Showing 96001 words to 99000 words out of 242549 words
tashar."
Mami Khadija ta fada musu bayan sun fito. Ita da Sauda suka wuce bangaren Mama Nasima. Abbati ya dubi Munzali da mamakin baro mara lafiya. Sai da yaji ciwon karya ne ya dan yi murmushi. Ta kusa dasu Farha ta zo ta wuce ta nufi motarta. Ko kallon inda suke bata yi ba sai faduwar gabanta da ya tsananta da tazo giftawa ta gefensu. Munzali ne ya yi karfin halin kiran sunanta yadda Abbati yake fada da zolaya.
"Barka da rana Ya Farha."
Watsa masa wata muguwar hararar da ita kanta bata ma san ta iya ba tayi. Abbati yana lura da duk wani motsinta. Bakinta ta dan turo kamar za ta yi magana, maganar da alamu sun nuna a tsiwace za ta fito. Sai kuma kawai ta wuce zuciyarta na dokawa da sauri da sauri.
Wani irin abu take ji game da Abbati da yafi karfin tunaninta. Ya kuma sanya jin yana da aure yi mata nauyi. Me yasa basu fada mata tun farko ba ta shirya zuciyarta? Allah Ya sani indai wannan abin da take ji shi ne so to kuwa ba kankani take yiwa Abbati ba. Gara ta kama kanta haka nan...karshenta ma matar ba daya bace. Ko yaransa nawa? Saurin girgiza kai tayi da ta fahimci inda tunaninta ya nausa bayan ta zauna a motar. Tayarwa tayi tayi ribas tana cin taya. A guje ta fice daga gidan ko tunanin na bayanta bata yi ba...
'Ina tunaninsa mana.'
' Idan na bace musu ai dole ya kirani.'
'Sai in rama nima.'
'Me za ki rama?'
'Da me za ki rama?'
Zantukan zuciyarta kenan lokacin da ta daidaita akan titi.
Tana zama a motar dama Abbati ya karbe mukullin daga hannun Munzali ya shiga mazaunin direba shi ma ya fizgi motar don kada ta bace masa.
Dariyar mugunta Munzali ya fashe da ita "Mutumina kana ruwa, a bulallen kwale-kwale, kusa da mayunwaciyar kadar da 'ya'yanta suka bata. Hodijan inji Fillo. Farha tayi fushi amma kuma naji dadi."
Abbati ya galla masa harara "ko baka fada ba na san kaji dadi mana. Ji wannan fara'a da kake yi kamar ka tsinci hakori."
Dariya ya bashi saboda kana ganinsa ka san yana tare da damuwa. Abu ne goma da ashirin, bai san ta ina zai fara ba.
"Dariya ma kake yi ko Munzali?"
"Wai kuka zaka yi ne duk ka bi ka bata rai?"
Kwafa Abbati ya yi yana dana sanin karbar tukin. Banda tsoron kada Farha ta bace masa da tuni ya kaiwa Munzali duka. Wata kwafar ya sake Munzali ya ce,
"Wallahi in ka tabani sai nayi kararka wurin Farha. Na san wannan cije leben ba zai wuce lissafin yadda za ka taba lafiyata bane idan mun tsaya. Banda haka da tuni ka fahimci nasarar dake tattare da fushin Ya Farha" ya kare maganar da zolaya.
Cike da rashin yarda Abbati ya ce "Nasara?"
"Nasara mana. Mutumina me yake saurin batawa mata rai idan suna son namiji?"
"Zancen kishiya."
"To ana kishin abin da ba a so ne?"
Kyakkyawan murmushi ne ya bayyana akan fuskar Abbati a take. Me yasa bai yi wannan tunanin ba? Munzali ya yi ta tsokanarsa har suka yi parking a gefen Farha.
Tun kafin motarsu ta tsaya take hango fuskokinsu suna dariya. Wani abu ya zo ya tokare mata wuya yaki sauka. Kishi ne wanda bata san daga ina yake tasowa ba. Gefe da gefe motocinsu suke. Sai ya zamana idan suka bude kofa ita da Abbati zasu gogi bayan motar juna. Yana sane ya matseta a wurin gashi daya barin ma akwai mota.
"Ka matsa zan tafi." Ta furta lokacin da ta harare shi.
Murmushi ya yi mata. Murmushinsa mai kyau ya ce "Idan ki ka tafi b'ata zan yi a hanyar komawa."
Har cikin ranta taji murmushin nan. Sai dai kishin ya ci galaba a kanta domin ya saka ta fadin abin da taji kunyar amsarsa
"Dariyarku ta kai ku gida."
Taji haushi ashe. Munzali kuwa me zai yi banda dariya.
Tana kallo Abbati ya harare shi kwatankwacin yadda tayi. Sadda kai tayi kasa don saura kiris ya saka ta dariya.
"Mugu, ka ce min inyi murna kishina take yi. Gashi ka sa na kuma bata mata rai. Ni wallahi da zuciya daya na damu da kai. Ko a mafarki ba zan baka gurguwar shawara ba."
Ba shiri Farha ta kawar da kanta gefe ta danne dariyarta.
"Ya Farha ki juyo don Allah."
Girgiza kai tayi don ba za ta iya kallonsa ba tare da tayi dariyar ba.
"Fita ka bata hakuri mana" cewar Abbati yana budewa Munzali kofa, duk hankalinsa ya tashi "harda wani cewa wanda ake so ake kishi."
Farha na jin abin da ya fada ta juyo da sauri suka hada ido. Bude nata tayi yadda ta saba yaji kamar ana fizgarsa cikin idanun. Kafin ya farga ta lumshe nata tana murmushi.
Shi ma murmushin ya yi har zuciyarsa yana jin wata irin nutsuwa.
"Ya Farha ki tausaya min mana. Fushin nan na kishin ne ko na gaske?"
Munzali ta kalla yana tsaye tsakanin motocin biyu. Kallonsu yake suna burge shi. Abbatinsa ya sami mata in sha Allahu.
"Ka ce masa ya bar ta a ciki?" Ta furta a hankali.
Sannu a hankali Abbati yaji kamar zuciyarsa ta kara girma saboda jindadi.
"Za ki jiramu?" Ya tambayeta bayan ya fito.
"Zan jira."
Sai da suka yiwa juna murmushi sannan ya juya. Munzali ya dawo jikin tagarta ta daya barin.
"Farha.." ya kira sunanta a nutse.
Waigawa tayi har taji kunyar kila ya kula da kallon Abbati da ya shiga tashar da take yi.
"Don Allah ki so Abbati. Ban san ko kina da wasu samarin ba amma da wahala ki sami mai sonki kamar shi. Tunda ya ganki na daina gane kansa. Mutumin kirki ne. Idan zan fara fada miki karuwar da nayi da zama dashi sai mun bata lokaci a wurin nan."
"Dadin baki ya ce ka zauna yi min?" Ta tsokane shi.
Yadda tayi sosai ya sake burge shi.
"Kut...wallahi kun dace! Bakinsa baya mutuwa shi ma amma a zuci saukin kansa har ya kusa yi masa yawa. Sau nawa ina masa wayo bai gane ba.." ya ce yana dariya.
"Ai kuwa ka daina daga yau..."
"Dalili?"
"Zan tare masa."
Farinciki ya mamaye Munzali. Burinsa ya cika. Abbati ya sami Farha.
Hannu ya saka a kasan habarsa ya kalli gate din tashar da Farha lokaci guda ya kada kai
"Wallahi kun dace. Sosai, sosai, sosai. Mungode Ya Farhan Abbati."
*
Nambar da aka kira shi Abbati yake nema zai tambayi inda Hanne take kamar an ce ya kalli hagunsa, ya hangota zaune akan benci. Hannunta tasa tana bubbuga kanta yadda ta kanyi a gida idan amosaninta ya dameta da kaikayi. Yana bata kudin zuwa salon amma don bakin hali, kamar wadda take cikin rashi sai ta soke abinta. Shampoo ma idan ya siyo ba ya sanin inda yake tafiya. Kan dai kullum dankare da amosani. Makotansu inda take zuwa kitso, tayi fada da matar duk akan tayi mata maganar neman maganin amosani. Ga gashin himili guda da tsaho da cika amma gyara sai taga dama. Da ya gaji da magana ne ya yi mata rantsuwar idan ta sake yin susa a gabansa sai ya aske shi. Shi ne ta koma bubbugawa har ta saba.
Mayafinta yana kafada. Daurinta bai rufe tsofaffin jelunan gashinta ba. A kusa da ita namiji ne yake cin abinci daga shi sai gajeren wando. Rabin cinyarsa ma a waje yake daf da jikinta. Gashi da cibiri-cibirin gashin kai mara kyawun gani. Sauran mutum biyun dake daga barin duka mata ne amma suna cin abinci ana buga shewa.
Gabansa ne ya fadi. Zuciyarsa ta tsinke har yaji kamar ya karasa ya dauketa da mari. Matsalolin Hanne suna da yawa. Ba zai taba yarda wai tashi a kauye da rashin wayewa ne suke damunta ba. Ya yi mata duk abin da ya dace domin ta gyara rayuwarta a matsayinta na mace. Da 'Yashshafa ce ta sami rabi-rabin abin da ta samu ya tabbata sai an ga canji. Duk da haka a yau dai abu daya ne ya tsaya masa a rai. Kazamar rayuwarsa ce ta gifta ta gaban kwakwalwa da zuciyarsa. Da sauri ya ja istigfari yana fesar da numfashi. Matsanancin tsoro ya mamaye zuciyarsa a lokacin da ya tuna cewa ba don rashin lafiyar da ya yi ba kila da yanzu ya koma inda yake son bari. Da bai je ba sai Allah Ya musanya masa da samun mallakar zuciyar abar sonsa. Wani abu da bai hango faruwarsa nan kusa ba in ma yana da rabo.
Hango shi Hanne tayi ya nufo inda take ta tashi da sauri. Jikinta har rawa yake saboda tsabar masifar dake cin ranta. Tsayuwa tayi a gabansa ta sanya hannuwanta a kugu tana girgiza.
" Ina 'Yashshafan take? Hmmm, wallahi kada ma ta gwadani don ba mutumci ne gareni ba."
Abbati kam sai da ya daure zuciyarsa sosai ya iya cewa "su waye suke binki bashi a nan?"
Shekeke ta kalle shi a zuwan ya ma raina mata wayo
"Auuuu, wai nan bagarar dani zaka yi don na barta? To Yasin uban kuturu ma ya yi kadan. Kowa yaci tuwo da ni miya ya sha wallahi tallahi"
Mutane har sun soma kallonsu ya jinjina kai cikin son ya hadiye fushinsa.
"Nine kuturun kenan, mahaifina kuma bai isa ba?"
Fahimtar katobararta tayi sai ta kama bakinta ta tsuke. Mutumin da ya kira shi a waya ya taso da ya ga ta tsaya dashi. Kudinsa ya fada da na mai abinci duka Abbati ya basu sannan suka kamo hanyar fita daga tashar.
Munzali da Farha suna can suna hira kamar sun saba. Dama ya fi Abbati saurin jan mutane. A haka ya gane Farha ma ba baya ba. She is very friendly ga iya magana.
"Yanzu nan gaba kuma idan ya hadu da wata, haka za ka tsaya kana wasa shi a gabanta ko?"
"Ba fa zan gaji da cewa kun dace ba. Wato nan bugun cikina za ki yi ki ji ko akwai wata. Abbati ake yiwa wannan wayon ba ni ba."
"Shi ma din ai ka gama yi masa wayon daga yau."
"Na yarda fa. Amma ki kwantar da hankalinki. Daga ke babu kari."
Mahaifinta ta tuno taji kunci na neman rufe farincikinta. Karin aure ba shi bane matsalarta. Munzali da ya kula da fuskarta sai ya ce,
"Matarsa ma bata da matsala, in sha Allahu zaku zauna lafiya."
Tunda yake bai taba jin Abbati ya zagi Hanne ba shi ma ba zai fara ba a bayan idonsa. Yana dai kawo masa korafi idan abu ya ishe shi amma iyakarta kenan.
Ita ta fara hango su saboda tana fuskantar gate din tashar. Gabanta faduwa ya yi taji ta karaya. Yau dai bata shirya ganin matarsa ba. Kuma bata ga dacewar su hadu a tasha ba. Munzali da ya bada baya kuwa sai hira yake mata yana jingine da tasu motar.
"Zan yi gaba kafin su karaso in jira ku a can" ta nuna titin da yake kallonsu wanda shi zasu bi su koma.
"Ba za ki jira ku gaisa ba?"
"Idan munje gida sai mu gaisa." Ta amsa a hankali. So take kawai ta bar wurin kafin su iso.
Abbati yana tunanin da kalmar da zai gabatar dasu da juna kawai ya ga motarta tayi ribas kuma ko ta juya ta kallesu. Numfashi ya sauke ya mikawa Munzali mukulli. Shi ma bai tambaye shi dalili ba saboda yana iya ganin damuwa da bacin rai shimfide a fuskarsa.
"Ka kora su 'Yashshafan ne?" Hanne ta tambayi Abbati da dan hope dinta.
" 'Yashshafa zan kora ko su 'Yashshafa? Ita mutum daya ce. Su kuma yana nufin harda surukarki wadda ta tsuguna ta haifeni."
Gefe ta muskuta saboda kunyar da ta sake ji sai tayi shiru. Lokaci lokaci take yin tsaki ko tayi kwafa cikin bacin rai. Mai rabata da 'Yashshafa yau sai ya shirya.
Da shirun ya gagara tana gudun zuciyarta kar ta fashe ita daya sai ta soma surutai
"Wai ni za a yiwa bariki? Hmmm. Har tayi girman sanin kissa? Yarinyar da a gabana ta fara kirgar dangi..."
Fadan da baya son yi ya hau ta dashi. Don wata tsawa da ya yi mata sai da ta kusa sakin fitsari a zaune.
"Hanne!!!" Ya kira sunanta da karfi da kuma alamun gargadi. Ko kula da yadda take zazzaro idanu bai yi ba ya cigaba da yi mata masifa
"Wallahi zan fasa miki baki kuma na mayar dake tashar ki koma Kano. Kin sha burkutu ne da za ki shigo mota kina yi min wannan haukan? Ya dace kiyi magana irin wannan a gaban Munzali?"
Girgiza kai tayi da sauri.
"Bude baki za ki kiyi min magana. Nace ya dace?"
"Bai dace ba" Hanne ta bashi amsa baki na rawa. Bata zata zai tanka ba tunda ta saba debo shirmen haukanta tana yi baya kulawa.
Duk abin da suke yi Munzali bai tanka ba. In da akwai wurin da suka shatawa juna layi duk da basu furta da baki ba to zamantakewarsu da matansu ce. Suna kaiwa juna korafi da neman shawara. Amma babu zaman zubarwa matan da mutumci. Ko babu komai dukkaninsu 'yan uwansu na jini suka aura. Yanzu ma parking ya yi ya fita daga motar. Farha bata kula sun daina binta ba don tunda ta ga ba Abbati ke tukin ba ta daina kallon motar ta madubi.
"Yanzu me nayi da har za ka ci mutumcina a gaban Munzali? Saboda Allah a dakeni a hanani kuka?"
"Ni ne ma na zubar miki da mutumcin Hanne? Yau ko ciki daya muka fito da Munzali ya dace ki dinga zancen kirgar nono a gabansa?"
"Kirgar dangi na ce."
"Kar kisa in zageki Hanne. Ko kirgar kindirmo ne ai ya san me kike nufi. Wannan shirmen ne ya kawoki dama ba duba mijinki ba?"
"Sannu ya jikin?" Ta ce a sakarce.
Madadin ya amsa sai ya ce "tsabar kishinki na banza ya saka ki fitowa ko kaya babu? Da ba yau zamu koma ba haka za ki zauna?"
Gefen kafafunta ta hau lalube tana cewa "Da kayana. Na taho da kaya." Sai ta dafe kai "washhh, Yasin suna shagon mai shinkafar nan."
Yi mata magana ma bata lokaci ne. Fada ko duka asarar energy. Fita kawai ya yi ya fadawa Munzali ta baro kayanta.
"Ku wuce can zan koma tashar na dauko. Tafiyar tamu kamar da wuya dai a yau. Bana son fitar yamma bare ta dare."
"Ba ayi haka ba."
Munzali ya ce da Abbati. A dalilin Hanne tayi tafiya ya dace ya kaita ta dan huta kafin su kuma daukar hanya. Sannan suna bukatar yin magana a junanau. Wanda ya kira Abbati akan bashin da Hanne ta ci suka sake kira aka kwatanta masa jakar. Suka yi masa alkawarin dubu biyar idan babu abin da ya salwanta ciki sannan suka rabu. Munzali ya koma tashar, Abbati ya wuce gidan Alh. Tahir da Hanne. Su biyun sun gane hanyar a bi daya tak.
***
Fafur Mardiyya taki zuwa asibiti saboda ciwon karya ne. Ta dai nuna taji sauki. Sai da Mami Khadija ta fita daga dakin sannan Mardiyya ta yiwa Sauda bayanin abin da ya faru.
Dundu ta yi mata a baya "Amma dai baki kyauta ba, baki ga yadda hankalin Mama ya tashi ba."
"Haka shi ma ya ce."
Da shakiyanci Sauda ta ce "Shi? Har kin fara ce masa shi? Lallai Abba ya fara tari auta ta isa aure."
"Ba fa haka bane. Kinga babba ne. Bai dace na kira sunansa kai tsaye ba." Mardiyya ta ce da nufin kare kanta.
"Hakkun. Ladabi da biyayya akwai dadi."
Shan kunu tayi don tsokanar Sauda bata karewa. Idan ta saka mutum a gaba sai ya kusa kuka.
"Bana so...abokan shawara kawai ya ce mu zama kar ma ki fassara."
"Hakka!" Ta ce bayan ta tashi tsaye tana dariya "su abota manya."
Tsokanar da take gudu Sauda ta sami kofar yi har sai da ta nuna kamar ranta bai baci ba. Sannan ne Saudan ta turawa Farha text wadda a lokacin suka isa tashar ta fada mata Mardiyya kalau take. Sauran bayani sai ta dawo.
*
Lilu ne ya tuko motar Suhaib, shi kuma ta Abbati wadda take asibiti suka dawo gidan tare. Wurin parking suka nufa kowa ya daidaita motar da yake ciki bisa tsari.
Kafin shigowarsu Baaba Mari ta dinga jin kamar suna takurawa masu gidan. Sun zauna jiran su Abbati batare da sanin ko masu gidan suna da uzuri ba. Dadin dad'awa ga an ce 'yar gidan babu lafiya. Babu alamun canjin fuska ko kadan a tattare da matar gidan amma da yake bata saba ba sai take jinta a takure. Ga Deluwa da 'Yashshafa sai kai hannu suke cikin tray din snacks suna dauki daidai.
"Kiyi hakuri mun zo mun dora miki dawainiya."
Mami Khadija ta sake fadada fara'arta
"Me ya kawo wannan magana? Ni wallahi baki ji yadda nayi farincikin zuwanku ba. A haka fa ake kulla zumunci kiga har 'ya'ya."
Baaba Mari sai dariya "kayya Hajiya. Mu fa 'yan kauye ne. 'Yan birni suna zuwa kauye?"
"Har kinsa naji babu dadi. Muma ai zama ne ya kawo mu nan amma silar kakaninmu kauyen ne. Mu 'yan Soba ne kuma har yanzu muna ziyartar dangi a can. Garinmu a karkashin Kaduna yake."
Uwar azarbabi Hajiya Deluwa mai hangen surukuta za ta hadata da Mami tayi saurin shiga hirar.
"Mu kuma daga Kirikasamma muke. Amma ita Mari aure ne ya kawota. Ita 'yar Maigatari ce."
Baaba Mari bata gwasaleta ba. Hirar sai ta tafi su uku. Deluwa ta rasa inda za ta saka kanta don murna. Da mace mai aji irin Mami Khadija take hira. Takaicinta ma na rashin bude kwanukan abincin da Baaba Mari bata bada fuskar yi ba ya yi sauki. Sai kayan fulawa suke ta gabza.
Mami Khadija ce ta sake komawa bangaren Mama Nasima tunda bata san ciwon karya bane. Ta damu da Mardiyya kamar yadda ta damu da nata 'ya'yan. Da ta dawo Baaba Mari ta ce ta kaisu su gaishe da marar lafiyar. Mami Khadija kuwa taji dadin kyawun tunanin Baaba Mari. Su biyu suka bi ta. 'Yashshafa anyi gamo da samosa ta kasa hakura ta bisu. Tun dazu Deluwa take yi mata inkiya da hannu akan ta barshi haka don ita ma ta ci amma taki. Sai da suka fita taji falon ya yi tsit sai karar AC. Ita kadai ta firgita kanta da muggab tunani.
"Wannan shuuuuuu haka kamar wucewar fatalwa?" ta ce da rawar baki.
Guntuwar samosar hannunta ta ajiye ta tashi a hankali ta sulale waje. Da baya da baya take tafiya tana kiran Deluwa a tsorace.
*
Kai tsaye Lilu ya danno kai bangaren Mami Khadija sai ganin yarinya ya