Showing 144001 words to 147000 words out of 242549 words
musu sallama shi ma ya yi harda cewa su gaida gida.
Murmushinsa bai hanata satar kallon Munzali ba a hanya tana jiran ya fara fada. Gani take kamar na mugunta yake mata bayan ya gama hada mata bomb.
Kallon hanya da zurfi cikin tunani da take ganin Munzali ya yi bashi da alaka da abin da take tunani. Suhaib ya yi masa magana ne akan baffaninsu maza da suka yaba dasu har suka bukaci a sanar dasu cewa su turo iyayensu indai da gaske suke. Ya kira Abbati yafi sau shurin masaki amma bai dauka ba tunda gari ya waye. Abin ya karu domin yanzu wayar ko shiga bata yi. Haka ya rufe ido ya kira layin Baaba Mari shi ma shiru. Kafin ya isa kofar gidan Hasiya ya kira mutum ya kai shida a gidansu Abbati. A kalla kowanne ya kira sau uku ko hudu. Hankalinsa ya tashi sosai har ta kai kwatancen gidansu da Murja take yi masa baya ganewa sosai. Sau biyu yana yin kwana sabanin wadda take fada masa.
Tsayuwarsa da mota ke da wuya Ummita ta fito rike da Hasiya a jikinta. Tangadi suke duk su biyun. Hasiya na ciwo, Ummita na firgicin irin aman da taga tana yi. Cikin kankanin lokaci ta fita daga hayyacinta. Ko kashe motar bai yi ba Ayaah da Murja suka fita da sauri.
"Me ya sameta?"
Ummita tana kuka ta fada masa yadda Hasiya ta dinga amai daga kwabin lalle. Babansu kuma tun safe Abdulkarim ya turo aka tafi dashi asibiti tare da Abbas. Duk wannan bayanin a hanya aka yi shi. Gudu irin na ganganci ya dinga yi saboda kakarin da Hasiya take yi a galabaice.
Kiran Abbatin da bai sake samun damar yi ba kenan a ranar domin suna zuwa asibitin emergency aka nufa da ita.
***
"Gabadaya na kasa fahimtar bayaninka Abbati. Haka kawai ta suma bayan bata kwana da ciwon komai ba?" Mal. Inuwa ya furta hankalinsa yana ga Baaba Mari dake kwance akan gadon asibiti rai kwakwai, mutu kwakwai.
Atine ce tayi karfin halin cewa "Ya ce magana suke fa yaji ta daina amsawa"
Duka 'ya'yan Baaba Mari suna dakin da aka kwantar da ita a babban asibitin garin Kirikasamma. Abbati ya rasa me yake masa dadi a duniya. Gefe guda ya samu ya zauna ya hada kai da gwiwa cikin tunani. Tare suke da mahaifinsu Mal. Inuwa da wasu cikin Gwoggoninsu matan 'yan uwansa. Shi Mal. Inuwa yafi kowa nuna gigita saboda yadda yaga Abbati ya fito da ita waje a hannu ko motsi bata yi. Daga shi har 'yan majalisarsa sun dauka bata da rai.
Kowa yana tofa albarkacin bakinsa game da ciwon da ba a san silarsa ba likita ya dawo. Wasu gwaje gwajen jini ya sake rubutawa ya bukaci Abbati ya biyo shi waje.
Da sauri Mal. Inuwa ya ce "Fadi ko ma mene ne Dafta. Nan wajen duka babu bare. Me ya sami Mari?"
Likitan ya dubi Abbati wanda ya gyada masa kai sannan ya fada musu abin da suka gano.
"A gaskiya jininta ya hau fiye da kima har yana barazanar taba mata zuciya. Idan ba a dauki matakin da ya dace ba zata iya samun stroke (mutuwar barin jiki) ko ...."
"Allah ma Ya kiyaye" cewar Mal. Inuwa da rawar murya "indai kudi ne sha Allahu ba zai gagara ba. Ayi mata duk abin da ya dace ga danta nan."
"Malam. Malam"
Ba Mal. Inuwa da ta kira ba, duka wanda yake dakin sai da ya juya da farincikin ganin Baaba Mari ta farfado.
Da hannu ta yafito shi ya matso kusa da gadon ya duka kansa ganin tana ta motsa baki.
"Ku mayar dani gida."
Wani irin kallo ya mata cikin tashin hankali ya daga kansa ya yiwa Abbati inkiya da ya matso. Su Habi duk sai suka fice.
"Kaji taurin kan mata ko? Wai a mayar da ita gida."
Murmushi tayi masa "Idan an kaini asibitin waye zai biya kudin?"
"Wace irin magana ce wannan? Ko kin sami makuwa ne saboda ciwo?"
Muryarta ta kara dusashewa ta ce "kana da sauran kadara ne Malam da zaka sayar ka nema min magani?"
Duk da ya soma harzuka haka ya daure saboda ba lafiya gareta ba ya ce
"Wai ba ga Abbati ba? Mari lafiyarki kuwa?"
Idanun Abbatin ta lalubo da nata. Ya zabge tamkar shi ne kwance a gadon asibitin. Kalamanta na gaba a gareshi ita kanta basu yi mata dadi ba sai dai babu gudu ba ja da baya.
"Ban yafe ba idan ya sake kashe min kwandalarsa. Ban yarda kaima ka kashe min daga kudin da ya baka ba. Sannan idan ban tashi ba ka isar da sakona ga dan uwanka Sa'idu. Ni MARIYA BA YAFE MASA BA!"
I just published "31" of my story "UWA UWACE...". https://www.wattpad.com/1072817053?utm_medium=com.whatsapp&utm_source=android&utm_content=share_published
UWA UWACE...31
Batul Mamman💖
"Anya Mari baki yi gamo ba? Yaya Sa'idun kike ja wa Allah Ya isa?"
Wani bacin rai ne ya turnuke kirjinta. Wato bai ma damu da abin da tace akan dan cikinsa ba sai yayansa wanda ya zama silar rushewar rayuwar 'ya'yanta maza.
"Ko in hada da kai ne?"
Mal. Inuwa ba arziki ya saita fuskarsa daga fushin da ya yi da farko
"Ni kuma me nayi?"
Ko kula shi bata yi ba ta dubi Abbati da murmushi. Wannan karon kallon yana cike da soyayyar uwa da danta. Yadda ya koma yafi mata ciwo akan shi kansa. Dukiyarsa take son ta raba shi da ita domin babu amfani su cigaba da ninkaya cikin haram. Sabuwar rayuwa za ta tura shi da taimakon Allah wadda bai taso cikinta ba tunda ya fara sana'arsa. A yanzu yafi bukatar soyayyarta da tausayawa kuma a shirye take ta nuna masa domin yaji dadin tuba.
"Kirawo 'yan uwanka su taimaka min na tashi."
Kai ya gyada daidai da saukowar hawaye a idanunsa. Tana kallon yadda yasa bayan hannunsa ya dauke hawayen sai dai bai hana wasu gudana suna maye gurbin wanda yake sharewa ba. Haka ya fita bai yi musu akan rashin son zamanta ba. Ya fahimceta sarai. A shirye yake ya bi umarninta. Da hannu ya kara goge idanunsa sannan ya kira kannen nasa.
Da ya fita Mal. Inuwa kallon tuhuma ya dinga yi mata. Tabbas akwai abin da yake faruwa tsakaninta da Abbati. A matse yake da son ji. Sai dai yanayin fuskarta ya sanya tayi masa kwarjinin da ba zai iya yi mata titsiye ba.
Likitan da ya dubata har bakin mota ya bisu yana nanata musu gangancin dake tattare da dauketa a yanzu.
"Bai kamata ku biye mata don ta ce ba za ta zauna ba" ya dubi matan da ya tabbatar 'ya'yanta ne saboda kukan da suke da rokon yayansu akan su zauna "za ta iya shiga yanayin da dukkanku nan sai kun yi dana sanin kin karbar shawarata."
Habi sai ta koma kusa da mahaifinsu tana kuka.
"Kaji abin da yake cewa Baba. Don Allah ka tilasta mata ta zauna."
"Abbati?"
"Baba muje gidan. Da kaina zan dawo da ita asibiti in Allah Ya yarda."
Iyakar abin da yace kenan ya shiga gaban motar da zata mayar dasu gida.
*
Deluwa ce kan gaba wurin zuwa bangaren Baaba Mari bayan sun dawo. Daga ita sai daurin kirji da dankwali a ka. Tabe baki tayi tana soshe-soshen jiki.
"Yo aka ce mana ranga- ranga aka fitar dake ashe ma ciwon ba wani na azo a gani bane."
Ci-kan-ki wannan bata samu daga bakin kowa ba. Ta gaji da maganganunta ta kama hanya za ta fita.
"Ki kirawo min mijinki idan kin fita"
Wata irin juyowa Deluwa tayi ta kalli bakin Baaba Mari da ya furta wannan maganar. Har wani duka ta kaiwa kunnenta domin tabbatarwa.
"Ki ka ce?"
"Ki turo min mijinki! Da jikina da kwari da kaina zan je na same shi."
Mal. Inuwa dama ya matsu yaji me yake faruwa. To amma shi ma yadda tayi maganar ba karamin tsorata shi ya yi ba. Musamman da ta sallami duka 'ya'yanta da jama'ar gidan da suke sashen nasu ta bar Abbati shi kadai. Dadin dadawa kuma sai shi ma Abbatin ya yi wata magana da ta sabule masa kuzarinsa ya kara shiga firgici akan me yake faruwa.
Hadiyar yawu mai masifaffen daci ya yi, idanunsa duk sun shige ciki ya dubeta.
"Baaba tona min asiri zaki yi? Na rantse miki ba yau na tuba ba. Ni da Munzali har..."
Runtse idanuwa tayi da ya ambaci sunan Munzali. Allah Ya sani ko sunansa bata son ji balle ayi hirarsa. Ya fice mata a rai lokaci guda kamar anyi ruwa an dauke. Akwai laifin mijinta da yayansa dumu dumu amma nasa mai girma ne. Bata jin zata taba manta cewa shi ya koya masa....karshenta ma har yanzu suna yi. Tsigar jikinta a take ta mimmike da wannan tunanin.
"Idan ban yiwa tufkar hanci ba ka san irinka nawa zasu samar mana a dangi?"
Abin da ta ce kenan. Sai ya koma jikin bango ya tsaya tare da jingina bayansa. Babu wani abu ko digo da yake yi masa dadi a duniyar nan. Nadama iyakar nadama ya kara yi. Ya tsani ranakun da ya mika jikinsa ga marasa tsoron Allah cikin manyan mutane masu fada a ji a kasar nan. Farincikin da kudaden suka saka shi ya koma bakinciki.
Sallamar Mal. Sa'idu da kakkaurar murya mai nuni da girman bacin ransa sai da tasa hanjin cikinsa kanannadewa. Zazzabi mai zafi har cikin 'bargo ya afka masa. Daga wannan lokacin zai sanya kafa guda da sabon shafin rayuwa. Idan har zai iya cigaba da rayuwar.
Shikenan!
***
"Wa nake gani kamar Mariya?"
Asabe ta takawa kafafunta burki a daidai kofar dakin Innayo. Laluben dakin da yake sakale akan dokin kofa ta sake dagawa da hannunta ta leka ciki. Tabbas jikarta ce take hangowa zaune akan cinyar Salima tana ta zuba surutu. Ranta ya sosu ta taka cikin falon ko sallama babu sai ganin hannunta Salima tayi tana kokarin fincikar Qibdiyyan.
"Tashi ki wuce muje."
Noke kafada tayi ta kwace hannunta. Salima ta murmusa kawai ta ce mata "tashi mana Qibdiyya. Sannu da zuwa Asabe."
"Ban son munafunci. Ki rike sannunki ki sakar min jika"
Sababi ta hau yi akan dalilinsu na riketa a dakin.
"Shi ma Munzalin zai zo ya sameni. Akan me zai kawota bai fada min ba?"
Innayo da Zara duka suna falon amma yadda bata nuna ta gansu ba haka su ma basu kulata ba. Ta gaji da fadanta ta dauki Qibdiyya da karfi ta nufi bangarenta.
Ihunta suka ji da ta tura kofar ta bude ba tare da ta saka mukulli ba.
"Jar uban nan! Wallahi gidan nan baku so zaman lafiya ba. Wace mai kokarin ce ta bude min daki?"
"Daddyna ne ya budewa su Uncle Lilu."
Asabe ta gatsina fuska "waye kuma Unku Lihu?"
"Uncle Lilu da yake min doki a bayansa... " Cewar Qibdiyya da mamakinta irin na yara idan aka kasa gane abu mai mahimmanci a wurinsu.
Asabe hakura tayi da neman ba'asi. Duk inda yake ta san dole zai dawo daukan 'yarsa. Zata nemi karin bayani a wurinsa. Sannan kuma ta samu ta karbi kudin da take tunanin shi ya zo bata.
Mayafinta ta kama za ta cire Qibdiyya ta ce zata yi fitsari. Sunkutarta tayi gabadayanta ta shiga bandaki. Yarinya fes da ita amma saboda son burge mahaifinta kamar ba dan cikinta ba ta tube mata kaya.
"Wanka zan miki kada ya dawo ya ganki haka kamar wadda tayi dambe."
Bata da ruwan dumi amma don kar ya dawo bata gama ba idan ta tsaya dafawa sai tayi mata da mai sanyi. Qibdiyya harda kukanta don garin babu wannan zafin da zai sa mutum wanka da ruwan sanyi. Aka zo shafa mai tabi ta mulketa da man kadanya sai kyalli take. Ta kawo kwalli aka rambada mata a ido. Ta tafi dauko pant din da ta cire mata a bandaki Qibdiyya ta kai hannu gabanta tana susa. Wanka ne aka yi aka koro maikon jiki amma ba ayi mata tsarki ba. Dan datti da ruwan sabulun da ya wuce ta wajen da fitsarin da tayi ba a wanke ba.
Wannan susa akan idon Asabe da ta dawo daga bandakin.
"Kalau kike kartar jiki haka da karfi? Kwanta mu gani ko kurji ne a wajen."
Da kanta ta kwantar da ita ta kai hannu za ta raba kafafunta taji ta cafke mata hannun. Idanuwa Qibdiyya ke binta dasu tana yi mata kallon tsoro.
"Kema hannu zaki saka min a nan? Kiyi min a hankali ba mai zafi ba. Kuma ba zan fadawa kowa ba don kada ki yanka min Daddy da Papa."
Asabe ido kawai ta zuba mata ta kasa kwakkwaran motsi saboda firgici.
Qibdiyya kuwa tuni ta rufe ido tana jira ayi a gama. Da taji shiru sai ta bude idon a hankali. Da karamar muryarta ta ce da Asabe,
"Ni ce zan yi miki?"
Kamar wadda aka kwadawa mari sai lokacin Asabe ta dawo hayyacinta. Kuka ta kama yi ba tare da ta sani ba ga jikinta ya soma rawa kamar mazari. Furucin Qibdiyya ya matukar tayar mata da hankali fiye da tunani. Shi yasa bata ma san lokacin da ta d'aka mata wani mugun duka a cinya ba.
"Ki yi min uwar me? Na bonu ni Asabe. Kiyi min me? Tashi don uban...."
Qibdiyya ta tashi zaune a razane tana son yin kuka amma tsoro ya hana. Daddy ya hanata kuka ko taji zafi idan yana yi mata abu irin wannan. Cewa yake hawayenta na fita za a saka mamanta a rami a rufe da kasa. Tun bata iya ba har ta kware wurin danne hawayenta. Idanu tsilli tsilli ta kafe Asabe dasu babu alamar kuka duk zafin dukan.
"Daina kallona" wani tunani tayi ta sake kwantar da Qibdiyya ta soma dubata. Allah ne kadai Ya taimaketa bata suma ba akan abin da ta gani. Kankanuwar yarinya ta kusa gama budewa.
Kafafunta kasa daukarta suka yi bata ankara ba tayi zaman 'yan bori a kasa. Kai ta dago dankwalinta ya karkace saura kadan ya fadi ta kalli jikarta.
"Waye yake taba miki nan?" Ta nunawa Qibdiyya inda take tambaya da hannu.
Razanar da tayi a dalilin dukan da tayi mata dazu da kuma tsoron kada a rufe mata uwa a rami sai taki fada. Jikinta yana bata cewa idan ta fada din ma ba tsira zata yi ba.
Asabe ta gaji da tambaya ta soma dukanta. Amma ko digon hawaye babu sai ajiyar zuciya. Hargagin muryarta tana cewa "ba za ki fada min ba?" har tsakar gida. Uwani ta fito tana waya taji. Hanyar dakin ta nufa sai dai kafin ta isa Innayo ta fito daga nata dakin ta ce mata kada ta soma zuwa.
"Bana son gulma ki zo ki wuce naki uzurin kada ki ja min magana".
Komawa tayi din amma haka kawai taji ta kwadaitu da son sanin me yake faruwa. Maganar dai kamar da Qibdiyya ake yi amma bata ji ko tarin yarinyar ba.
*
"Munzali kana ina?"
Sautin muryarta banda alamun tashin hankali harda kuka yake iya ji.
"Muna asibiti da Hasiya ne amma na kusa tahowa. Wani abin ne?"
Karo na farko a rayuwar Asabe da ta dakata tayi tunani kenan da kwakwalwarta. Wannan sam ba maganar waya bace.
"Ka taho da sauri ina son ganinka yanzun nan."
Bayan ajiye wayar hankalinsa ya kasa kwanciya. Yasa rai da jin mitarta akan zuwa wurin 'ya'yan Innayo. Kudi ya damkawa Ummita kafin shigowar Hon. Habu ya ce musu zai je gida ya dawo.
Akan hanya ya dinga kiran Abbati shiru bai dauka ba. Kansa ya sake daukar chaji kamar ana buga guduma. Ya san Abbati ba yaro bane da za a zane bayan ya fadi gaskiya. To amma me ya biyo bayan fadin tunda ya tabbatar da wahala idan bai fada din ba.
***
Sanyi da daddadan kamshi ke tashi a wani katafaren falo. Duk inda ake neman ni'ima mai shiga zuci an gama samu a nan. Mazauna wurin maza ne su biyar wadanda shekarunsu suka tura. Ga kuma shaida a jikinsu na cewa sun kama kasa. Daga 'yan siyasa sai 'yan kasuwa sai kuwa masu manyan mukamai a gwomnati.
Dukkaninsu sanye suke da manyan kaya harda babbar riga illa mutum daya. Daga gani shi ne mai masaukin baki saboda yadda ya bararraje. Hula da babbar rigarsa duk suna gefe guda can nesa dashi. Bayani yake yiwa babban bakonsu. Amininsu ne ta fanin harkokin 'yan mata. Sai gashi a Kano garin yake gida ga sauran hudun.
"Yanzu sai da kana shirin komawa Kaduna zaka sanar damu zuwanka Alh. Tahir? Karramawar nan da ake yiwa manyan baki ma baka bamu damar yi maka ba."
Cewar mai gidan hutun (guest house) din da suke ciki.
Dariya Alh. Tahir ya yi masa "banda abinka ni da na taho da taurarina guda uku ina ni ina bin kwararo?"
Kwashewa suka yi da dariyar shakiyanci suna zolayar juna. Nan hira ta kacame da ciye ciyen kayan abinci na alfarma. Maigidan aka kira ya amsa ya bayar da umarni ga mai kiran da ya shigo.
Alh. Tahir na jin haka ya san ba zai wuce mace aka kawo ba. Murmushi ya yi yana gyada kai.
"Ni dai bari na gudu don na tuba."
Wani Alhaji mai tulun ciki ya tafa da na kusa dashi suka yi masa dariya "Kowa ya tuba don wuya ba lada."
Alh. Tahir ya kada kai "da lada fa. Abubuwa sun cabe min. 'Yar banzar yarinyar nan kawar Farha da nake fada muku yanzu fa Yakumbo ta rantse sai na aureta. Yarinyar da take yawonta da kananan yara kuma duk na sani."
Mai gidan yaja guntun tsaki "duk laifinka ne. Na fada maka wallahi Malamina yana aiki akansu maganar nan zata bi ruwa. Ita Yakumbon da kanta za ta ce a bar maganar. Yarinyar kuwa duk iskancinta sai an sauke mata shi. Ba za ta sake yin wani yunkuri domin bata maka suna ba."
"Wai kai Alh. Tahir tsoron me kake ne? Ka amince mana ka yar da kwallon mangwaro. Yarinyar nan a bariki ta sameka tayi kadan ta kawo maka cikas da girmanka da komai." Wani da bai ce komai ba tun dazu ya tofa albarkacin bakinsa.
Mai neman kuka ne aka jefe shi da kashin awaki. Basu wani jima ba suka shawo kansa. Nan take Maigidan wanda aka fi sani da Comared ya kira Malamin tsibbunsa a waya. Suna kan magana wani mutum sanye da kufta da wando ya zo ya shige cikin dakin Comared din da dan matashi da bai fi shekaru sha takwas ba.
Bayan ya gama wayar ne Alh. Tahir ya tsare shi da idanu yana nuni da dakin nasa.
"Comared ba dai kaima ka fara daya harkar ba da maza?"
Kkamar dazu, yanzu ma dariya sauran