Showing 126001 words to 129000 words out of 242549 words
sark...."
"UWANI!"
Hadiye sauran maganarta tayi ba shiri saboda karfin tsawar da ya daka mata.
"Ki dauko mayafinki yanzun nan ina jiranki a mota."
Bata gama dawowa daidai daga firgicin da ta shiga ba Mubashir ya kirata. Saurin dawo da nutsuwarta daga tunanin me ya sami Salihi tayi ta amsa wayar.
"Umma gamu a bakin gate amma KNUPDA sun yi alamar a dakatar da aiki a gidan."
Kwakwalwarta ce ta toshe na 'yan dakiku ta dinga maimaitawa Mubashir tambaya daya kamar mai bitar karatu.
"Su waye kuma KNUPDA?"
***
Farha bata dago da kanta ba har Abbati ya gama fada mata asalinsa da musabbabin zuwansa Kano. Labarin nasa ya sami sauyi ne a wurin silar arzikinsa inda ya ce mata kasuwanci suke yi amma yanzu sun balle daga jikin ubangidan nasu. Ya fada mata unguwar da suke ginin shopping mall da ire iren kayayyakin da suke son zubawa a ciki.
A lokacin da yazo gabar da dole karya ce kadai za ta iya rufa masa asiri sai da ya hadiyi yawu mai daci. Da kansa yake jin tsana da kyamar dabi'ar da suka rayu cikinta. Yana son Farha so mai girma. Burinsa idan har ya mallaketa su zamewa juna tamkar warin takalma masu cike junansu. Yadda bashi da sirri da Munzali yana fatan kusancinsa da ita yafi wannan. Ba don komai ba kuwa face sanin cewa duk matsayin aboki matar aure ta fishi. Ita da mijinta aminai ne, masoya kuma ma'aurata.
Kimanin minti uku da yin shirunsa amma har lokacin bata dago kanta ba. Tuni ya fara sarewa yana jin ya rasata kenan har abada. Magana mai girma irin wannan ya so ace a gida aka yita. Sai dai kuma tazo masa bagatatan ne da Farha tayi masa tambayar cikin hirarsu.
"Don Allah ki dago kan ki ko sallamata zaki yi kada ki ce ba za ki sake iya kallon wannan almajirin dan kauyen wanda ko kwalin primary bai mallaka ba." Muryarsa ce tayi wani irin rauni mai fallasa ruhi da zuciya tana raurawa saboda tasirin soyayyarta a zuciyarsa. Bai gaji ba ya sake yi mata magana domin ya kagara ya san matsayinsa duk da ya gama sallamawa.
"Ni ba tsaran aurenki bane Ya Farha, amma wallahi ina sonki da dukkan zuciyata."
Farha bata san yadda zata kwatanta halin da Abbati ya jefa zuciyarta ba da kalamansa na karshe. Zuciyarta kara fadi take a cikin kirjinta tana kuma cikewa da wannan bawan Allah dake gabanta.
Kosawa ya yi da rudanin da zuciyarsa ta shiga a sakamakon shirunta.
"Ko in tafi?"
Sai lokacin ta dago da taji ya dan tura kujerarsa baya alamun zai tashi.
"Idan ka tafi kana tunanin tsaran auren nawa zai zo?" Ta ce a raunane.
Kansa ya gyada da murmushin da ya tsaya a labbansa. Wurin kawai yake son ya bari kafin ya tsinci kansa a kan gwiwoyinsa yana rokon soyayya.
Hawaye ne ya zubo mata ba shiri da ta hada ido dashi. Wannan wace irin zazzafar soyayyace suke yiwa juna haka? Da jikakkun idanunta ta dube shi.
"Yazo ya aureni kana ji kana gani?"
"Kin yarda idan yazo na kore shi ko waye?"
Ita ma kai ta gyada masa amma nata murmushin mai sauti ne da jindadi.
"Kina ganin su Mami zasu yarda ki aureni?" Ya tambayeta da sabuwar damuwa.
"In sha Allahu babu matsala."
Gyara zamansa ya yi gami da sakin ajiyar zuciya. Suka kalli juna suka yi murmushi a tare. Abbati ya kasa dauke ido daga kan kyakkyawar fuskarta.
"Kin san me?"
"Ina dai so in sani" ta lumshe idanunta sannan ta bashi amsa.
"Na dan kware a Ingilishi."
Farha bata san lokacin da ta kama dariya ba.
"To ko mu kara ne?"
"Me ya yi zafi daga wasa"
Dariya suka yi tare a idanun Mami Khadija wadda ta zo wucewa can nesa dasu da kawayenta. Murmushi tayi ta dauke kanta kafin su farga cewa ta gansu. Fatanta Allah Ya cikawa 'ya'yanta farincikinsu.
A zuciyar Abbati kuwa tunani yake kada Allah Ya kawo abin da zai raba shi da Farha. Shi kan shi tsoron girman soyayyar da yake yi mata yake yi. Idan ya rasa ta......baya son sanin halin da zai shiga idan ya rasa ta.
*
Can daya bangaren inda Munzali da Mardiyya suka zauna suma tasu hirar suke gwanin sha'awa. Hirar irin son da Abbati yake yiwa Farha yake mata tana bashi amsa da tabbacin yayarta ita ma tana kaunar aminin nasa.
"Da gaske dai ba sona kike ba ko Mardiyya?"
Ya furta daga sama suna tsakar magana. Gabanta ne ya fadi domin tun haduwarsu bai taba kiranta da sunanta ba. Kallon ma kamar tayi masa laifi haka ya tsareta da idanu duk sai ta daburce.
"Me nayi don Allah?"
Yanayin tsoratar da tayi sha'awa ya bashi. Yarintarta ta fito sosai sai kara shiga zuciyarsa take yi.
"Tunda muka zauna nake yi miki zancen su Abbati amma ko ki bata rai ki ce a canja hira. Kamata ya yi nima naci ribar lokacin nan nayi miki hirar zuciyarta da yadda take kaunarki."
Sunkuyar da kai tayi tana wasa da wayar hannunta. A haduwarsu da yawan wayarsu ta gane Munzali yana da son wasa da tsokana. Wannan ma yana daga cikin abubuwan da suka sa take son sa.
"Baki ce komai ba."
Mardiyya sai ta zabi ta rama ita ma ta nuna masa wace ce ita.
"To ni me zan ce? Ka kebe 'yar karamar yarinya kana yi mata zancen soyayya."
Dariya sosai ya dinga yi yana bude baki ya rufe kafin ya ce "kin ce wani abu. Wato yarinya ko? Bari na tashi na nemi daidai dani a cikin taron nan"
Hannuwanta ta daga kamar mai addu'a da ya mike ta soma cewa "Allahumma..."
Tsayuwa ya yi yana kallonta cikin wani irin yanayi mai kashe jiki "karasa mana."
Sai ta daure fuska ta cigaba
"Allah Kasa duk wadda Daddyn Qibdiyya ya gani ya yiwa magana ta ce an kawo kudin aurenta."
"Diamond girl" ya ce yana dariya sosai "I love you."
A guje ta tashi ta bar wurin har tana tuntube da kujera akan hanya.
Munzali ya dinga murmushi yana mai mamakin yadda zukatansu suka zama mallakin yaya da kanwarta lokaci guda.
*
Filin rawa Lilu yaje ya yi abarsa son rai ya dawo inda Sauda take tare da Qibdiyya. Yarinyar ta sake abinta tana ta yi musu hira. Tana ganin Lilu ta gudu wurinsa. Sauda ta ce.
"Baban yara ita ma ka sayeta kenan"
Ranar har su Abbati suka tashi tafiya Qibdiyya tana hannun Lilu. Kowa sai da ya shaida yadda tasu tazo daya daga haduwa. Da ya zo sakata a mota shi da iyayen nata babu wanda ya kula cewa kiss ta so yi masa a baki. Dama ce bata samu ba saboda tana yunkurowa ya sauketa a jikin Abbati.
Kuruciya bata barta ta dauke shi komai ba. Uncle Daddy ne kadai yake yi mata. Sai kuma mutanen cikin ire iren bidiyo da yake kunna mata ya ce tayi masa abin da ta gani. Ta fanin kallo Zakiyya tana matular kokari don ko fim ta daina kallo a gaban 'yarta saboda kaifin basirar yarinyar. Shi yasa bata da aiki sai karatun waya. Sakacinta a bangaren saka ido ne a cikin gida. A zatonta tunda suka fito ciki daya da Daddy ba zai taba cutar da ita ba balle 'yarta.
(Ya ke UWA mai dimbin daraja da martaba. Ba a ce ki sanya zargi da kokonto a tsakanin mu'amalar 'ya'yanki da 'yan uwanki ba. Nagari masu sonmu da gaskiya sun ninka shaidanun. Yana da kyau amma ki kula da irin shakuwarsu ko tsoronsu da yara ke ji. Idan tayi yawa to wajibi ki bi abin cikin laluma ki gano musabbabinsa. Ita alakar da aka gina da taba jikin juna a waje tana da wuyar bari. Shi yasa ma yaran da ake yiwa fyade ko koya musu mummunar dabi'a ake samun wahalar hanasu. Sai kin dinke baraka tsakaninsu da mai koya musu sai suje suna nema a wurin wasu da kansu. ZINA MASIFA CE GA BABBA DA YARO! Rabuwa da ita sai an dage sosai.)
***
KIRIKASAMMA
Dakin Baaba Mari babu haske sosai saboda ta gama shirin bacci. A kwance take tana ta juye juye akan gado. Jikarta ta wajen Atine da suke kwana tare sai munshari take abinta. Gajiya tayi da tunanin da ya addabeta ta tashi za ta dauro alwala kamar yadda aka koyar dasu a islamiyya. Babu wani abu da ya gagari addu'a, musamman a hada da qiyamul laili.
Alwala taje ta dauro a bandakinta wanda Abbati ya yi mata a falo. Da yake fitilar chaji ta kunna tana iya hango tsakar gidansu sosai. Maigidanta ne har yanzu shadaya da kwata na dare zaune tare da Mal. Sa'adu wanda ya yi uwa ya yi makarb'iya akan bakon da suka yini dashi. Su uku har bakon hira suke suna dariyar wani abu da ya fada.
Daki ta wuce ta dauki hijabi da abin sallah. Komai a sanyaye take yi saboda wani kwantacwn abu da bata san a ina yake ba yana fada mata akwai matsala. Ko Munzali bai taba zuwa Kirikasamma shi kadai ba. To me zai sa 'yan satittika da nad'in sarautar Abbati shi wannan Shazalin ya dawo?
I just published "27" of my story "UWA UWACE...". https://www.wattpad.com/1029251873?utm_source=android&utm_medium=com.whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=BatulMamman17&wp_originator=A%2FjBKEA%2FIPJkMQcFon9sHPKf%2BYzihwobswtFyypgUAcyHfG1WzcO47tsfx%2F1d5kzPijXW4%2BSo5KkOcwf5xJ%2BR4xf0WysWT1dYqEA%2BVvMqaK%2FRzw%2BmqlRdh6rqVmac01t
UWA UWACE...27
Batul Mamman💖
***
Gari ya waye, rana ta fito tun karfe shida da rabi. Zuwa goma na safiyar Asabar jama'ar dake waje har sun fara jin zafinta. Sai dai wannan zafin ba zai hana masu uzuri a waje fita su gabatar dashi ba. Kamar kowacce rana ga dan Adam, ita ma wannan Asabar ta zo a matsayin ranar kuka, farinciki, dariya, bakinciki, fargaba, alhini da kowane irin yanayi da mutane ke tsintar kawunansu.
A safiyar wannan Asabar din ne Uwani ta amsa wayar Mubashir mai tafe da mummunan labari akan gininta.
A ranar ne kuma Shazali ya wayi gari a Kirikasamma bayan ziyarar bazata da ya kaiwa gidansu Abbati.
Ita ce kuma ranar da Hasiya ta zaba domin kai wa Salima kukanta akan saurayin Ayaah.
Duka dai kuma a wannan ranar ne Abbati da Munzali suka je daurin auren kanin Mami Khadija bayan dinner din da suka je ranar Juma'a da daddare. Dinner din da basu baro ba sai da suka tabbatar an sami musayar zukata tsakaninsu da 'ya'yan Alh. Tahir guda biyu.
***
Ana kiraye kirayen sallar Magariba Shazali ya isa Kirikasamma. Girkin abokiyar zaman Baaba Mari ne. Tana jin an ce abokin Abbati ne ta fito daga rumfar da suke girki tana fadin maganganu. Ciki har tana cewa
"Ban san da zuwan bako ba saboda haka ban girka dashi ba."
Baaba Mari ko tari bata yi ba har ta juya ta tafi. Bakinciki da hassada ba bakon abu bane gareta daga wurin kishiyar dake morar arzikin Abbati. Niyarta idan an kawo mata nata abincin ta bashi. Sai gashi an hada masa gara guda daga bangaren Mal. Sa'adu. Atine da Habi su ma ba a barsu a baya ba saboda kada mahaifiyarsu ta wahala. Kowacce ta aiko da abinci.
Ashe kusan karfin girkin ma 'Yashshafa ce tayi. Deluwa ta rasa inda za ta saka ranta domin a burge wannan bako. Mahaukaciyar motar da yazo da ita kadai ta ishi bawa shiga rudani. Akan Shazali ita mai iya hakura da Sha'aib ce kamar yadda take kiransa.
Kafin lokacin kwanciya baccin da Baaba Mari ta kasa runtsawa Mal. Inuwa ya shigo dakinta. K'aidarsa ce zaga matansa da asuba da kuma bayan Isha. Da murna ya shigo mata yana yabawa baiwar dansu wanda har masu kudi ke ziyartar iyayensa.
"Idan aka kirani da Uban Abbati sai naji duk garin nan babu ya ni. Dubi dai ace mutum mai arziki kamar wannan ne a gidanmu..."
Kula ya yi hankalinta ba ya gare shi ya bata rai.
"To yanzu kuma me ya faru? Tunane tunanenki na banza akan arzikin danki ne ya sake dawowa?"
Murmushin yake tayi tare da kawar da kai domin ko za ta kwana tana bayani baya taba fahimta.
"Malam kenan."
Komawa ya yi ya zauna yana dubanta cikin yanayin da yaki jinin ganinta.
"Ki fadi damuwarki tunda nayi imanin akwai. Yau da ace ba Inna Mairo ce ta karbi haihuwar dan nan ba sai ince ba naki bane shi yasa kike gwada masa halin matar uba ko dan riko. Ni ko da wasa ban taba jin uwar da take yiwa dan cikinta bakincikin samun arziki ba sai ke Mari."
"Har yanzu kana ganin laifina don na damu da son sanin silar kudin da mu da danginmu muke ci? Daga zuwa almajiranci sai kudi kamar suna zuba daga sama?"
Ransa ya soma baci amma ya danne domin baya son rigima a daren nan.
"To meye a ciki? Arziki ba na Allah bane? Kuma yana baiwa wanda ya so bi ghairi hisaba. 'Yan kasuwa nawa ne suka fara a matakin da yafi bara kaskanci amma yanzu sun wuce sa'a?"
"Cikinsu kuma kowanne idan an tashi zaka ji an cewa abu kaza yake sayarwa ko yake kerawa. Shin ka taba tambayar kanka me Abbati yake sayarwa? Ka taba ganin wani abu cikin kayan sayarwarsu ya kawo gidan nan?"
Shirunsa ya bata damar cigaba da magana cikin lumana.
"Malam ni da kai mun sani cewa yaron nan duk fadi tashinsa yana yi ne domin ya inganta rayuwarmu. Kafatanin gidan nan babu wanda Abbati bai shiga rayuwarsa ba." Muryarta sai ya karye tun kafin ta fadi abin da ke zuciyarta "dan nan yaron kirki ne ba don ni na haife shi ba. Amma ina tsoron kada haram..."
"Ya isa!" Mal. Inuwa ya furta yana mikewa. Zargin ta dasa masa wanda ko kadan bai so ba. A duk lokacin da son bincikar dan nasa ya bijiro masa sai tsoron abin da zai tarar ya hana shi. Amma yau yaji wani irin nauyi ya sauka a zuciyarsa mai tayar da hankali.
"Allah Ya huci zuciyarka. Mu kwana lafiya."
Daga wadannan kalaman ya shige uwar daka ta barshi. Ya fita zuciyarsa tana ta wasiwasi. Amma yana zuwa wurin Mal. Sa'adu da ya same shi da Shazali suna hira sai ya tura zarginsa baya.
Da safe Deluwa har dakin da aka sauke Shazali ta tura 'Yashshafa ta kai masa abinci. Ta hada mata da hudubar kwarkwasa domin daukar hankalinsa. To 'Yashshafa ko kadan baiyi mata ba daga kallon farko. Akwai kudi ta gani daga sutura da motarsa. Bashi da wani muni amma mummuman nufin dake zuciyarsa ya tasirantu a cikin ji da ganinsa. Ko murmushi yake idan ka kalle shi zuciya sai ta harba saboda shaidan ya gama dashi. Da zumbura baki tayi sallama kuma yana amsawa ta ajiye a bakin kofa ta gudu abinta. Gara dai a mayar da ita Kadunan ko sa saba da Suhaib. Matsalarta daya akansa bata wuce kaninsa da ya kirata Iya duba-duba ba. Idan ta auri yayansa sai ta tashi tsaye ta saita shi don kada ya rainata.
Wajajen biyu da rabi aka raka Shazali bangaren Baaba Mari zai yi mata sallama. Ita kadai ce a falon nata tana sauraron rediyo.
'Saboda ke Abbati bai isa ya jika min aiki ba. Munzali baya ketare maganarsa. Idan ya ce su komo gareni karshenta da gudu zai biye masa ya amince.'
"Zauna mana"
Baaba Mari ta furta da dan karfi domin ta dawo dashi daga duniyar da ya luluk'a. Jikinta har sanyi ya soma yi da ya shigo saboda kallon da ya kafeta dashi yana tunanin yadda zai bata mata da.
Gaisheta ya yi da girmamawa da zai tafi ya kawo dubu hamsin ya ajiyeta a kusa da ita. Kudin ma tsoro ya bata tunda bata san manufarsa ba. Haka kawai ya zo ya kwana kuma gari ya waye zai tafi ya hadata da kudi.
"Daukesu don Allah."
Nunawa ya yi kamar bai ji dadi ba ya yi magana cikin rashin walwala.
"Don Allah ki dauka kisa mana albarka. Na san da Abbati ne ba za ki ce ya dauke ba."
"Duk da haka ai kai bakonmu ne. Ni dai don Allah ka dauke nagode."
Wayarsa ya zaro yana cewa "tunda baki daukeni d'a ba bari na kira Abbati da kansa ya fada miki matsayina."
Matsawa tayi daga inda kudin suke tana sauraron alamar shigar kira saboda speaker ya saka. Sau hudu ya kira Abbati bai dauka ba saboda suna zaune da Munzali suna amsa tambayoyin Alh. Tahir da wasu yayyensa. Sakon text Shazalin ya tura masa wanda ya saka shi kira hannu na rawa bayan ya tashi ya fita.
(Ina dakin Baaba Mari a Kirikasamma)
Shazali sai ya dauka ya kuma danna speaker a lokacin da Abbati yake magana hankali a tashe. Ya gama birkicewa gami da tsorata. Magana kawai yake yi yana mai jin inama zai iya bude ido ya ganshi a gidan.
"Ban gane kana dakin Baaba ba? Shazali me zai kaika gidanmu."
"Zumunci mana."
"Zumunci? Ko da can ka taba jin na nemi yin zumunci da kai da balle yanzu?"
Shazali sai ya kalli Baaba Mari ya marairaice kamar kalaman sun bashi mamaki shi ma.
"Ka bari na fita nan ba wurin wannan maganar bane. Ni kararka na kawo mata akan kasuwancinmu. Sana'ar tana kawo kudi kana neman durk'usar damu."
Daga bayan fage (background) Abbati yaji ana kiran sunan wata ya kuma gane muryar mai kiran da sunan wadda aka kiran duka 'yan gidansu ne. Hankalinsa sai ya nemi gushewa saboda tsananin tashin hankali da ya gane da gasken yana gidan. Gargadin da yake yi masa ma a raunane ya fito domin yana daf da fita daga hayyacinsa.
"Shazali! na rantse idan ka fada mata wata magana sai ka raina kanka. Hummm....Kai bari kaji in fada maka, idan ka sake ka fada mata abin da zai tayar mata da hankali sai na dauki mummunan mataki a kanka."
Baaba Mari tana daga zaune amma jiri ke dibarta. Hannuwanta ta sanya ta rike gefe da gefen kujerar two seater da take kai a zaune. Idanunta a rufe taji muryar Shazali yana bawa Abbati amsa. Tasa muryar a nutse take fita da wani abu da za a iya kira da nasara.
"Kwantar da hankalinka ni hanya ce ta biyo dani na zo muka gaisa. Ban san sadar da zumunci da iyayen aboki laifi bane da ban zo ba."
Kashe wayarsa ya yi ya juya ya fita ko sallama bai yiwa Baaba Mari ba. Bukatarsa ta riga ta biya. Ko yanzu kasuwa ta tashi Dankoli ya ci riba. Bukatunsa akan Abbati biyu ne. Ko dai tsoron tonon asiri a wurin mahaifiya da danginsa yasa shi komawa ruwa ko kuma asirin ya tono ya zubar masa da mutumci kamar yadda ya hana shi cigaba da samun kudi. Yadda ya san Munzali yana jin maganar Abbati ko uwar da ta haife shi baya jin ta isa dashi. Umarnin da hani a hannunsa suke. Shi yasa ya zabi biyo masa ta bayan gida.
Abbati ya dinga kiransa wani