Showing 168001 words to 171000 words out of 241571 words
Chapter 57 - YAR MACE Complete Document hausa novels by Mai Damu.txt
Akwai kwallin mallaka
Zoben mallaka
Set na Jigidar mallaka
*Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbersππ»ππ»ππ»
07069711327 Whatsapp ,Ina maraba daku customersπππππ
Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mataπππππππππhttps://chat.whatsapp.com/DMCa4TXOqV712jNc1UBBRH
*Gidan zafafan kayan Mata masu kyau da inganci na yar mutan sokoto maman Yusuf likitar Mata,*
*Bayan kayan Mata muna tura abubuwan da zasu amfanemu game da Zaman auren da wasu magungunan da zaku iya hadawa da kanku da sauransu*
52
Shafa bayana take tana gaya min kalmai masu dadi da kwantar da hankali, nayi kukan da nasan in sha Allah ba zan kara yi, Tafida ya sake ni saboda rashin mutunci. Tafida ya cire min yarda da tsammanin duk wani d'a namiji, ya samin shakku da tsoron mu'amala dasu, shafa bayana take tana faΙin. "Kiyi hakuri Allah yana tare da masu gaskiya! Allah ba zai kunyata ba, kin rufa musu asiri suka nime tona miki Allah ya rufa miki asiri duniya da lahira, ya kuma miki sutura duniya da lahira." Addu'ar da Mama take min yasa naji kaina kamar an yanke min duk wani bakincikin rayuwa, amma mutuwar aure da ciwo, domin kuwa sai da na kwanta asibiti domin jikina rikicewa yayi, sai da na sha.
BakiΙaya ji yayi ina ma zai iya da ya ajiye mukaminsa ya huta, ya rasa waye zai taya shi jimami. Tsawon kwanakin nan yayi shine cikin tashin hankali, shi yasa ya rufe wayarshi ko taron gwamnoni da za ayi na arewacin Nijeriya bai samu zuwa ba amma yasan mataimakinshi zai je, haka yasa ya cigaba da boya, sai dai wani hali Ummu take ciki? Me yake faruwa dole ya koma gida dole ya je yaji meke faruwa, Ιaya wayar shi ya ciro ya kunna ya ga sakon Deen.
_Kana ina ne? Ina ka shiga? Me yasa kayi haka? Me yasa baka tambaye ni me ya faru ba? Aliyu kayi kuskure Ummu bata da nufin cin amanarka, Mahmoud yayi kokarin mata fyade ka kunna wayarka muyi magana_
Jikinshi na rawa ya kira kira Deen, layin bata shiga, gwada kiran layin gida yayi, ai kuwa ya dauka. "Safiyyudeen!" "Na'am Aliyu? Kana ina ne?" "Ina Abuja!" "Ok ka jira nima ina hanyar gidansu Tinah ne amma gani nan zuwa a ina kake nazo?" Nan ya gaya mishi inda yake. Sai da ya isa gidansu Tinah ya daukota suka zo Hotel din da yake, ya tara gashi yayi wani irin muni. Ko inda yake Tinah bata kalla ba, ta zauna a can tana shan ruwan da ta ganina dakin. "Why Tafida?" "Nuna min video yayi ya ce kuna cin amanata kai da Ummu!" Ya fada kanshi s sunkuye. Wani naushin takaici Deen ya zuba mishi a gefen fuskar shi, tayi ja kuwa domin sai da ya tintsira.
"Jaki kawai! Ka kasa bawa Ummu tsaro hatta matsayin da kake da shi bata da tsaro, ka gaza fahimtar da ita, girma da halaccin da tayi maka. Ka kwana da Saadiya daki daya ita ba yar wani ba ce? Ka yi soyayyar banza da Yaran mutane anan Abuja, ka zata wayo kayiwa Allah? Sannan don zalunci hatta fita unguwa sai da ka hanata saboda kada abin da kayi ya faru da ita! Ni da kai na gaya maka cewa kada ka sake Mahmoud ya samu mafaka a gidanka, ka da ka yarda Mahmoud ya samu inda zai zauna a gidanka alaka da duk za ayi ayi shi a waje. Karewa Mahmoud domin ya rufawa kansa asiri ya haΙa wanann rigimar, Tun a niman auren Ummu Mahmoud ya fara tanadin yadda zai lalata shirin Abba akanka. Tun daga nan lokacin Mahmud ya fara bibiyar Ummu, kayi ta cin mutuncinta kai hatta daren aurenku sai da Mahmoud ya bi Ummu akan ta kashe aurenka zai aureta. Ganin taki yasa shi har Abuja bika dan iska na zane shi wai ashe dan iska irinka ya bashi mafaka a gidanshi. Ban gaya maka gaskiya don na.wanke kaina ba na gaya maka gaskiya don na wanke Ummu daga zargin da kake mata kada ka lalata mata suna, Sannan ko Abba yasan abin da ya faru, amma ka rufe idanunka ka sake Ummu! Abba ya ce ka bani shaidar sakin domin mahaifiyarta tana bukata, sannan don Allah daga yau kada ka kara nimana a cikin rayuwarka, in har zaka iya rufe idanu ka zarge ni da shiga gonarka har abada babu amfanin na zauna da mutum irinka!"
"A'a Deen! Ba zan iya rubutawa ba!" Juyawa Deen yayi ya ce masa. "Shi kenan na isar da sako, Tinah muje na ajiye ki a gida yau zan koma Maiduguri!" "A'a muje ka kwana gobe sai kayi asubanci!" Ya dauki top dinsa ya fita ko ta kan Tafida da yake kiranshi bai bi ba, ya rabu da Tafida kenan na har abada, idan ya cigaba da zama da Tafida zai aikata mishi kome. Rike rigarshi Tinah tayi ta ce mishi. "Me yasa ka bayyana kanka idan ba taimakonshi kazo yi ba? Me yasa?" Murmushi bakinciki ya sakar mata ya ce mata. "Tinah ko mutuwa Tafida yayi Ummu ta haramta a gare ni, ba zan iya shiru na bar zancen bane, nayi mamaki da naji wai ni wancan dan iskar da na dauke shi kamar Hassan dina, yana zargina Tinah kin san yadda nake jin shi a raina kuwa? Ji nake kamar ciki daya muka kwanta! Gayen can ya sadaukar min da abin da ba zan iya sadaukar mishi. Tinah wancan gayen dan iska ne mara mutunci." Yadda yayi ta zagin Tafida, Tinah ta ce mishi. "Me zai hana ka rufe shi da duka?" Girgiza kai yayi yana faΙin. "Nayiwa Ammah alkawarin duka daya zan mishi, ba zan kara ba." "Tow ka yafe mishi aboki ne kawai zai iya maka abu ka yafe mishi matukar ya yiwa rayuwarka halacci a rayuwarka!" Cire madubin idanunshi yayi yana goge kwalla da ya zuba mishi. "Babana ya kasance drive babban mota ne" ya juya cikin dakin yana kallon Tafida. "Kaf unguwarmu Alhaji Muhammad Jadda kaΙai yake iya daukar abu ya bawa makota da mabukata! Babab Aliyu. Bayan haka ko a yaranshi Aliyu ne ya dauki wannan dabi'ar ya muku kyauta ba tare da kun tanbaye shi ba, unguwarmu ai kin ga shi unguwar masu kuΙi. Bayan rasuwar Babana rayuwa bata zo min da sauki ba lokacin muna ss2, wallahi abin da zamu ci ya gagare mu." Ya nemi wuri ya zauna yana juya kanshi, "Kannena mata biyu, Hajja da Jalilah, a lokacin matsi yasa Ammah kokarin tura Hajja aikatau, a lokacin na rasa waye zan gayawa ya hanata. Yan uwanmu kowa ya guje mu babu kowa, ana haka yarinyar nan ta fita dibo ruwa a gidansu Mahmoud." Cikin wani irin karfin hali ya d'ago yana kallon Tafida hawaye na zuba mishi sosai. "Wancan dan iskar gayen yana tsaye a kofar gidansu, ana dagga da shi ya tafi makaranta ya ga shigarta gidansu Mahmoud, tun yana tunanin zata fito domin Mahmoud amma shiru babu labarinta. Ganin haka ya saka ya kwasa da gudu ya shiga cikin gidan, bata inda ake diban ruwa, ashe tana shiga Babansu Mahmoud ya kirata yana." Kuka yake yana rufe fuskarshi. "Wai yaron nan don kutumar ubansa, ni yake zargi. Tinah koda ya shiga cikin gidan Mahmoud ya tafi makaranta, kai tsaye parlour Alhaji Abbas ya shiga ya samu mutimn nan ya saka Hajja a gaba tsirara. Mahaukacin nan bai yi tunanin kome ba, ya daki kan mutumin nan sai da ya suma, ya saka Hajja ta saka kayanta, bayan ya fito da ita da ruwan ya kawo gida. Ya samu ina mitan babu inda zata. Bai gaya min ba domin itama ya gargadeta kada ta gaya min. Haka tayi shiru, yadda yaga ina mita nan ya shiga min dariyar dole. Haka yasa ni a gaba sai da na gaya mishi. Abin da ya fada min cewa. Da akwai wanda yake son Hajja da aurar da ita aka yi, domin Hajja ta girma babu amfanin kaita aiki wani wurin, saboda ko babu kome zata tsira da rayuwarta da kimarta." Kuka Deen yake tafida ya mike tare da jingina da bango, wannan wacce irin abota ce haka. Take tambayar kanta. "Tinah kin zata a baki ya bani shawara? A'a yaron nan baya jin magana. Haka ya samu mahaifinsa da zancen abin da ya gani da kuma abin da Ammah take shirin aikatawa. Kasancewar baya jin magana tun muna Yara yasa mahaifinsa ce mishi zai yi kokarin ganin haka bai faru ba, muna zaune sai ga kayan abinci daga gidansu Tafida da cefane sannan shi Babansu da kanshi ya samu Ammah ya nimawa wani Yaron Abokinsa da yake aiki a London auren Hajja, a lokacin hajjar bata wuce sha uku ba, kuma da aka gayawa Iyayen Yaron suka ce dama suna niman y'ace suma gidansu duk maza ne idan ta shigo matsayin In-law ba zasu iya girmamata ba zasu so ta shigo a matsayin y'a a cikin gidan. Haka Tafida ya aurar da Hajja, tana nan a gidan mijinta da Yaranta hudu, maganar da nake miki Babban Yaronta ya shiga jami'a sunanshi Aliyu suna kiranshi jonior Tafida. Ya sani ya san tana nan, bata tashi gaya min ba sai da Aliyu ya bar Maiduguri wani zuwan da tayi ta gaya min abin da yayi mata, Tinah na kai ki da nisa, tun daga ranar da aka fara kawo mana abincin danye gida, har yau Alhaji Muhammad Jadda bai daina ba, muna cikin waec aka kawo form na scholarship committee na Borno, gidansu tafida aka kai, wurin Babanshi aka kawo saboda yana cikin manyan dattawan arewa. Koda aka bashi bai yi tunanin kowa ba sai ni, domin already ya biyawa Tafida makaranta a sudan. Saboda nayi wani shirme ni da Mahmoud, Deen ya wanke ni ya ce shi da Mahmoud suka aikata, aka rufe shi na dawo gida a daren Aka yi belinsa, yana zuwa gidan mu ya nufa ina kofar gida, sai da ya kai ni gaban Ammah ya dauke ni da mari. Ammah ki gaya mishi kada ya kara shiga sha'anin Mahmoud! Wallahi sai na karya mishi hannu da kafa ya zauna a wuri guda, da ace bana nan ya zaka yi da Jalilah kai na kuma ganinka tare da shi sai na maka dukan mutuwa, yiwa ammah sai da safe muka fito. Ya kalle ni ya ce min me zaka yi da kuke ni? Makarantar Jalilah zan biya kasan Hajja itama zaman wani take bata da shi balle ta bamu shi yasa Mahmoud ya ce na saci ragon. Nawa ne kudin? Dubu uku! Matsiyaci dubu uku yo ko a tsaye anan ina da dubu goma, dauka ka biya mata idan kana son kuΙi ka samu Malam bala yana min wani aiki, ba matsala zai na baka kada ka ji kome, Tinah wani irin aboki ya dauke ni? Tinah don kada nayi sata ya saka me musu bayin ruwa yana sayar mishi da karro, ake kawowa daga wasu jahohin, mutumin nan kasar kano ne, shi yake kawowa, Tinah Alhaji Muhammad Jadda ya fita hakkin Yaranshi tun daga kuruciya har girma domin har ni ya dauke nauyin karatuna, haka aka tura shi Sudan, daga ranar na fara bin malam bala kasuwar muna tare, har na samu scholarship na tafi Sudan nima, da kudin aka biya makarantar Jalilah, muka gama jami'a ni sai na koma kasuwar karo, tafida ya dauke takarduna ya mai da mu makaranta inda muka yi masters, a lokacin Jalilah ta ce zata shiga makaranta school of nursings borno, Tafida ya biya ban sani ba, don itama tafi sakewa dashi, sai da Ammah ta gaya min! Yanzu haka Brother dinsa Alfah yake sonta, amma na rantse miki da Allah ya mishi warning kada ya sake ya yaudare ta domin zai yanke mishi gabanshi ya ga yadda zai auri wata yar iska. Tinah farkon nimawa Tafida Mata ina tare da Babanshi, yana ganin Ummu ya ce min kai duba zata yiwa mahaukacin Abokinka? Ina ganin Ummu naji Tafida ya dace, na ce mishi na amince." Numfashi ya sauke yana kallon Tinah da take hawaye ya ce mata. "Akwai wani Malami mutumin Abba me sosai, lokacin da Tafida ya dauko rashin ji bani mantawa saboda kin.ga shi kome nashi kai tsaye yake a gaban Uban kowa, ni kuma ba zan iya yin haka ba saboda bani da confidence! Shi mahaifinsa mai kudi ne kuma babba ne ni talaka ne fut idan na ce zannyi wani abu tafida ma b zai bari ba zai ce zan saka Mamana cikin tashin hankali. Babansa ya kai ni wurin Malamin ya nuna mishi ni ya bashi labarin kome, murmushi Malamin yayi ce shiga tambayana ina bashi amsa, bayan wani lokaci ya ce min. Gobe na je, haka kuwa washi gari na koma yana ganina ya b'ata rai ya ce min. Kasan Tafida bai da matsala me yasa baka gaya min a gaban Babanshi ba? Me yasa ba zaka iya taimakawa wurin gyara dabi'arshi, yana sonka kuma zai yi kome domin ka, kayi mishi alfarma mana!!" Ya d'aga kai sama yana jin hawaye na zuba mishi. "Tun daga ranar na daura dammara akan Tafida. Tinah bana son tashin hankalinsa har yau da nake gaya miki akwai mutane dayawa, da suke son ganin bayan Tafida amma kasancewar muna da shi babu wanda ya isa ya mishi wani abu, wannan sara da sukar domin na cika alkawarin da na dauka na tsaya mishi, ga Yarinyar ta shigo rayuwarshi nasan hatta familynshi wasu basu dauketa mutum ba, saboda wannan dan iskan bai mutunta ba, Tinah da a ce ina son Ummu na gaya mishi gaskiya wallahi sai ya sake ta kome za ayi mishi ya aureta, Tafida yayi min min abubuwa dayawa, Mijin Hajja yaso wulakantata saboda zai kara aure nake gaya mishi, kin san kiran shi yayi a waya ya mishi warning tare da gaya mishi matuΖar ya sake ta yi kuka akan aurenshi sai ya biyo shi har London, ba kudin Tafida yasa nake manne da shi, sadaukarwa da yayi min ya wuce na fada, amma na hakura abotarmu, alakarmu, amintarmu na hakura da shi, zargina yaΖe zargina dan iskan nan yake ba kara ganinka a kofar gidansu sai naci mutuncinka, kayi sha'aninka nayi nawa, kuma ka nisanta kanka da Ummu Hadiyya, in sha Allah sai Allah ya bata wanda yafika, wanda zai kula da ita wanda zai sakata farinciki." Ya juya tare da barin dakin.....
π« LITTAFINA NA KUΖI
500β¦
8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay
Shaida biya a turo ta wannan numbers din.
+2347035133148
Or
+2348130269641
Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76
πΎπ»πΎπ»πΎπ»πΎπ»πΎπ»πΎπ»πΎ
*_GYARA SHINE MACE_*
*_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_*
πΎπ»πΎπ»πΎπ»πΎπ»πΎπ»πΎπ»πΎ
*_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327
*Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*ππ»ππ»ππ»ππ»ππ»ππ»
Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku kula,
Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,π
Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu ajiπ
Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin kiπ
Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai ,
Mmn Yusuf likitar Mataππ
Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin saukiπππ
Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babukuπππππ
Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima
KADAN DAGA CIKI WASU KALOLINππ»ππ»
Kalolin gumba
Kalolin matsi
Kalolin gari
Kalolin tsumi
Zumar dabino
Zuma Mai rubutu
Zumar goron Tula
Zumar ridi
Dahuwar kaza
Dahuwar zabo
Dahuwar zuciya
Dahuwar ciccibi
Dahuwar tsoka Tara
Dahuwar Yan shila
Dahuwar kwai Mai rubutu
Turaren mallaka
Turaren Mara
Turaren tsugunno
Turaren k'irji
Shuumar humra
HATSABIBI turare
Hatsabibiyar humra
Matan gaske
Maltinat Mata
Shayin Mata
Tsumin kankana
Sirrin tafin k'afa
Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini
Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta