Showing 327001 words to 330000 words out of 411050 words
Chapter 110 - MAFARI COMPLETE BOOK HAUSA NOVELS BY UMMU MUAZ.txt
yadda ake tafiyar da Miji .
Hafsa ita ta rage dariyar ganin yayan su na tsaye yana kallon su , ita ma sai ta ɗan ɗaga murya lokacin da take miƙewa tsaye tace , "Ƙanwata Amarya ki fito kuyi sallama big bro zai tafi idan kuma ma mu kike jin kunya , kun ga ku zo mu bar wajen tace da sauran 'yan uwan ta , nan take suka miƙe suka yi ɗaki suna ƴar dariya tare da sake yiwa yayan su fatan Allah kiyaye hanya ,
Doctor Hamza da yake tsaye hannun sa a zube cikin Aljihun rigar rigar jumfa jikin sa , ya ɗan gyaɗa musu kai da murmushi a fuskar sa , shi ɗaya ne ƙwal ya rage a falon .
Ganin sa ya mayar kan ƙofar ɗakin Hajja lokacin da Yakaka ta buɗo ƙofar ta fito kan ta a ƙasa fuskar ta kadaran-kadahan , ɗan matsawa kaɗan tayi ta bayan kujerar falon ta ɗan durkusa , " ina yini yaya dakta ,
Bata jira ya amsa ba ta ƙara da cewa " Allah ya kiyaye hanya ,
Bata yarda ta dubi sashin da yake ba bare ta san cewa ya matso kusan ta sai da ta miƙe tana shirin wucewa ta shige ɗakin su da yake kusa da ita , sai kawai ta ji ya riƙo hannun ta ,
A hankali ya jawo ta ya kusan haɗe jikin su , hannuwan sa yasa ya kewaye kunkumin ta , yana kallon fuskar ta da taƙi yadda ta ɗago kai , muryar sa ƙasa-ƙasa yace " haka ake yin sallama ? Babu addu'a ? Baki ji Hajja tace ki min abunda zai bani kuzari bane ?
Da sauri ta ɗago kai , signal ya mata da duk girar idanunsa biyu , yana 'yar dariya da fararen haƙoran sa da suke da kyau sosai akan fuskar sa mai rangwamen haske .
Ɗauke kai Yakaka tayi gefe can cikin ranta tana mamakin meyasa ta hango kamar sauyin mu'amala a tare da shi daga jiya zuwa yau ? muryar ta cikin sanyin tace " ai nace Allah ya kiyaye hanya na yi addu'a ,
Hannun yasa ya sake juyo da fuskar ta saitin sa , ya zarce da sanya ɗan yatsan sa ya shafa saman idon ta , da yasa Yakaka ta lumshe idanun ta da sauri , " Ya idanun ki sun wuce ko ? Basu sake damun ki ba ko ? Ya tambaye ta da ragwan sauti ,
gyaɗa kan ta tayi tana ƙoƙarin kautar da fuskar ta , amma ya ƙi bata damar haka sai ma hannuwan sa duk biyu da yasa ya tallafi fuskar ta yana shafa kumatun ta masu taushi yace ," to ina saurarar ki ki min Duas kuma ki min abunda Hajja tace ki min , ko bakya so na samu kuzarin tuƙin ne ?
Sallamar wata baƙuwa ya sa Yakaka ta fisge jikin ta da ƙarfi da daman baki ɗaya a takure take damar gudu take ta son samu ,
Sai dai bai bata damar gudun ba ya riƙe hannun ta lokacin da suke gaisawa da matar ya san ta ɗaya daga cikin mutanen Amnee ce , ta zauna akan kujera.
" Ba za ki min Duas ɗin ? ba yace yana jaan hannun Yakaka su fice daga falon , babu yadda ta iya ta bi shi sai dai suna fitowa suka hango Amnee na tahowa daga sashin Baa ,
" Yaa Doctor Allah ya kiyaye hanya ya kai ka lafiya , ya kare ka , ta harhaɗo kalmomin cikin sauri tana ƙoƙarin kwace hannun ta daga cikin nasa , kafin ƙarasowar Amnee ya sake ta da sauri ta taka tana komawa ciki , da murmushi ya bi bayan ta da kallo wani irin nishaɗi ne mai daɗi yake huɗa shi .
Ƙarfe uku ya ɗau hanyar Abuja tare da sofiya wacce ya biya gidan su ya ɗauke ta dole bayan ya mata jaan ido tare da barazanar barin ta ta cigaba da zama a gidan su na wasu kwanaki da take son yi dai-dai yake da rabuwar su baki ɗaya , jin haka ba shiri ta tattaro ƴan kayan ta ta bi shi, ba tare da ta kula Momy kori sun yi wata sallamar kirki ba saboda haushin ta da momy kori take ji .
ASSALAM ALAIKUM MASU KARATU DA FATAN KUNA LAFIYA ?
INA GODIYA DA YADDA DAI HAR KULLUM KUKE HAƘURI DA NI .
INSHA ALLAH SHAFI NA GABA SHINE ƘARSHEN LITTAFIN MHR DA ZAI BIYO BAYA NAN BA DA JIMAWA BA.
NAGODE
[2/5, 10:29 PM] Zuraiyah Zuzu 🌟: MAFARI
( Hargitsin Rayuwa)
Umm'muaz
49
MARADI-NIGER
Kwanakin da suka biyo bayan bayyanuwar mummunan aikin da Gimbiya maimounatou ta aikatawa Biyamuradi Youssouf , tare da sa hannun Mammadou da Hajiya Mama ,
Masarautar maraɗi ta kasance cikin alhini mai tarin yawa , kusan kullum aka yi zaman fada da Waziri ne ke jagoranta ba'a da wani batu da ya wuce na sake tattaunawa kan wannan mummunan lamari haɗi da yiwa Biyamuradi Addu'ar samun lafiya tare da fatan dawowar Maimartaba .
Da har yau da suke cika kwanaki ishirin da ɗaya basu baro india ba , Amma ana saka ran dawowar tasu a yau ko gobe saboda saƙon yiwuwar dawowar tasu ya iso musu .
Akwai labari daga majiya mai tushe cewar gimbiya Siyama tare da ƙanin Biyamuradi Youssouf , 'Bilal wanda shine mai binsa a haihuwa sun fara shirin tafiya India domin cigaba da jinyar sa da har kawo yau babu wanda yasan takamaimai a halin da lafiyar Youssouf ɗin ke ciki .
Ta ɓangaren Hajiya Mama kuwa duk yadda ta kai ga sanyawa idanun ta toka ta mustsiƙe ta cigaba da yin harkokin ta yadda ta saba , amma ta gagara domin yadda labarin sa hannunta da na ɗan ta wajen yunƙurin kisan da Matar Biyamuradi tayi masa , ya bazu ba a bakin bayu da hadiman cikin masarautar Maradi kaɗai ba har jama'ar gari da na wasu jahohin labari ya kai musu .
Ake kuma kucin-cina labarin tare da sake liƙa masa baƙaƙen sassa ana sake munana sa ba ƙaramin tasiri hakan yayi wajen kassara mata duk wani karsashi haɗi da ɗagawar da take tinƙaho da shi na kasancewar ta matar Sarki .
Dan haka gaba ɗaya sai take neman zama mujiya , tsarguwa take da irin kallon da bayun gidan suke mata , gefe guda ga dumuwowi birjik da suka mata ƙawanya , wanda bata saba shiga makamantan su ba , mafi girman su halin da ɗan ta tilo namiji yake ciki wanda yake tamkar ga ƙoshi ga kwana yunwa a wajen ta , domin kuwa tasan muddin Youssouf ya rasa ransa, cikin hakan akwai yiwuwar shima Mammadou ayi masa huƙunci mai tsauri da ka iya kawo ƙarshen shima tasa rayuwar .
Ga Maimartaba da bata san matsayin ta takamaimai a wajen sa ba , bayan tonon sililin da Maimounatou tayi mata a gaban sa , gefe guda kuma ga Mairamar sarki da take autar ta sannan mafi soyuwa a wajenta cikin 'ya'ya da tun bayan faruwar wannan lamarin da ta samu labarin kome bayan kuka bata wani taɓuka abun kirki ,
Rufe kanta take a ɗakin ta da yake sashin uwar-riƙon ta , ( Hajiya Umma ) ta ci kuka ,domin lamarin ya mata tsauri wajen ɗauka duka biyu a lokaci guda ,
dan kuwa bayan kasantuwar Youssouf yayan ta mafi kusanci da yawan ƙauna a tsakanin su fiye da duk sauran 'yan uwan ta , ta shaƙu da shi tunda ta buɗi ido ta ga kanta riƙe a hannuwan sa , shiga hatsarin rasa shi ba abune mai sauƙi a wajen ta ba .
Damuwar ta tana sake hauhawa da hango rugujewar zancen auren ta , tare da ma guntilewar alaƙar su ita da masoyinta da suka ɗibi tsawon shekaru uku suna soyayya wanda yake yaya ne ga gimbiya Maimounatou , uwa ɗaya uba ɗaya gaf ma ake da yanke ranar auren su cikin watannin gaba kaɗan a sha biki , sai ga shi wannan mummunan lamarin ya shata layi a tsakanin su , domin kuwa ko ba'a sanar da ita ba ta san makomar soyayyar su ita da Khaalifa , sannan tun kafin a hana ta ita ya kamata ta fara zare soyayyar sa daga ran ta , bayan abunda ƙanwar sa ta aikata ga Biyamuradi ai babu wani sauran alaƙa mai girma da zai sake shiga tsakanin masarautun nasu biyu .
Ba tun yau ba ta riga ta san wasu daga cikin munanan halayen Mahaifiyar su da ita koyaushe huɗubar ta tare da yunƙurin ta bai wuce na ganin ta raba kyakkyawar alaƙar da ke tsakanin ta da uwar-goyon ta tare da sauran ƴan uwan ta da suka haɗa uba ɗaya ba ,
da ita kuma ko kusa bata ganin aibun su , sannan duk wasu laifuka nasu da hajiya Mama ke faɗin sun aikata ko suna kan aikatawa , ita bata kai ga kama su da ko guda ba dan haka koyaushe take biris da huɗubar ta , tare da toshe kunnuwan ta , ƙaunar ƴan uwanta a jinin ta yake tana ƙaunar su kwatankwacin ƙauna tare da zallar kulawa da su ma suke nuna mata a matsayin ta na ƙaramar ƙanwar su ,
ga hajiya Umma kuwa ba zata ce kome ba da ya wuce fatan alheri tare da godiya ,riƙo ta mata na haƙiƙa ba irin riƙon ƴar kishiya ba , dan haka take jinta basu da wata maraba da Hajiya Mama , sau dayawa ma tafi kusanci da Hajiya Umma akan ita Hajiya Mama ,( goyo guba )
Amma ace sanadin son zuciya irin na Hajiya Mama duk ta rusa mata farin-cikin ta a lokaci guda ? Gani take kamar Hajiya Umma da sauran ƴan uwan ta duk zasu tsane ta akan laifin Mahaifiyar ta da ɗan uwanta , a tsakanin hakan take yawaita tambayar kanta anya kuwa tayi sa'ar uwa ???
An cigaba da tsare Gimbiya Maimounatou tare da Mammadou a Niamey , saboda rashin sanin halin da Youssoufa ke ciki ya hana a tura su ga kotu ,
kawo yanzu kuwa Mammadou iyakar nadama ya yita , ko abincin da ake ɗan kawo masa , baya iya ci duk ya lalace yayi duhu , bai taɓa zaton akwai wani lokaci da zai zo yayi danasanin zazzafar ƙiyayyar da yake yiwa ɗan uwan sa ba irin wannan lokacin da ya sarƙe cikin sharrin Gimbiya Maimounatou da ta tsaya kai da fata kan shi ya kawo mata gubar da ta ciyar da Youssouf da a zahiri ba gaskiya bane ba shi ya kawo mata ba ,ba shi kuma da wata masaniya akan haƙiƙanin me ya faru ga Youssouf a wannan daren , iyakar abunda ya sani shine yaje gidan Youssouf mintoci kaɗan bayan ƙiran sa da tayi saboda kusancin da yake tsakanin gidajen nasu biyu da wuri ya isa , ƙarƙashin jagorancin gnala da ta tare shi tun a babbar ƙofar gidan ya cimma har falon da Youssouf ke yashe a ƙasa cikin halin fitar hayyaci , a lokacin shi da kansa ya shiga ruɗani ganin halin da ɗan uwansa ke ciki , a ɗimauce ya shiga tambayar gimbiya Maimounatou
" Ya mutu ne ?
Da gaske Youssoufa ya cimma kushewa tai ?
Bai gama tantance da abunda ke faruwa ba lokacin da suka tsinkayo jiniyar 'yan sanda ,
Kallon-kallo aka yi tsakanin su ukun , da ruɗani ya bayyana a fuskokin su sannan da wani irin sauti Gimbiya Maimounatou tace ,
" Mammadou ka shigo da ha'inci cikin lamarin mu amma kayi kuskure ka kuma yi shuka a idanun maƙwarwa , muddin kuwa baka yi wani yunƙuri ba tarkon da kayi na iy afkawa har da kai da makusantan ka ,
Cikin ruɗewa yace ,
"ki bar surutan banza ki faɗi wanne tanadi kika yi kafin ki aikata wannan aikin domin nayi gaugawar shafe girman laifin ki kafin lokaci ya ƙure miki , ko kin manta Yarima ɗiyan sarki kin ka kashe ?
Kafin yin wani yunƙuri mai girma jami'an tsaron da bai kai ga tantance kakin soji ne a jikin su ko kuwa na 'yan sanda ba , suka dunga tururuwar shigowa falon kafin ya farga sun cika falon , bai shaida fuskar ko ɗayan su ba , sai fa Tafeeda da shi kuma tun shigowar sa ya rufu ga Youssoufa bakin sa ɗauke da sallalami gami da addu'o'i .
Hanjin cikin sa ya kaɗa lokacin da ya lura jami'an tsaron wajen riƙe suke da bindigogin su da suke ɗane a saitin su shi da gimbiya Maimounatou , tsoro mai girma ya ziyarce shi lokacin da ya farga da tsaka mai wuyar da yake ciki , da dukkanin alamun da suka bayyana ya taka sawun ɓarawo .
masaniyar sa ɗaya shine yasan gimbiya maimounatou tana da mummunar manufar kashe Youssouf tun shekarun baya da ta taɓa furta musu hakan shi da Hajiya Mama lokacin da suka yi wata ganawa ta sirri da su da ita wanda a lokacin suka haɗa hannu wajen ganin sun kai Youssouf ɗin ƙasa da shi da Hajiya Mama ba burin su kashe shi ba , ( kashe shi abune wanda ba sa hangowa kansu hanya mai ɓillewa ta nan ) kwaɗayin su tozarta shi suke irin tozartuwar da zata kai shi ga rasa damar sa ta hawa ƙaragar mulki burin su ya bar nahiyar su yayi nesa da sarauta , yayi rayuwa mai cike da baƙin-ciki tare da rashin nasara to ko'ina Mulkin Maradi ya zama na Mammadou .
Ga rashin sa'ar su sai ta ritsa da su munafunci shi ai daman dodo ne ubangidansa yake cinyewa , Mammadou ba shi da wata kafar kufcewa daga zargin da yake ciki , Maimonatou kaɗai ita ce ke iya fidda shi ita kuwa bata shirya hakan ba ,
kafin a raba musu ɗakin da ake tsaron su cikin a cikin sa , babu irin roƙo da magiyar da bai mata ba kan ta tausaya ta faɗi gaskiya , amma tayi funfurus sai yaɓa masa baƙaƙen kalmomi masu cike da raini take yi wanda a lokacin shi basu ishe shi sauraro ba bare yayi hanƙoro akai , nadamar son zuciyar da ya aikata cikin kowanne sa'a guda na sake yi masa dabaibayi .
Gimbiya Maimounatou kuwa ? Zuwa yanzu lamura sun fara zuwa saɓanin tunanin ta , dan kuwa har kawo yau da take cika satika uku , sau ɗaya bata ji daga wani nata ba wanda kuma tana da masaniyar tuntuni labari ya je musu , to yaya haka ta kasance mata ? Tana sane ko kowa ya iya kauda idanunsa daga gareta sakamakon laifin da ta riga ta aikata , Abban ta ba zai iya ba , saboda sanin da tayi tauraruwar ta ta ɗara ta kowa haskawa a zuciyar Mahaifin su sumfurin ƙaunar ta kuma mai banbanci ce da ta sauran ƴaƴa , duk kuwa da kasancewar ta ɗiya mace ,
Tun tana sanya ran za'a buɗo kofa ace ta zo ga Maimartaba mahaifinta yazo ganinta da kansa ,tare da Mahaifiyar ta , daga nan ta san zasu nemi belin ta tana da tabbacin za'a basu idan yaso daga baya sun haɗu a kotu su da mutanen Youssoufa da take jin ba wani nisa shari'ar zata yi ba za'a kawo ƙarshen ta sanin da tayi tasu masarautar ai tafi ta su Youssoufa ƙarfi har ma da dukiya .
shiru ya tsawaita babu wani motsi daga iyayen ta .
ta sassauko burin ace ko da wani daga cikin tarun yayyunta maza da mafi yawa basu wani cika shiri da ita ba musamman waɗanda suke yan uba , amma duk da haka tana harin ko uku daga cikin ne su zo ko da kuwa ace zasu ƙare mata zagi, ita dai ta yadda su zo su ƙarbi belin ta .
Har ta kai cikin ƴan kwanakin nan ta fara burin ina ma da ace ko da wani babba daga cikin masarautar su ne ya zo ganin ta ? ko da ace bai nemi belin ta ba ya jishe ta labari na daga abunda ke faruwa ga iyayen ta da ma masarautar su baki ɗaya da yasa suka yi watsi da ita a cikin wannan maƙasƙancin wajen da yafi dacewa da wajen hora maƙasƙanta daga cikin bayun ta .
Jita-jita ya kasance gaskiya domin kuwa a daren ranar Maimartaba sarkin Maradi tare da Hajiya Umma suka dawo cikin masarauta .
Da dawowar su bai fi da awa guda ba labarin samun lafiyar Biyamuradi ya kewaye masarautar , inda ake da tabbacin farfaɗowar sa daga magagin ciwo sai dai an yi masa aikin da yasa zai ɗan sake yin wasu kwanaki a can ƙasar India kafin ya warke baki ɗaya ya dawo .
Tamkar rana haka masarautar ta ɗauki murna har da ƴan bushe-bushen algaitu na bayyana jin daɗin samuwar lafiya ga Biyamuradin Maraɗawa wanda tamkar hatsarin rasa shi da aka shiga ne ya wanke duk wasu laifukan sa na baya da ake ganin sa da shi tare da haɓɓako da ƙaunar sa a zuciyoyin Al'umma .
ruwan ƙiyayyar kuma da ganin aibun sai yayi tsallen alkafira ya wanke Hajiya Mama tare da Mammadou , ta ukun su Maimounatou babu wasu abun aibatawa da ya wuce su lungu da saƙo na birnin na maradi murnar dawowar Maimartaba ake tare da farin-cikin jin cewa Yarima yana samun sauƙi .
Siyama wacce tunda Hajiya Umma ta shigo sashin nata da daman ita ma tun bayan faruwar lamarin ta baro ɓangaren gidan su ta dawo ɗakin ta da yake sashin uwar riƙon ta ,
Ita ta bi bayan Hajiya Umma har zuwa ƙuryar ɗakin ta ta kuma shiga Hidimar abincin Hajiya Umma , tana sauraron duk wasu amsa waya da Hajiya Umma ke yi da 'ya'yan ta da sauran jama'ar ta , da duk dai batu ne kan samuwar lafiyar Youssoufa , cikin wayar ne ta ji Hajiya Umma na lissafa sunayen waɗanda zasu tafi India domin cigaba da zama da Youssoufa na ƴan wasu satika kaɗan nan gaba , ƙannen sa maza biyu kawai ta lissafa bata ji sunan ta a cikin masu tafiyar ba.
amma duk da haka zuciyar ta cike take da farin-cikin jin lafiya ta fara inganta ga Mijinta , bayan irin tashin hankali