Abuja da yara shi kadai ya zo ganin iyayensa da magana da Alh. Bala. Wannan yasa masu hidimar gidan su ma suka zage damtse anata kai kawo.

"Naga kamar umarninka kadai suke bi. Don Allah ka ce kada ta zubawa wallahi na koshi."

Furucin Honorable kenan bayan duk abin da yaci kuma aka sake kawo masa farfafesun jelar saniya.

Abdulkarim ya dagawa mai aikin hannu da murmushi a fuskarsa sannan ta fasa zubawa. Kallon Honorable ya yi yana mai kara jin tsoron Allah ta yadda rayuwa take jujjuyawa ga bayi.

"Gani nayi duk ka rame. Don Allah ka sake cin wani abu."

Honorable ya tuntsire da dariya "banda abinka kuma sai aka ce a cin abinci guda zan yi kiba?"

Dariya suka yi tare suka taba hira sannan Honorable ya tashi zai tafi. Abdulkarim ya ce bai san zance ba. Yana son jin me ya faru dashi tsayin lokaci har rayuwa ta koma haka.

Tiryan tiryan ya labarta masa komai. Ba kuma don maula ba sai don dalili guda wanda ya fada masa kamar haka,

"Duniya bata da tabbas Abdulkarim. Ba komai ne yake zama tabbatacce ba a rayuwa. Saboda haka ka daure ka rike gaskiya a duk inda ka sami kanka. Idan duniya ta ciyar da kai gaba fiye da nan sai ka dinga kallon kasa kana kara godiya ga Allah. Bana maka fata amma ko da za ta kawoka inda ta ajiyeni to kada ka karaya da samun rahama. Allah ba Ya dorawa bawa abin da yafi karfinsa. Ba zan boye maka ba da farko na shiga kunci saboda rashin sabo da babu ga Abbas a kwance. Da ilimina na fara hasashen ko auren Hasiya ne ya jaza min talauci. Sai gashi ashe ita za ta rike gidana da 'ya'yana. Duk zafin talauci idan Allah Ya baka mace ta gari to tabbas Ya kwashe maka radadinsa."

"Zan so ganinta. Muje da kaina zan kai ka gida." Cewar Abdulkarim, zantukan suna shigarsa da kyau.

Honorable ya dage baya so. Shi ma Abdulkarim ya dage sai yaje. Daga nan ya tashi ya bi wata hanya zuwa bangarensa. Da envelop ya dawo ya mika masa.

Allah Sarki! Yawun bakinsa ya kafe. Idanuwansa suka kada suka yi ja....a wani shudadden lokaci shi ne yake bawa Abdulkarim. Yau duniya ta nuna masa cewa tables can always turn. (Ya Allah Ka rabamu da talauci da karayar arziki. Duk abin da zai taso mana na kudi Allah Kasa mu fi karfinsa.)

"Duk ni kadai? Basu yi yawa ba?" Ya ce da murya tana rawa. Raba kudin ya yi gida biyu ya mika masa rabi.

Abdulkarim sai yaji wani abu mai nauyi a zuciyarsa. Honorable Habu yafi karfin wulakanci a wurinsa. Laifin kansa ya gani da ya yi sakaci da zumunci har ta kai bai san mawuyacin halin da tsohon ubangidansa yake ciki ba. Ace har ya kai matsayin da dubu dari za ta kawo masa kwalla a ido.

"Kada kayi min haka Honorable. Ban kyauta ba a baya na sani amma ka dauka Allah ne bai shirya haduwarmu ba sai a yanzu da muke sa ran alkhairi ya biyo bayanta."

"Haka ne. Nagode.."

Godiyar ma katseta Abdulkarim ya yi suka fita zuwa mota tare. Wannan karon daga su biyu a bayan mota sai direba. A hanya ne yake tambayarsa irin sana'ar da yake son yi. Lokaci ya ja babu batun komawa siyasa. Idan an manta da mutum sai ya zo da kwakkwara kuma kyakkyawan shiri tafiyar take sake armashi. In ba haka ba kudinsa kawai zai yi asara.

"Zan yi shawara da Hasiya sai na fada maka" Ya ce da murmushi a fuskarsa.

Abdulkarim ya kama dariya sannan ya ce "Allah Yasa bata aurar da duka 'ya'yanta ba ta bani guda. Don naga alama idan na auri rainonta kila sai nayi shugaban kasa."

Honorable ya girgiza kai "abin kuma harda zolaya?"

Abdulkarim bai ce komai ba. Ba kuma zai ce ba har sai yaje gidan ya ga 'yan matan da ya sani a baya tun suna yara. Kudurcewa ya yi a zuciyarsa indai ba rashin tarbiya wanda baya tsammani ya gani ba ko su suce basu son aurensa ba zai nemi guda.

***

Mardiyya da Sauda ne tare da Suhaib da Lilu tsaye a jikin motar Abbati. Sun rako su bakin mota shi da Munzali bayan sun shiga sun gaisa da Mami Khadija. Mama Nasima bata nan kuma Mardiyya sai addu'a take yi su yi su bar gidan kafin ta shigo. Sau biyun da ta zubar da kimarta a gaban Munzali bata yi a gaban yayyenta ba. Ba kuma ta son a fara daga yau.

Hirar motoci suke yi wadda Lilu da Munzali ne karfinta.

Lilu ya shafa motar yana binta da kallon bege
"Ni dai ba don yau za ku tafi ba ai da na dana ko zuwa karshen layinmu ne in kashe arna."

Keyarsa Suhaib ya kwade ya kuma ce idan bai kama kansa ba sai ya fadawa Mami. Mardiyya da Sauda zasu yi dariya ya hade rai zai yi kaza huce kan dami.

"Wai me ma ya fito daku ne? Wurinku suka zo? Ku koma ciki."

Munzali ne ya shigar musu domin Abbati kamar baya wurin. Hankalinsa yana kan hanya yana dakon ganin ta ina Farha za ta bullo.

Da sauri Munzali ya ce "Ya za ka korar min kanne?" Dan nesa kadan da inda suke tsaye ya nuna da hannu yana mai cewa "In ganki mana Diamond girl."

Karashen maganar ya yi ne idanunsa a cikin na Mardiyya. Kawar da kai tayi da sauri gabanta na wata irin faduwa ta daban. Bata san yadda akayi yau take jin Munzali a ranta haka ba. Tun dazu take satar kallonsa sai ta ga shi ma ita yake kallo.

Juyawa tayi za ta gudu saboda kunya Sauda ta rike mata hannu. Shi kuma gogan ya basar kamar ba daga bakinsa maganar ta fito ba. Abbati ma dake son tambayarsu game da Farha amma ya kasa sai da yaji kunyar.
Wato duk yanzu halinsu yake fitowa game da mata da suka hadu da wadanda suke so.

Suhaib ma dai daskarewa ya yi don kusan yafi kanwar tasa jin kunya. Gyaran murya ya dinga yi ba kakkautawa don ya kasa magana. Lilu kuma ya dinga kikkifta idanu na shakiyanci sannan ya ce,

"Diamond dai da na sani mai shegen tsadar nan ka kira Mardiyya?" Hannu ya sakalo a kafadarta ya tako kusa da Munzali dake ta murmushi ya tsaya da ita a gefensa. Hannuwa ya hada kamar mai shirin daukar hoto yana aunosu ta cikin zagayen da yatsunsa suka bayar. Ya dawo kunnenta yayi magana kamar rada amma kowa na ji
"Baby Sis kin matso mana class wallahi." Ya koma ga Munzali " Kai ma Alh. Munzali ka more. Hummm don ma kada ka ce yabon kai da sai in ce duk 'yan matan Kaduna babu kamar na gidanmu."

Hannun Mardiyya ya fara kamawa suka ti musabaha sannan ya saki ya koma kan na Munzali yana faman murmushi gami da nanata kalmar "congratulations."

Suhaib ji ya yi kamar ya daga shi a kafada su bar wurin. Lilu ba ya jin magana ya ce a ransa kafin kuma a zahiri ya biyo shi. Zillewa Lilu ya yi bai bari ya kama shi ba ana ta dariya.

"Baka da kunya ko kadan." Suhaib ya furta yana fuskantar bangaren Abbati. Nauyin Munzali ne ya kama shi saboda a gabansu yake yiwa Mardiyya wani irin kallo. Gashi sun girme shi sosai balle ya yi irin jan idon nan na yayan budurwa.

Abbati kafadar Munzali ya ture da tasa har sai da yasa shi rankwafawa yana mita.
"Munzalin ma ai ba kunyar gare shi ba da ya yi mata magana a gabanmu."

Daure fuska Munzali ya yi cikin wasa yana hadawa da hararar Abbati.

"Ai dama ba ayi maka gwaninta. Sharar fage nayi maka don duk su watse kafin ta fito."

"Wa?" Lilu da Suhaib suka hada baki wurin tambaya.

"Ya Farha" Sauda da Mardiyya suka basu amsa a tare.

Suhaib bai san lokacin da wani irin murmushi mai cike da tsantsar annashuwa ya bayyana akan fuskarsa ba. Farha ce yau da kunnuwansa yaji ance namiji yana jiranta? Ganin murnar na neman yi masa yawa kuma bashi da tabbacin me yake faruwa sai ya ce,

"Yanzu duka nan dama zance ku ka zo ba daukar mota ba?"

Sauda da Lilu har ma da Munzali sai dariya.

"Diamond girl kanwata ce kuma abokiyar shawara ko?" Munzali ya yi magana yana kannewa Mardiyya ido sannan ya dora da cewa "wasu ne dai har a cikin bacci za ka ji suna kiran Ya..."

Bakinsa Abbati ya rufe da hannu su Lilu aka sami nayi sai dariyarsu suke. Munzali na kokarin kwatar kansa Abbati kuma yana faman yi masa alkawura akan idan ya kama bakinsa zai cika masa su.

"Zan tuka motar har Kano!" Ya fadi abin da ya san zai yiwa Munzali dadi.

A take Munzali ya daina kokarin janye hannun Abbatin ya nutsu. Yana sakinsa yasa dariya. Da gaske wautar Abbati bata wani buya lokuta da dama.

"Riba biyu kenan. Kaga dai kowa ya fahimci menene baka son na fada. Alkawari kuma dole ka cika tunda ban fada da bakina ba" Mukullin ya dorawa Abbati a tafin hannu ya yafito Mardiyya da hannu.

"Kina ta sani dibar kunyar Ya Suhaib kuma kin ki zuwa."

*

Gate din gidan aka wangale direban Alh. Tahir ya shigo ciki. Wurin ajiye nasa motocin ya dan yi nisa da inda yake hango 'ya'yansa da wasu baki biyu suna dariya. Motar da ya gani a kusa dasu kuma a bude ce tasa ya gane su waye. Mami Khadija bata tauye masa hakkinsa na maigida ba, ta sanar dashi game dasu tun ranar da suka ajiye motar a gidan.

"Ga sirikinku nan" cewar Lilu yana yin gaba wurin mahaifinsa.

Mardiyya da Sauda ma da sauri suka mara masa baya suna kiran "Abba" tamkar wanda ya yi tafiya. Kafin su karasa ya ware hannuwansa ya rungume kowacce a bari daya. Kirjinsa yaji ya takure saboda rashin Farha. Indai su uku suka zo tarbarsa to ita a bayansa take tsayawa ta riko wuyansa da hannuwanta biyu. Daga nan haka suke raka shi har daki. Wani lokacin ma su taya shi cin abinci. Lilu kuma idan yana gida shi yake dauko masa jaka da wayoyi. Yanzu ma ya dauko harda babbar rigar da ya bari a motar ya ratayota a kafada. Tun tashinsu Suhaib baya zuwa sai suke ganin kamar irin abin nan ne na babban yaya. Farha kuma tunda taga bidiyon nan take kirkirar abin da zai hanata fitowa idan ya dawo ko ya aika a kirata.

Yanayin soyayyar uban da 'ya'yansa ya burge Munzali da Abbati matuka saboda basu tashi a haka ba. Gara ma Abbati ya san nasa mahaifin yana dan kokartawa amma babu zancen wata runguma ko sakin fuska makamanciyar wannan. Duk ranar da suka kwatanta haka karshenta Mal. Sa'idu sai ya tsire masa uba. Shi kuwa Munzali ina ma suka hadu balle a nuna an damu dashi.

"Manyan yayye basa zuwa oyoyo?"

Munzali ne ya tambayi Suhaib amma Abbati ne ya lura da yanayinsa a lokacin da yake bayarda amsa.

"Mu ai mun girma an barwa kanana"

Ba da niyar nuna musu komai ya yi ba amma bakidaya annurin fuskarsa ya bace. Irin kallon da ya yiwa mahaifin nasa ya kawar da kai Abbati ya kasa fassarawa. Kamar kallon tsana, kiyayya ko jin haushi. Kallo mai nuni da cewa akwai wani kwamtaccen abu na bacin rai tsakanin uban da d'ansa. Bai bar tunanin ma ya zauna masa ba ya kawar dashi ta hanyar sakin fuska suka karasa wurinsu shi da Munzali.

Da fara'a ya tarbesu ya kuma dinga jansu da hira. Dama ransa a bace yake daga office amma ganin yaransa kadai ya wanke masa komai. Wata sabuwar ma'aikaciya suka dauka shi ne daga zuwanta ta fara nuna masa alamun tana so su kulla mu'amala. Matsalarsa da Farha ta janyo masa rashin kwanciyar hankalin neman yarinyar duk da ya kwadaitu da ita tun farkon zuwanta. Abin da ya bashi haushi kuwa bai wuce kukan da ta saka masa a office ba bayan ta gaji da dabarunta ya daka mata tsawa ya ce ta fita.

"Amma sauran duk sun ce ba haka kake yi musu ba. Ni me na rasa?"

Wannan magana ta hana shi hadiyar yawu a lokacin saboda dacin da ya taso masa. Sauran da take nufi ba wasu bane illa matan kamfanin nasa da ya nema a baya. Kenan duk kudaden da yake kashe musu da gargadin su rike bakunansu ya tashi a iska. Suna hirar da juna harda yi masa cune...in ba cune ba ta ya akayi yarinyar ta san ta nemi jan ra'ayinsa tunda ba shi ya fara nemanta ba? Har suka iso gida yana tunanin mutum nawa aka fadawa? Mutane nawa ne suke yi masa kallon tsirara mara kima ba tare da ya sani ba?

Farha da baya tsammanin gani a cikinsu ya tambaya Sauda ta fada masa tana gidan Mama.

Ba shi kadai yaji babu dadi ba harda Abbati da suka yi alkawarin haduwa yau.

Alh. Tahir murmushi ya yi ya ce "ta fi ku dokin bikin nan naga alama."

"Abba bata fada maka za ta tafi ba?" Mardiyya ta tambaye shi don tayi mamakin tambayar tasa.

"Yau meeting muka yi tayi amma naga missed calls dinta zan kira."

Sallama ya yiwa su Munzali ya wuce nasa bangaren kafin a kara wata tambayar da za ta fallasa karyar da ya musu. Abbati kam jikinsa ya yi sanyi tunda bata sanar dashi ba kuma ta san zuwan a yau dominta ne. Farha ta fi karfinsa ta kowacce fuska idan ya dubi tarayyarsu. 'Yar masu kudi duk da dai ya san indai don kudi ne ba zai wahala ba. To amma cikakkiyar 'yar boko ce mai tsaftataccen asali. Sirrin rayuwarsa ya sanya bai sami damar jin bacin ran kin fada masa ba. Zuciyarsa dai ta raya masa cewa bashi da wannan matsayin. Tunani ne ya yi masa yawa sai kawai ya yi sallama dasu Suhaib ya shige mota bangaren direba . Munzali dake son magana da Mardiyya sai ya fasa ya ce zai kirata.

"Mutumina kayi hakuri. Karshenta inda taje din ba za ta iya haduwa da kai ba shi yasa bata fada maka bata nan ba ko ta ce ka biyota" Munzali ya fadi a kokarinsa na kwantar masa da hankali bayan ya zauna.

Da sanyin jikin da bai so ko Munzali ya gani ba ya ce "Kar ka damu."

Suna tafiya Suhaib ya tafi wurin Mami Khadija. Albishir ya yi mata don yafi kowa sanin damuwarta akan Farha.

"Amma Mami yarinyar nan don wulakanci sai ta tafi gidan Mama bata fada masa bata nan ba? Wallahi duk yadda yaso boyewa sai da na gane rashin jindadinsa."

"Ai kuwa zan gamu da ita. Ta barmu da damuwa Allah Yasa ba ita take korarsu ba muke tunanin su suke kin zuwa."

Zancen yana da mata da kuma tsoron kada a sami matsala a gaba ta fara yi masa suka shiga wata hirar daban.

A waje kuwa sai da kowa ya tafi sannan Lilu ya nufi dakin Abbansu da kayansa da ya dauko a mota. Tunawa ya yi da katin daurin auren wan abokinsa a dakinsa ya juya. Ya san ba zuwa zai yi ba tunda rana daya ne da na kanin Mami da za ayi a Kano. Duk da haka amintarsa da abokin nasa tasa yana son Abban nasa ya sani kuma ya kira baban angon ya masa fatan alkhairi.

Akan gadonsa ya ajiye kayan Alh. Tahir ya bude durowar gaban madubi ya dauko envelop din katin. Jakar office din ya fara dauka sannan wayoyin. Ya dago babbar rigar biruka da wallet suka fado daga aljihun jakar. Guntun tsaki ya yi na bata lokaci

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login