Showing 96001 words to 99000 words out of 241571 words

Chapter 33 - YAR MACE Complete Document hausa novels by Mai Damu.txt

24 Dec 2024

14728

tana can babu kwanciyar hankali.....🚫 LITTAFINA NA KUƊI
500₦
8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay
Shaida biya a turo ta wannan numbers din.
+2347035133148
Or
+2348130269641
Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76


Duk da abin da Tafida yayi min, sai naji sam Mama bata kyautawa Hajiya ba, ina jin yadda Hajiya take kara kaskantar da kanta wannan matar akan Tafida tana ganin jarabawa. Ban gama tsinkewa da Lamarin Mama ba sai da naji tana faÉ—in. "Hajiya idan Matarsa bata da hankali, rukayya sai ta biye mata su zo taiwa Ummu Hadiyya tijara? Na zata duk wani kiyayya zai kare tunda ga zuriar a tsakaninsu amma abin kamar wanda bana sonshi."
"Kiyi hakuri Maman Ummu na sani anyi laifi, amma a kara hakuri haka ba zai sake faruwa ba." "A'a Hajiya na san duk abin da ya faru ki fahimci halin da Ummu take ciki, shi da ke da Mahaifinsa kuna buƙatar Ummu, yan uwansa basu bukatar Ummu idan da yau Tafida da Yan uwansa suna da bukatar Ummu tow da na gani a kasa, shi a cire shi ya shiga damuwa rashin Ummu amma saboda kiyayya irinta dangin miji babu wanda ya zo da sunan ganin yaranshi, idan na fahimta ba Ummu ne basu bukata Tafidar ne baya gabansu sannan Ummu ta haifa masa Yara abin da yake musu zai koma kan Yaran Ummu!" D'ago kai Hajiya tayi cike da mamaki taya Maman Ummu ta hararo abin da take tunani. "Hajiya abin da na faɗa gaskiya ne, kiyi hakuri idan ya samu lafiya ya sawwake mata kowa ya huta su rike nasu dan uwan ni zan rike nawa Yar, aure ne mun fasa an janye." Hajiya cikin sanyin murya tace mata. "Maman Ummu kin san dan yau ka haife shi baka haifi halinsa ba!" "Haka ne Hajiya amma kiyi hakuri ni tun ranar da Ummu ta bar gidan nan na fita a sawun iyayen da suke tursasa Yaransu, a yanzu ina tsaye ne akan Y'ata, Hajiya ni ina da sauki akan Ummu saboda ba ita ɗaya na haifa ba, idan Mahaifinta yasan da haka ni ban san me zance muku ba, kuyi hakuri ya sawwake mata ai tayi kukan zama da shi a cikin ukubar rayuwa yanxu da ya zama wajibi ta raba da shi ai tayi. A da can ban sani ba, a yanzu da na sani ina sonta ina gudun kada wata rana a kawo min gawarta. Hakuri da muke basu ba wai tsoron kada su rasa auren ba ne a'a muka koya musu ne suyi hakuri akan Yaransu. Idan har muka cire amsar bukatarsu da kukansu wata rana gawarsu za a kawo mana, don Allah ki fahimce ni, ina son na tsaya mata ne a matsayina na Uwar Yar mace." "Maman Ummu na fahimce ki, ita Ummun xan iya ganinta!" "Tana cikin dakin!" Mama ta mike ta bata hanya, shigowa Hajiya tayi, ya zauna tana murmushin yake. Ina tsaye na kasa motsi bakina rawa yake. "Zauna Ummu!" Zama nayi kaina a sunkuye. "Suna barci ko?" "Eh Hajiyata!" "Kiyi hakuri na san Mamanki ta dauka da zafi, amma kiyi hakuri Tafida ya sauya dayawa mafi girman sauyawar da ban tab'a gani ba. Nasan an yi miki kuskure amma ni nazo bada hakuri ne, tun da na ganki nasan yanzu bani da aufi ko mutuwa nayi Tafida yana da wacce zata tsaya mishi zata kuma mishi addu'a, ban kara yarda ba sai da na zauna dake sai naga ashe duk addu'ar da nake Allah ya jima da amsa min su, Ummu Hadiyya haka kawai nake miki kallon wacce ta amshi tarbiyyar Tafida saboda hakurin da kika yi na zama da shi a wannan baudadden halin nashi, kuma kika boye kome nashi baki tab'a gayawa wani ga halin da kike ciki ba, kawai don ki rufa mishi asiri, wannan kin fi karfin na kiraki matar Tafida sai dai Magajiyata. Domin kiyi abubuwa da bakina ba zai iya furta su ba, Ummu Hadiyya ina me kara baki hakuri zan ta zuwa kullum domin bikonki don ina son ki kasance da Tafida har zuwa lokacin da Allah ya diba muku. Amma maganar saki Mamanki tayi hakuri ba zan iya goyan bayan Tafida ya sake ki ba, da na ga saki a tsakaninku gara a wayi gari bana raye!" Da wani irin sauri na d'ago kai ina kallon Hajiya wacce murmushi ke kwance akan fuskarta. "Mahaifiyarki tana da gaskiya da mutunci da wata ne ba zata kula ni ba kuma ba zata bari na ganki ba, amma ta bari na ganku. Ki yi hakuri ki kuma saka a ranki kece hasken gidan Tafida."


Duk sai na rikice na rasa me zance mata, Hajiya ta saye ni da kalamanta wanda nake jin kamar wani abu yana zaburana nace mata zan bita, amma ba zan iya watsawa Mama kasa a idanuna ba, bayan gudun da nayi yanxu aji nace xan koma gidan Tafida. Mama sai ta hallaka ni da duka kawai gara na hakura naga lokacin da Mama ta diba min ni yanxu wani shakkar Mama nake ji. "zan tafi Ummu idan kin samu lokaci ki zo ki ganshi!" Hadiye yawu nayi a raina nace. *Cab Hajiya zaki saka Mama tayi min dukar sakwaran shege.* motsi Mufidah tayi ta kalle ni, dauko yarinyar nayi na mika mata, ta rungume tana faɗin. "Fuskarta kamar na Tafida yana Yaro, gashi nan ya girma ya zama.gwamna!" Ni dai ban ce kome ba, a hankali ta mika min ita tana min alama na kwantar da ita. Haka kuwa nayi, aikuwa ta koma barci ta ce. "Ba farkawa tayi bakiɗaya ba, ba kuma nono take so ba ta farka ne taji kina kusa da ita ne!" Gyada kai nayi. Haka ta fito Mama tana wurin kwashe abinci. "Hajiya gashi na zuba miki, zaki tafi?" "A'a Maman Ummu ai tunda naga kawata da mijina naji na koshi, bari na tafi. Na gode!" "Tow a kasa miki a kaiws mutanen asibitin mana!" Fadadda murmushi tayi tana faɗin. "Ba zan ki amsa ba, nasan zai ci idan yaji daga gare ki ne!" Fita Mama tayi ta shiga dakin yan mata ta dauko babban kula me kyau ta zuba abinci, ta saka farfesu a kananun kulolin, sannan ta mika min muka fita, "Ummu na gode sosai!" "Hajiya ba kome, ki gaishe shi da jiki Allah ya d'aga kafadarshi. Kada ya manta al'umma suna jiranshi." Na fada mata a hankali, bayan ta shiga motar ta ce min. "Ke fa?" Damke hannayena nayi ina kallon kasa. "Na fahimce ki Ummu ba zan so ki sabawa iyayenki ba, amma Tafida yana nan yana jiranki!" Shiru nayi ban iya bata amsa ba, har suka bar unguwarmu da ake ta aikin gyara ungwar, cikin gida na dawo jikina a mace, kallo daya Mama tayi min ta dauke kai na wuce daki, ina cire hijab ya banko dakin. "Ina jin kalaman da Mahaifiyarshi tayi amfani da shi wurin rarrashinki, wai ke don Ubanki ba guduwa kika yi ba don nace ki koma? Meye kike nufi da ni da zaki fara tafiya kamar kazar da kwai ya fashe mata?" Cikin tsoro da tashin hankali na ce mata. "Allah Mama ni ban yi wani abu, kuma ban ce mata zan koma ba na rantse da Allah!" "Ke Ummu zan ci abu kazan kazan Ubanki, kada ki ga kin yi min abu ban tanka miki ba zanci Ubanki na rantse da Allah, na ji labarin kin bukaci zuwa ganin Tafida sai na taka wuyarki idan Yaranshi ne suzo su ɗauki kayansu. Yar banza mara kunya da baki son zama da shi hatta ni na sani da kalamanki da motsinki, amma yanzu da kika ji labarin zai mutu har kin bayyana saboda kin mai da ni yar iska na ga shegen da zai fitar min dake zuwa gidan Tafida zai na ci mutuncinku, ita ai Uwace akan me zata bar yaranta suna juyata an gaya miki ni zan ɗauki wannnan iskanci ne ta kuma zuwa wallahi sai na tura can kauyen Ubanki ki zauna a can naga dan iskar da ya isa dawo dake. Ko ance miki ban san me nake yi ba ne, tow ya isa haka ki kame kanki ko naci ubanki!" Tunda naji haka na rufawa kaina asiri, na nutsu ban san kuma me zance mata ba, na dai san tunda tayi haka tow ba makawa akwai wata a kasa. Abinci Uwani ta kawo min na fara ci, ta ce min. "Ki nutsu ki fahimci Mama, tunda kika bar gidan nan ta sauya daga yadda kika santa, a yanzu zata yi fadar nan ne domin darajarki idan ta kama ma auren ya mutu kada ki ce mata kome, tasan me take yi, kuma zata tsaya miki in sha Allah ita tayi alqawarin haka!" Haka yasa nayi bala'in nutsuwa tsoron Mama ya kara lullube ni. Kayan da nazo da shi na ja na fara budewa ga akwatin da Tinah tayi min tsaraba, budewa nayi na fara ciro kayan Mama ta shigo tana kallon Abincin.."Me ya hana ki cin abincin?" "Mama da zafi ne idan ya huce xan ci." Na fada ina cire kayan ciki ina ware tsarabarsu Mama. "Wai ma tukun gidan Uban waye kika je?" "Mama ina Ibadan wurin Tinah kawata din nan na abuja!" Ajiyar zuciya ta sauke, tana faɗin. "Kada ki kara min irin wannan abin da kika yi duk inda kika san zaki je ki gaya min na baki shawara!" Kallonta nayi kafin nace mata. "A lokacin kin ki saurarona ne!" "A yanzu xan saurare ki gaya min me wancan dan banza yayi miki?" "Mama ya wuce fa!" "Ai ba zaki gaya min ba!" "Idan na gaya miki zaki cigaba da tsanarshi ko don albarkacin su Mufid a kyale shi haka." Harara ta watsa min tana faɗin. "Allah ya kyauta!" Sai da na cire mata nata kason da turaren Baba Bulama, sannan na ware na mutanen gidan, wayarta da take gefen gado ta fara ƙara. Dauka nayi na bata ta saka a kunne. "Alhaji lafiya!" "Lafiya lau gani nan zuwa da Alhaji Kabiru." "Tow shi kenan!" Ajiye wayar tayi ta gaya min Babana yana zuwa. "Mama shima yayi fushi ko?" "Uwaki ban sani ba;" ta wuce waje kafin wani lokaci an kia abinci da ruwa da kome ni kuma nayiwa su Mufid wanka na shirya su, sannan na watsa tare da alola na fito na saka kaya na tadda sallah, a lokacin suka iso, Shigowa dakin Mama tayi ta dauki Yaran ta kai musu, ina idar da sallah tana kara shigowa. "Ki je can ki same shi, kuma wallahi kika sake kika bani kunya sai na zaune ki, domin na lura shi ta alakarsu yake da Uban Tafida ni kuma kece a gabana." Gyada kai nayi tare da barin dakin, koda na nufi parlour gabana ne yayi ta faduwa na rasa me ke min dadi, tsoro da fargaba yasa na kasa shiga, "eh tsayuwar me kike yi?" Inji Ummi da ta zo zata wuce. Taima tana bayanta. "Shiga" ta daka min tsawa, da sauri na shiga da sallama. "Ke kuma ki wuce wurin Maman Ummu gani nan zuwa." Ta wuce bangarenta, ni tunda na shiga da sallama na zube a gaban Babana. Murmushi yayi yana faɗin. "Bulama Yarka tana tsoron karya!" "A dai yi hakuri Alhaji!" "Tow Allah ya zauna da su lafiya, kiyi hakuri kowa hakuri ake akan zaman auren nan, yaushe zaki koma?" "Baba kayi hakuri ba zan koma ba don Allah!" Yadda nayi maganar yasa shi murmushi ya ce min."tow ba damuwa Allah ya yi albarka." Amin nace a raina, sannan ya min nasiha sosai kafin ya sallame ni, murmushi yayi ya cewa Baba Bulama. "Me kake ganin akan wannan lamarin?" "Alhaji a bar yarinyar tayi ra'ayin kanta, idan har yadda nake ji ne akan zamansu tow Ummu tana buƙatar nutsuwa sosai, Alhaji Muhammad Jadda mutanen kirki ne, amma iyalinsa basu da kirki don Allah kada aminta da alaƙarku yasa ka tauye mata hakkinta ka barta ita da mahaifiyarta su yi wannan yakin!"


Haka Babana ya mishi sallama akan ya bar mishi wuka da nama,.kome ya taso a gaya mishi.
***
*TAFIDA*
Lokacin da Hajiya ta dawo an cika a dakin yana jingine da bango Deen yana rike mishi da bowl na fruit. Ta shigo dakin tana me kallon rukayya, wuce su tayi sai da ta ajiye basket din ta nufi Rukayya ta kifa mata mari, sai da dakin ya dauka. Sannan ta kara kifa mata mari. "Tashi ki bar gidan nan ko na miki baki ki lalace!" Tashi tayi jikinta yana rawa, zata fita ta ce mata. "Hajiya me nayi don Allah?" "Zaki fito ko sai na hada ki da Allah!" Da sauri ta fita ta juya ga Sa'adiyya. "Ba ni na auro ki ba, amma ki saka kafarki ki koma wurin uwarki domin idan na ganki a cikin gidan nan sai ya sake ki har uku gara ya zauna babu mace da ya cigaba da zama dake!" Da sauri Sa'adiyya ta fita babu wanda ya ce mata cikanki. Abincin da ta zo da shi ta buÉ—e. "Hajiya kin je gidansu Ummu ne?" Murmushi tayi tana faÉ—in. "eh Safiyyudeen!" "Yau kan zanci abincin Mamanta!" "Ummu ta dawo ne?" "Eh ta dawo Tafida!" Murmushi yayi yana faÉ—in. "Shi ne baku gaya min ba!" "Tow ba gashi ka sani ba!" Abinci Hajiya ta zuba musu Maryam ta ce mata. "Hajiya akan me zaku mari Rukayya sannan ki kori Sa'adiyya?". Duk suka zuba mata idanu. "basu da hankali ne!" "Akan Ummu kenan don sun gaya min sun je gidan!" Zuba mata idanun Hajiya tayi tana mamakin yadda take shirin bin bayansu Rukayya. "Eh wani abu ne?" "Amma Hajiya yarinyar da ta gudu bata son zama da shi ne ake wannan hukuncin." "Eh saboda ita ne, da yau kun saka Tafida akan hanyan kun kaunaci Tafida Ummu ba zata yi tunanin barin shi ba, amma daga ke har rukayya kun mai da min Yaro saniyar tatsarku bukatar ranku yake kawo shi ga Tafida. Babu ruwanku da Yaranshi me yake ciki kawai kun samu wanda ya dauke muku bukatarku, shi kuma nashi bukatar ko oho, maza fita ki bisu Allah yana gani ban tab'a kin ku ba, amma akan Tafida sai inda karfina ya kare, ita Ummu zata dawo gare shi ko kuwa bana raye zata tallafe shi kamar yadda ta saba. Ku kuma ku je Allah ya kyauta!" Domin Mama ta gaya mata magana da yasa take jin ba zata iya kara barin Tafida ya rasa Ummu ba, koda kuwa haka zai zama ajalinta, ana cikin wannan yanayin Deen ya shigo, suka gaisa ya zauna yana korafi. "Hajiya tunda ya fara aiki bawan Allah nan ya manta da ni ya manta da matsayina, abu daya ya sani ya saka a kawo min aiki ya koma gefe ya cigaba da harkansu shi da Deen ban san bai da lafiya ba, tsabar wulakanci ban san Ummu bata gari ba sai da ya saka ana bincike, Hajiya tambaye shi me yasa zasu juya min baya?" Ya fada kamar zai yi kuka, "Kai tafi can ban manta da kai ba,aiki ya maka yawa nima aiki ya min yawa bamu da lokacin haduwa sai dare, Deen da kake gani shi nake gayawa Abubuwa masu muhimmanci ya rike min lokutansu sunan ina gwamna ne amma wallahi bani da lokacin kaina sai dare!" "Eh haka ne kinji ba Hajiya wai yana bawa Deen Abu masu muhimmanci ya rike shi." Cika cokali Deen yayi da abinci yana ci ya ce mishi. "ka taya shi murna Ummu ta dawo namu da kai yanzu bikon Ummu!"


"Da gaske?" "Kwarai da gaske!" "Masha Allah amma an san daga in take?" "Ko ina Ummu ta je, nayi Imani da Allah ba zata je inda zai zama wani abu else." "Eh haka ne kuma, Alhamdulillahi." Suka ci-gaba da hira.
**
*SA'ADIYYA*
Sa'adiyya bata saduda ba, kiran Smarty tayi ta gaya mishi rubutun da zai yi, sai da ya ji tsoron ya ce mata. "Gaskiya Hajiya na wannan aikin da hatsari!" "kayi kada ka damu zan tsaya maka, kuma akwai wanda zai wanke ka." Haka tai ta zuga shi har ya amsa mata ta bashi kudi me yawan gaske. Sannan ta zuba idanu.


A cikin kasa da awa 24 yaron nan ya birkita social media, wanda ya janyo cece ku ce, dama Wayar Tafida yana hannun Deen ya gani, don haka da kanshi ministry of Information technology, ya tsaya a babban hall dinsu ya zuba musu idanu. "On behalf of Borno state Government! Na zo ne a binciko min Yaron da yake rubutu na.baku awa biyu!" Ya kalli agogon hannun shi ya sakar musu murmushi ya cigaba da cewa. "Lokacin ku ya fara, idan kuka yi fail hmm! Ku saka a ranku aikinku nan amma kuma matsayinku zai ragu! A nimo min gurayen 2011 to 2013 maza ku fara aiki time dinku ya fara." Fitowa wasu matasa suka yi aka ajiye musu computer sannan ya koma gefe ya zauna, wasu dalibai masu sanin makaman aiki suma suka fito. Dayan su ya d'aga hannu ya ce." Yallabai wata uku da suka wuce na datsi IG din mataimakin IG na kasa, saboda ina son na dauko ni aikin yan sanda, Yallabai aikin da ka basu a cikin awa biyu ni zan maka shi a minti talatin! Idan an amince ni kawai aikin dan sanda nake so a dauke ni!" "Kai ku dakata, meye sunanka!" "Jabir Adam!" "Ku bashi!" Mika mishi computer aka yi ya zauna tare da cewa. "Yallabai ka saka lokaci!" "Lokacinka ya fara!" "A dakata!" Kallon MD na ministry din yayi yana faÉ—in. "Lafiya!" "Yallabai daga fadar abu sai a biye mishi! Ka mata yayi a fara jaraba shi tukun." Dariya yaron yayi ya ce mishi. "Tow ;" kafin mutumin ya cigaba da magana Yaron nan ya shige kan wayar MD tare da kwashe kome na shi na account dinsa.. "Yallabai ka ce mishi ya bude satar shi!" "Bude!" Ba musu ya bude datar. "Sunanka Haruna Gambo, kana da account uku, daya First bank. Daya UBA, kana da kudi a kowani account ka duba nawa ne a cikin suka rage, sannan kana da wasu hotona da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login