Showing 102001 words to 105000 words out of 242549 words
mata a ladabce. A zatonsu gefen da ta kebe kanta tana danna waya duk cikin rashin kunyarta ne.
"Ku kuma don baku taba gani ba sai ku yanke mata hukunci da rashin iyawa?"
Mamaki ya kara kamasu. Anti Hasiya ce fa ta kare mata! Anya yau lafiya kuwa? Kara musu mamakin tayi ta hanyar kallon Antin tasu suka yiwa juna murmushi sannan ta kallesu ta murguda baki. Da sauri ta ta juya ganin Anti Hasiyan ta bude baki. Bata so tayi mata fada yau. Kullum ita ce mai laifi idan abu ya hada da yayunta. Yau dai ita aka tarewa. Duniya tayi mata dadi.
*
Innayo ta fito daga bandaki ta jiyo muryar Uwani da Zara a cikin daki. Bata ji shigowar Uwanin ba ta shiga wanka bayan ta gama hadin sabulun salo na jaririyar da take nuna bata damu da ita ba. Hannun kofar ta kama za ta bude ta ji zancen da suke yi wanda ya sake tsinka mata zuciya game da sha'anin 'ya'ya.
"Yo don dangin Innayo basu zo miki barka ba sai ki hau kuka? To ko dai kin ji wata magana ne?" Uwani ta furta da bacin ran ashe duk kukan Zaran ma mara dalili ne a ganinta.
"A cikin gidan fa nake amma ko mutum daya ban ji ta kira ta fada musu haihuwar ba. Ai dole abin ya yi min ciwo. Kuma ita ma bata taba daukan yarinyar nan duk kukan da za ta yi."
"Kinga Zara bana son munafunci fa. Ni ce ba wata ba da za ki fake da rashin zuwan dangin Innayo don ki boye 'yar tsamar dake tsakaninki da mijinki. Daukar jika kuma ina ce haka kike so?"
Daidai lokacin Ayaah ta shigo. Murmushi ta yiwa Innayo tunda sun gaisa lokacin da suka zo. Tashin maganganun da ta ji ita ma sai ta kasa karasawa dakin. Fita ya kamata tayi amma ta kasa lokacin da ta kula idanun Innayo a birkice suke. Akwai boyayyen bacin rai da damuwa a cikinsu. Sai kuma kwallar da ta cika shi taf amma taki bari ta zubo.
"...ba har gidanki ki ka kirani akan in zo in karbarwa su Innayo tsofaffin kayan da baki dinka ba don kada su zama abin kallo wurin taron suna ba?Ko baki dinga yamutsa fuska da na baki labarin tana ciwon hakori ki ka ce kazanta bace? Shi ne yanzu za ki dinga kukan karya kamar kin fi kowa damuwa da ita..wai ma da kin taba gayyayarsu suna ne?"
"Meye na daga muryar? Kuma duk abin da ki ka fada ai bai canjata daga zama uwata ba." Zara ta ce da sanyin muryar wanda hankali ya fara ziyarta.
Uwani tayi wata irin dariya ganin kamar rainin hankali Zara take yi mata.
"Daga baya kenan amma kin san sai dai ki fadawa wanda bai sani ba ko? Na san Innayo za ta ji dadi. Ko ba komai yadda ta dade tana son ki dinga rabarta sosai yau ta samu tunda baki da tudun dafawa."
Allah Sarki Innayo, kwallar sai ta sauko a guje. 'Ya'yan cikinka su yi maka irin haka ba karamin ciwo gare shi ba. Ji tayi kafafunta suna neman sakinta a kasa sai hannuwan Ayaah suka tareta.
Tausayin Innayo ya tsirga mata. Tunda suka shigo matar nan tana kan kafafunta. Amma ita ce 'ya'yanta suke yiwa haka.
Daga ciki suka ji Zara na cewa "Ko ma me za ki fada kiyi ta fada. Na riga na fara ganin nawa sakamakon, ki jira naki."
"Ba zan ga komai ba sai alheri. Wato rashin kunyar da ki ka kwana biyu baki yi ba saboda kin dawo gida mai soro ce tasa ki cewa nazo dama?"
Zara ta share kwallar da ba za ta ce ga aihinin dalilinta ba.
"Ki barshi kawai."
Ayaah kasa jurewa ganin hawayen Innayo tayi ta juya za ta fita. A yau ta fahimci me yasa a gida ake bukatar wanda ba ya shakkar kowa.
"Ina za ki?" Innayo ta tambayeta cikin dusashewar murya.
Kofar dakinta ta harara tukunna sannan ta ce "Anti Hasiya zan kira."
Innayo ta murmusa ganin ran Ayaah yana neman fin nata baci
"Dawo abinki Hajara. Idan babarki ta zo raina sai yafi yanzu baci. Ba wani hakuri gareta ba bare jin magana a irin wannan yanayin."
Ayaah bata san lokacin da tayi murmushi ba "da gaske ita ma bata jin magana?"
"Ban ce ba" Innayo ta amsata cike da kulawa.
Sautin tsakin Uwani wadda ta mike suka jiyo tana mai cewa
"Aikin banza. Kin san abubuwan da na katse na zo? To wallahi sai kin biyani tunda a bakin aiki nake ki ka sani fitowa."
Zara ta auna ta ga a neman lafiya babu ji da kai. Idan tayi shiru kanta za ta cuta. A yadda ta wahala kwanakin farkon haihuwarta ba za ta so a maimaita ba.
"Wurin dinkin nan nake so ki duba min. Ina jin kamar bai yi ba."
Metiron Uwani ba mutumci. Banda tana tsoron kada kasuwar ta watse da sai tayi dariya. Ai tun ranar da Innayo ta saka ta duba Zaran ta kula dinkin zai iya samun matsala saboda rashin kulawar da ya samu. Duk da cewa a ranar a tsorace take amma ta san muddin Hasiya tana wurin bata isa ta karbi kwandalar Innayo ba. Ashe kuwa tana da rabo. Tunda Zara ta sake kawo kanta wallahi sai taci kudinta.
Tashi tayi kamar za ta fita daga dakin a zuwan bata damu ba ta ce "Aiki ne na kuďi Zara. Sannan dole ki san karyar da zaki yi ki zo ki sameni a gida. A nan Innayo..."
Innayo kawai ta bude kofar. Su biyun kowacce ta zaro idanu. Jaririyar ta nunawa Ayaah.
"Dauki kanwarki ki fita kuma kada ki manta abin da na fada miki."
Umarni ta bi ta koma tsakar gida da 'yar jaririyar wadda ta sake nannadewa a shawul.
"Uwani"
Cikin Uwani sai da ya tsirga don tsoro ne ya cika mata zuciya. Yanayin Innayo yasa taji kamar tayi tsuntsuwa ta ganta a nata gidan.
"Ba dake nake ba?" Innayo ta yi mata tsawa.
"Na'am" Muryarta har rawa take da ta amsa.
"Ban ce ki duba min Zara zan biya ki ba rannan?"
"Kin ce."
"Isa ne ban yi ba ko? Saboda bani da wannan mutumcin a idonki."
Maganarta ta biyu babu hargagi balle daga murya. Amma zukatan fitinannu cikin 'ya'yan nata sun girgiza. Duk abinsu bata taba nuna musu wannan bangaren nata ba. Sai suka zata duk wani rashin albarkarsu za ta karba saboda tana son su.
"Wallahi Inn..."
Katseta tayi da cewa "Duba ta."
Zara ta kwanta da tsoron kada fadan ya dawo kanta. Uwani na dubawa ta ce sai an sake dinkin. Hawaye ta soma fitarwa kawai saboda tuna irin azabar da tasha a 'yan kwanakin da suka wuce. Tana ji Innayo ta ce da Uwani ta je ta dauko kayan aikinta. A gurguje ta fice. Duk da dan akwatin tafi da gidanka da take yawo dashi yana mota ita dai burinta ta ganta a waje. Bayan fitarta ne Zara ta kasa daurewa ta kira Innayo a raunane.
"Innayo."
Bata amsa ba ta fita daga dakin. Wurinsu Hasiya ta tafi ta ce komai suka gyara su adana shi suna sai wani satin.
"Wani abin ne ya faru?" Cewar Maimuna.
"Maijego babu lafiya. Banda ma sun dorawa kansu waye yake wani taron suna a haihuwa ta biyar?"
Hasiya kamar bata yarda ba. Dama ta kula da wani irin yanayi da Ayaah ta fito dashi kamar tayi kuka. Ana haka Uwani ta dawo. Bata cewa kowa komai ba ta shige ciki.
Innayo ta bi bayanta ta rufe kofar falonta. Kafin a fara tasa Zara kiran Alh. Unais. Sai da tayi masa kira hudu sannan ya dauka a wulakance.
"Ina fata ba cewa za ki yi kayan abincin sun yi kadan ba. Sannan ki fadawa Innayo dinnan don Allah ayi abinci maidadi saboda dangina da zasu zo da na Laurat. Ayi abin fita kunya."
Taji zafi kwarai da jin kalamansa. Sai dai kuma har duniya ta nade Zara bata da wata uwar sama da ita. Babu mai daukar wannan bakin halin duk son da yake mata ya ce zai jure ya cigaba da kulawa da ita irin na uwa da 'ya. Ita din cw dai dolenta.
"Innayo dinnan ce ba Zara ba. Ka fadawa danginka suna sai wani satin. Idan kuma za ku iya hakura gabadaya zai ma fi."
A hanyar komawa gida yake daga kasuwa. Yana baya direbansa yana ja. Jin muryar Innayo ba shiri ya tashi zaune daga kashingidar da ya yi.
"Wani abin ne ya faru?"
"Ba ta da lafiya."
Ya san Haj. Fatakwal ba za ta lamunce ba shi yasa ya ce zai sanar dasu yadda idan sun zo ba za su takura mata ba.
Gaban Zara yana dukan uku uku ta ji Innayo ta cigaba da cewa
"Baka fahimceni ba kenan. Kwata kwata bana son danginka su zo gidan nan gobe. Bayan wulakancin da ku ka yi min akan zamanta a asibiti da rashin lekowar waninku dubata sai ace za a zo suna? Ga kayan abincinku nan 'yan uwanta sun muku kara sun gyara. Ka aiko a dauka tunda matar taka bata nuna maka mutumcin mazaunan gidan nan ba balle ka zo da kanka. Sannan kasa a kawo mata 'ya'yanta su dubata."
Dammmm...Zara da Alh. Unais da ma Uwani dake tsaye a gefe kowa yaji gabansa ya fadi.
Tsoro ya ji kada ta ce ya sakar mata 'ya ya soma bata hakuri. Yana son Zara har yanzu.
"Kiyi hakuri zan zo. Amma don Allah ayi sunan saboda Hajiyata."
Wato saboda Hajiyarsa. Matar da bata san ciwon tata 'yar ba.
"Suna kam babu shi Unaisu. Idan kun zo ma ba za ku sameta a gidan ba"
Ta kashe wayar ta ce da Uwani tayi aikinta.
"Kinga ya soma warwarewa ne Innayo. Ko in ware duka na sake sabo?" Uwani ta tambaya gudun yin laifi.
"Ni da ban taba shiga aji ba ina zan sani? Ke dai kiyi aikinki zan biya."
Uwani ta san gatse ne. Yau bata san me ya faru ba amma tsoron bacin ran Innayo take irin wanda bata taba ji ba a baya. Haka nan dai ta duka tayi aikinta gabanta yana faduwar da bata san musabbabinsa ba.
Kafin a gama Zara ta kusa suma. Ihu ko surutu irin na mai jin jiyo bata sami zarafin yinsa ba. Tsoron sake batawa mahaifiyarta rai take yi. Wani abu da ya dade bai ziyarci zuciyarta ba. Innayo na ganin yadda take cije lebe da damkar gefen katifa sai ta matsa kusa da gadon. Hannunta kadai ta rike tana girgiza mata kai da rarrashi amma sai taji salama. Ciwon ya ragu sai wani irin abu da take ji game da matar da ta kawota duniya. Hawaye ne ya balle mata bata sharesu ba kuma babu niyar tsayuwarsu. Fuskar nan da ta tashi tana gani a bakin murhu a yau ta maye mata gurbin duk wata allurar kashe ciwo. Bata sani ba ko rashin kula ne amma kamar yau ta fara tantace komai na fuskar Innayo. Idanuwanta sun fada ciki ana gani za a gane wahalar rayuwa ce ta kawosu. Farar fatar da suka gada ta dusashe sosai. Wanda ya san kuruciyarta kadai zai iya bada shaidar ita din fara ce a da. Ga layukan girma don ba a ce tsufa ba sun zane mata fuska. Hannun da ta riketa dashi kuwa ba ka ce na mace bane. Babu kanta kamar da tunda ta daina kaso tamanin cikin ayyukan da take a baya. Amma fatar ayi wani irin tauri kamar na kakkarfan namijin da ya sha aikin hannu. Hannuwa ne da suka raini tare da aurar da mata har guda tara! Mata da masu kudin cikinsu suka juyawa hannun alkhairi baya. Matan da ita Zara take cikinsu! Kawai sai ta fashe da kuka. Ta sake yiwa hannun Innayo wani irin riko tamkar tare da rayuwarta yake tafe. A haka baccin wahala ya dauketa ga gumi ya wanke mata fuska.
Uwani ta gama tattara kayanta ta ajiye pain reliever din da Zara za ta sha idan bukatarsa ta taso. Tsakar gida ta fito za ta tafi daidai lokacin da Ummakati ta shigo gidan da sallama. Ita ma tunda Munzali ya yi mata magana akan gyaran zumuntarsu da 'yan uwansu ba karamin dadi taji ba. Baudadden miji gareta sai da kyar da sudin goshi ya barta ta fito barka da yamman nan.
Ta tsaya suna gaisawa Asabe ta jiyo muryarta tayo waje. Bata ga dalilin wannan shishshigi da 'ya'yanta suka fara ba cikin kwanakin nan. Fadan da ta taso yiwa Ummakati bai samu ba ta tsaya kallon wasan kwaikwayo a cewarta.
Innayo ce tayi saurin fitowa kafin Uwani ta bar gidan.
"Nawa ne kudinki?"
Sai taji kunyar idanun dake kansu. Ko babu su ita yau tsoron Innayo din ma take.
"Ki barshi ba zan karba ba."
Innayo ta hade rai sosai ta ce "Idan baki tsaya kin karba ba daga yau in kin zo gidan nan kar ki kuma shigar min daki."
Maimuna sai ta tashi da sauri "Subhanallahi. Innayo me ya yi zafi?"
"Kar ku saka min baki." Ta kuma kallon Uwani wadda duk ta tsure "nawa ne?"
"Dubu shabiyar. Don Allah ki barshi Innayo." Ta ce kamar za tayi kuka. Kowa ita yake kallo kamar basu santa ba.
Innayo bata saurareta ba ta kwance gefen zaninta. Dubu takwas ta hado dama ta san bata da shabiyar din. A rashin hankali na Uwani idan ta so kin karba da sai ta yanko kudin kasa sosai. Ita dai Innayo sai ta kalli Hasiya da Maimuna,
"Nawa zan samu wurinku?"
Hasiya ta so cewa kar ta biya sai dai ta kama bakinta. Dubu uku ta bayar ta bar dari biyu da zasu yi kudin adaidaita sahu ita da Ayaah. Maimuna ta bada dubu biyun da Innayo din ta bata dazu. Samarin 'ya'yanta kamar hadin baki kowa ya ciro dari biyar kudin da aka basu sallama na aikin kafinta da suke koyo. Murja ta dauko jakarta ta mika dubu daya. Ummita dari bakwai gareta a hannu ita ma ta mika. Ummakati ma da bata san silar abin ba ta bayar da dubu biyu. Ayaah ta bada dari ukun da ita kadai ta rage mata.
Uwani ta kasa motsi balle magana. Kannenta ne da 'ya'ya su duka amma haka suka hada kudin domin fitar da Innayo kunya. Da taki mika hannu ta karba sai Innayo ta kamo hannun ta dora mata kudin a tsakiya.
"Ai na ce miki zan biya ki. Allah ba zai bari naji kunya ba."
Ranar farko da Uwani ta ji muguwar kunya kenan a rayuwarta. Abin da ya faru yanzu shi ne asalin kaskanci a gareta. Tafi kowa kudi cikinsu. Amma sun hada sun bata. Bata iya kwakkwaran motsi ba sai da aka fara kiraye kirayen sallar magariba. Sannan ta farga ashe duk sun watse. Babu kowa a tsakar gidan duk suna falon Innayo sai ita kadai. Kwalla taji tana neman zubo mata tayi saurin sharewa ta fita a fusace.
Innayo sai ta saki labulen dakinta ta koma ta zauna. Tayi minti goma tana karantar yanayin Uwani. Addua take Allah Yasa shiriyarta ce za ta zo ita ma. Ko kusa bata ji dadi abin da tayi mata ba. Sai dai Uwani tana bukatar sabon karatu game da sanin hakki da darajar mutane ba ma mahaifiyarta ba ita kadai. Kudi sinadari ne amma ko kusa ba shi ne rayuwa ba kamar yadda ta zata.
***
"Kwarankwatsa dubu na gaji shika nake bida. Wannan wane irin aure ne? Ki don daga kauye ka auroni?"
Tashin hankalinta yafi tsoro akan na uwargidansa. Bai hango wani dalili nan kusa da zai sa ya saki Ummule ba. Balle yanzu ma da take dauke da cikinsa. Zaunar da ita ya yi a gefensa yana bata hakuri ta soma kuka. Zabi biyu ta bashi kuma kowanne mai tsauri ne a gareshi.
Salihi ya san cewa ta fi shi gaskiya sai dai kuma ya rasa yadda zai bullowa lamarin balle ya iya fadawa Uwani cewa ya yi mata kishiya watanni biyar da suka gabata. Yana jin kwarewa wurin iya masifa da kaskantar da mutum da Uwani take gwada masa ne suka mayar dashi lusarin namiji. Ba ya iya sakata ba kuma ya iya hanata. Dama kuma shi mutum ne mai yakana da hakuri. Ko kadan baya son hayaniya. Yana da rufin asiri daidai gwargwado, wannan ne ma yasa zaman nasu ya yi karko. Daidai da ashana Uwani bata taba karar saya idan bai bayar da kudin ba. Ita fa a dole ba za ta yi rayuwa irin ta Innayo ba. Miji ba zai kwanta ya mori arzikinta ba. Ita da kyautatawa ta miji da mata sai suka yi hannun riga. Babu wata riba cikin aurensu da zai d'orar banda yaran da suka haifa guda hudu. Su ma yaran bata basu mahimmanci kamar yadda take bawa aikinta. Tsabar son kudi a asibitinsu duk wadda bata son yin aikin dare kudi kawai za ta bata tayi mata. Haka suka tashi babu shakuwa tsakaninsu da ita. Shi kuma Salihi babu kulawa daga matarsa.
Watarana anyi jinkirin biyan albashi ya roketa bashi zai biya kudin makarantar yaran. Yana dan yin rance wurinta amma wannan kudin yafi na ko yaushe yawa. Kamar ba za ta bashi ba tana ta kiran babu don kada ya soma saka ido akan abin da take tarawa. Sai da yaran suka yi sati a gida, gashi ta dauki hutun shekara. Rashin sabo da zama dasu sai take jin sun caza mata kai. Hutun da take nema babu. Hayaniya taki karewa. Ba shiri ta ce ta dauki adashi ya zo ya karba. Sunyi akan ana albashi zai biyata sai gashi har an soma zancen jarabawar karshen zangon. Uwani panicked! A zatonta ya yi sama da fadi da kudinta. Ai kuwa ta tayar masa da hankali. Shaf ta manta ya aurar da kannensa biyu mata a wannan tsukin lokacin. Albashin nasa ma bai ishe shi ba sai da ya ci wani bashin. Ita dai kudinta kawai.
Takanas ta taka har gidansu. Mahaifiyarsa tayi mamakin zuwanta ta kuma tsorata. Saboda Uwani bata zuwa sai da dalili. Ba kunya ta fada mata halin da suke ciki.
"Wallahi idan bai bani a watan nan ba hukuma za ta shiga tsakaninmu. Ni ba irin sakarkarun matan da ake yiwa wayo suyi ta bautawa miji da 'ya'ya a banza bace."
Kwantar da kai tayi ta bata hakuri. Ita kuma sai wani jijjiga jiki take kar ta sassauta a fara kira mata ta yafe tunda mijinta ne.
"Gobe in sha Allahu za a kawo miki kudinki Uwani. Nawa ne?"
"Dubu dari biyu da tamanin da hudu."
"Kije gida ba zai gagara