Showing 363001 words to 366000 words out of 411050 words

Chapter 122 - MAFARI COMPLETE BOOK HAUSA NOVELS BY UMMU MUAZ.txt

10 Sep 2025

20141

bata taɓa zaton sharri da muguntar Hajiya Saratu , bayan irin mummunan asirin da ta yiwa ɗan ta har ya kai da zata iya enlevé surukar ta ?? Wacce irin ƙiyayya ce wannan Hajiya Mama take mata ?

Da hannu Hajiya Umma ta ƙira Ubbo da Siyama waɗan da suma suke tsaye kasaƙe kamar ruwa ya cinye su tace " ku kama ta zouwa sashi na .

Cikin sauri Youssouf ya girgiza kai kafin yace " zan tai da ita da kaina.

Gyaran murya Maimartaba yayi kafin yace

" bar su su tai da ita kai kouma ka biyo ni .

Daga haka ya juya bayu da sauran al'ummar gidan da har kawo yanzu babu wanda ya iya cewa ƙala wasu suka rufa masa baya .

Youssouf bai saki hannun Falmata ba duk da cewa tun da ta ji muryoyin mutane a wajen ta raba jikin ta daga na shi amma ya ƙi sakin hannun ta .

Har Sai da Hajiya Umma ta kama hannun Falmatan ɗaya ta rike sannan tace masa " ka tai ga ƙiran Mahaifin ka , itta tana ƙarƙashin kulawata .

A hankali ya miƙe yana waiwayen Falmata da ta sunkuyar da kan ta ya fita zuciyar sa cike da jin tausayin falmata da ya lura har rama tayi ta fita a kamannin ta duk wai a sanadin sa Hajiya Saratu ta mata haka ?

Ubbo da kan ta ta haɗawa Falmata ruwan wanka kamar yadda Hajiya Umma ta umarce ta ,

Hajja wacce yau ta samu damar shiga har uwar ɗakin Hajiya Umma tana sharar hawaye tace " mu je na gasa miki ƙafar ta ki uwarɗakina ko kya ɗan ji daɗin ta sannu kin ji Allah ya miki sakayya .

Hajiya Umma da take kallon Falmata cike da tausayi cikin ran ta wani irin yanayi take ji zuwa yanzu ta fara yarda da cewa kamar da sakacin ta har Hajiya Mama tayi nasarar kama Falmata yarinyar da zuwa yanzu ta fahimci da ita da danginta baki ɗaya basu da wata alaƙa da halin da rayuwar ɗan ta ya kasance a ciki kamar yadda take zato a baya , ashe Hajiya Mama ita ce mafarin kome ba Falmata da 'yar uwar ta ba .

Fuskar ta bata ɓoye halin da zuciyar ta ke ciki ba tace " kar a taɓa mata ƙafar za'a ƙira mai gyara yazo ya duba idan ma kuma asibiti za'a kai ta sai a tafi .

Ɗan lankwasa kai Hajja tayi tace "to bari a jira , O' ni hauwa'u yau na ga kura da fatar akuya ganin idona , wasu mutanen launin hankaka ne da su gaban su fari bayan su baƙi ai ba ƙaramin marar imani bane zai yi kinnafin ɗin ɗan adam ba , yo ai tazarar da take tsakanin kinnafaa da boko haram kaɗan ce , Allah ya raba mu da miyagun mutane .

A hankali Hajiya Umma ta amsa da "Amin dai , tana mayar da kallon ta kan Hajja.

A can ɗakin ganawa ta musamman Maimartaba tare da manyan mutanen Fada nasiha suka dunga yiwa Biyamuradi Youssouf suna tausar zuciyar sa , sun gwada masa girman haƙuri tare da matsayin da mutanen da Allah ya yiwa baiwa da haƙuri suke shi tare a gurin sa

da kusanci da haƙuri ke kawo wa tsakanin Mutum da Mahalccin sa Sannan suka jawo masa ayoyi da hadisai .

A ƙarshe suka bashi tabbaci kan cewa jarabawar Rayuwa ce Allah ya masa domin ya gwada ƙarfin imanin sa dan haka ya bar kome ga Ubangiji da idanun sa zai ga sakayya .

A hankali ya dunga jin nutsuwa na safko masa da kafin wani lokaci ya ji baki ɗaya zuciyar sa ta sauƙa wani irin nutsuwar da ya jima bai ji irin ta ba tana safko masa .

Liman da yake malami masanin Alkur'ani ya cigaba da cewa

"sannan shi sihiri gaskiya ne da masu aikata shi kaɗai suka yi imani da shi ,

"babu shakka cikin kur'ani duk wani magani da warakar kowacce cuta yake dan haka ga ayoyin Alkur'ani masu warware sihiri zan faɗa maka idan za ka iya kayi da kan ka Yousssouf idan kuma ka gaza ka bayar a yi maka ina mai tabbatar maka da cewa dukkanin wani sihiri da anka maka sai ya karye da iznin Allah sannan kuma Allah zai baka kariya daga dukkanin wani mgunta da za'a sake nufar ka da shi ta hanyar sihiri ba zai yi tasiri akan ka ba, ka samu takarda da alƙalami ka rubuta a yanzu Youssoufa ayoyin sune kamar haka :


1). Ta'awwizi da Basmala.

2). Fatiha kafa 7.

3). Aya biyar Ta farkon Suratul Bakara sau 7.

4). Ayoyi biyu ta tsakiyan suratul Bakara wato - Wa ilahukum ilahum wahid la'ilaha illa huwa har karshe sau 7.

5). Ayatul kursiyyu Suratul Bakara aya ta 255 sau 7.

6). Ayoyi uku a karshen Suratul Bakara wato daga baikin Amanarrasul Bakara 284-286 sau 7.

7). Shahidallahu a chikin Al Imran aya ta 18 da 19 sau 7.

8). Inna Rabbakumullahi Ladhi khalaqas samawati wal ardh.. acikin Suratul Al'araf aya ta 54 da 56 sau 7.

9). Afa hasibtum Annama khalaqanakum Abasan suratl Mu'minin aya ta 115 da 118 sau 7.

10). Wa Annahu ta'ala Jaddu rabbina mattakhadha..." a cikin Suratul Jinni aya ta 3 zuwa ta 9 shima kafa 7.

11). Aya goma na farkon Suratul Saffat shima sau 7.

12). Aya Uku na karshen Suratul Hashri wato "Lau anzalna hathal Quran.

13). Aya ta 10 na karshen suratul Yasin su ma sau 7.

14). Kulya ayyuhal kafirun sau 7.

15). Qul huwallahu ahad sau 7.

16). Falaqi sau 7.

17). Nasi sau 7.

A rika tofawa a ruwan zamzam ko ruwan sama ko ayi a duka biyun amma dabam dabam a samo ganyen magarya a dandaka guda bakwai-bakwai har gida 7 wato na kwana 7 Safiya da maraice ana sha ana shafe jiki dashi.


Da fatan ka Fahimta Yossoufa ? Sannan a kome kake kada kayi wassa da ibadar ka domin itta ɗin kariya ce mai girma daga dukkanin abun ƙi , ka faɗaɗa ibarda ka yalwata ta , sannan ka yawaita sadakha domin ita ma kariya ce .'

Youssouf da yake gama rubutu ya ɗago kan sa fuskar sa a nutse yace" na fahimta Malam kuma Nagode Allah shi saka da alkhairi .


Daganan ya baro sashin maimartaba bayan ya musu godiya mai tarin yawa , ya bar su suna cigaba da tattunawa .

Sashin sa ya nufa kai tsaye yayi wanka ya ɗaura alwalar sallar la'asar zuciyar sa da take cike da tausayin Falmata da son sanin halin da take ciki ta sa shi dole ya miƙa hanya zuwa sashin Hajiya Umma .

A zaune ya tarar da Hajiya Umma , a falon ta na ciki da Hajja sai kuma Ubbo suna sake jimamin lamarin banda ɓarin nauyayan kalmomi babu abun da Hajja take yi da lokaci-lokaci ubbo kan yi dariyar wasu kalmomin na Hajja .

Zuciyar Hajiya Umma ta sanyaya da ganin Yousouf ya dawo cikin nutsuwar sa har ma ta gagara ɓoye jin dadin ta .

Tayi hamdalah a bayyane .

Bayan sun gaisa ta ɗan dube shi kafin tace " ƙafar Fatima da akwai ciwo domin kouwa da kyar take iya takawa duk da dai na mata tambayoyi cikin amsar da ta bayar tacce bata da wata damuwa sai ta ƙafar da daman akwai tsohon targaɗe a gurin kuma ta sake gurɗewa dan haka nayi magana a ƙira mai gyara a duba ƙafar ko kuwa asibiti za'a ?

Cike da jin daɗin kulawar da ta nuna a karon farko ga Falmata , Youssouf yace "duk wanda kin ka ga yafi dacewa Umma.

"Ka shiga ciki ka gan ta suna ɗaki tare da Siyama.

A bisa ɗaya daga cikin gadajen Hajiya Umma biyu da suke ɗakin ya hango ta a zaune tayi wankan ta fes jikin ta sanye da doguwar riga ta atamfa daga gefe Siyama ce a kusa da ita hannun ta riƙe da wani ɗan kyakkyawan tasa ( Bowl ) da aka zuba ferfesun ƙaza a ciki da chokala biyu a ciki fork da soup spoons,

Ganin shigowar sa bai sa Siyama ta fasa kai soup spoon ɗin da ta cika da ruwan ferfesun bakin Falmata ba sai dai ta amsa sallamar sa da murmushi akan fuskar ta .

Ƙarasowa bakin gadon Youssouf yayi ya zauna a ɗaya gefen yana bin ƙafar Falmata da kallo wanda ta kumbura daga idon sawun .

Kallon sa ya mayar ga Siyama yana jifatan ta da ɗan kyakkyawan murmushi yace

"Siyama kina gatata ƙamnar ki hakka ? Da har kin ka ciyar da ita ba tare da ni kin tuna da cikina ba ?

Ɗan murmushi Siyama tayi kafin tace " ai itta a yanzu marar lafiya ce kai kouwa ka samu waraka insha Allah .

Murmushi yayi yana mayar da ganin sa kan Falmata yace "Fatima yaya ƙarfin jiki ? Ina ke miki ciwo bayan sawun ki ?

Cikin 'yar ƙaramar murya tace "ba ko'ina sai ƙafar tawa.

Tashi yayi daga bakin gadon ya ɗan yi durƙuso kafin ya kama ƙafar falmata a hankali ya ɗago ta ,

Ganin haka yasa Siyama tayi saurin miƙewa bayan ta ajiye kwanon hannun ta akan ɗan teburin gefen gado (bedside cabinet) .

Ta nufi ficewa daga ɗakin " Maman Yumna ina za ki tai ?

Youssouf ya furta haka yana bin ta da kallo

Lumshe idanun ta tayi ba tare da ta jiyo ba tace " zan tai na kawo ma abinci .

Daga haka ta ƙarasa barin ɗakin tana jin yadda suke kokawa tsakanin ta da zuciyar ta da take son ganin baƙin Youssouf da Falmatan.

A hankali ya mayar da ganin sa kan ƙafar Falmatan ya kai ɗan yatsan sa babba ya shafa gurin da ya ɗan kumbura a hankali da yasa Falmata rufe idanun ta a hankali tana jin yadda tsiƙar jikin ta ke tashi tare da wani yanayi da take ji na tausayi mai girma yana huda zuciyar ta , yana bin duk wani saƙo da lungu da ɓurɓushin jin haushin Youssoufa ya maƙale a ran ta kan laifin da take zaton duk yayi su a bisa son rai cikin sanin sa da yin kan sa .

Ji tayi laifukan sa na gogewa suna shafewa , ƙaunar sa , son sa , tare da tarin tausayin sa masu nawin da bata taɓa jin makamancin su ba saboda ji da tayi kamar zuciyar ta ba zata iya ɗauka ba , kamar sararin dake ran ta yayi kaɗan.

da wani irin tasiri mai girma suke maye gurbin duk wani ɗan taƙi da ta bar wa soyayya mallaki a cikin ran ta .

Tasirin so da take ji a lokacin ya fi ƙarfin rarraunar zuciyar ta da take sabon shiga a fagen soyayya .

Ɗago da kan sa yayi yana kallon ta bayan ya gama tofa mata addu'o'i a ƙafar ta .

Ya ɗan dau lokaci yana kallon ƙaramar fuskar ta da take sake zama 'yar firat yana jin tausayi tare da wannan son nata mai yawa yana masa yawo a zuci .

Jin sa shiru ya sa ta buɗe idanun ta a hankali suka haɗa ido .

"Sannu Fatima insha Allah za ki samu sauƙi kin ji kou ?

Gyaɗa kan ta tayi

A hankali ya miƙe ya ƙarasa ya ɗauki bowl ɗin da Siyama ta ajiye ya dawo ya zauna , ya fara bata ferfesun tana ci a hankali , har sai da ta ɗan ci dayawa kafin tace masa "ta ƙoshi .

Bayan ya ajiye kwanon ya dawo ya zauna tare da riƙo hannun ta ya sarƙe 'yan yatsun su waje ɗaya "Fatima kiyi haƙuri da abunda ya same ki Allah zai miki sakayya cikin gaugawa kuma insha Allah zan zamar miki garkuwar da babu wanda shi issa ya taɓa ki a rayuwa na ƙyale shi , kiyi haƙuri Fatima .

Matsa hannun sa da yake cikin nata tayi kafin ta ɗago kan ta tana saka idanun ta cikin nashi tace " Meyasa bata son ka haka ?

"Nima ban sani ba Fatima cikin rayuwata ban taɓa yi mata laifi ba amma ta zuba min ƙiyayya mai zafi da har da taimakon ta anka nemi raba ni da raina bayan ita ta gurgunta rayuwata ta rarraba ƙiyayyar da take min tsakanina da ɗiyan ta da suke 'yan ouwana .

Kan ta ta mayar ta kwantar a ƙafaɗar sa tana kaucewa kallon cikin idanun sa da suka fara sauya launi tace

"Kayi haƙuri ƙiyayyar ta ba za ta sa ko ta hana kome ba sai fa abunda Allah ya rataya alhakin faruwar sa akan ta .

"Idan ita bata son ka Allah da Manzon Allah su na son ka , Maimartaba yana son ka , Umma tana son ka sauran 'yan uwanka suna son ka , Siyama tana son ka , yaran ka ma zasu so ka .

Ɗan jim tayi kafin ta ɗago kan ta tana kallon cikin idanun sa tace " kuma ni ma ina son ka , Ina son ka , ina son ka dayawa .

A bazata ya tsinkayi kalmomin da bata taɓa furta masa ba , zuciyar sa tayi wani ɗan ƙaramin zillo da yasa shi sake ɗago fuskar ta da sauri ya riƙe ta yana kallon ƙwarar idanun ta , muryar sa a tsakani maƙoshin sa yace "me kika faɗi Fatima sake faɗi naji ? Maimaita min ?

"Ina son ka dayawa dayawa ba adadi
Ta sake furta hakan tana kallon fuskar sa cikin ranta " godiya take yiwa Ubangiji da idan ba shi ba da ƙarfin ikon sa wa ya isa mallaka mata wannan mutumin ma'abocin kyau da cikar zati tare da kyaun nasaba ?

Muryar sa tana sake nitsewa saboda ƙasa da yayi da ita yace "dagaske Fatima ?

Hannuwan ta tasa akan nasa kafin tace "da duk gaskiyar zuciyata ina son ka dayawa ,

Wani irin sanyi yake ji tun daga ƙasan ran sa yana taso masa yana nitsar da idanun sa cikin nata yace " son da nake miki yafi wanda kike min yawa Fatima , son da nake miki ba shi da iyaka , ni ban san iyakar sa ba, kin yarda na gwada miki ɗigo dagga cikin sa ?

Kan ta ta gyaɗa masa tana murmushin da yake bayyana haƙoranta ,

Tazarar dake tsakanin su ya haɗe yana manne fuskar sa da ta ta , tare da shauƙin son da suke yiwa junan su suka himmantu wajen gwadawa junan su tatatciyar soyayyar da suke yiwa juna .

Ƙwanƙwasa ƙofar da Aka yi yasa su sa rabuwa da jikin juna ,

Ba'a jinkirta ba aka murɗo ƙofar a hankali ta shigo bakin ta ɗauke da Sallama .

Siyama ce ta shaida musu zuwan mai gyaran ƙafa .

Yousaouf ya masa iznin shigowa bayan ya gyara mata mayafi.

Ba ƙaramar azaba Falmata ta sha ba kafin ƙashin da ya fita ya koma saboda tsamin da ƙafar tayi kwana huɗu da targaɗe .

Siyama da Youssouf su suka dunga rige-rigen share mata hawaye da gumin da ta haɗa sharkaf duk kuwa da sanyin ɗakin .

Bayan ta dawo cikin nutsuwar ta lokacin Youssouf ya bar ɗakin daga ita sai Hajja da ƙaramar murya ta cewa Hajja " Hajja ki bani wayar ki zan ƙira Mamana da Yakaka .

Ɗan jim Hajja tayi kafin da sigar rarrashi tace "Uwarɗakina Amma fa kar ki shaida musu abunda ya faru da ke domin ba'a sanar da su ba tun da Allah yasa kin fita lafiya kar ki faɗa musu kuma zuciyar su ta kasa nutsuwa da zaman ki anan .

"Ba zan faɗa musu ba Hajja kawai so nake naji muryar su mu gaisa .

"To babu laifi ga wayar ki ƙira su .

Sun jima suna Hira da ita da iyayen ta Khaalty Rahima da Amnee inda har suka yi ƙorafin cikin kwana biyun sun yi ta ƙiran layin Hajja bata ɗauka musamman ma a jiya da Yakaka ta koma Abuja .

Cikin ɗoki Falmata take sake tambayar su 'Yakaka ta tafi gidan ta ?

Amnee ta bata amsa tana dariya da cewa "jiya suka tafi tare da yayan naku takwarata an zama 'yan Abuja ( kamar Ammi Haseen 🤣)

Cikin zaƙuwa Falmata ta fara ƙiran layin Yakaka bayan sun yi Sallama da su Amnee.

Sai dai ƙira biyu tayi ba'a ɗauka ba , yamutsa fuska tayi tana sake danna ƙiran take mitar " Yakaka ko ina ta ajiye wayar ???



ABUJA NIGERIA

Kai-kawo Yakaka ta cigaba da yi a cikin banɗakin da take tsaye , karo na barkatai ta sake sunkuyawa tana leƙe ta ƙafar ɗan makulli , da sauri tayi baya tana sakin wani ƙaramin ihu ƙiris ya rage ta faɗi saboda santsi jikin ta na karkawa ta dafe ƙirjin ta tana mayar da numfashi .

Idanun ta ba ƙarya suka mata ba tirƙeƙen karen da take hangowa tun safe a can nesa daga tsakiyar ɗakin wani lokaci kuma ta hango shi a gefe shine ta gan shi daf da ƙofar a yanzu kamar ma shima leƙen ta yake ta inda take leƙawa dan babu shakka sun yi ido huɗu ita da shi..

Zamewa tayi ta zauna a ƙasa dirshan cikin banɗakin daga inda take tana iya jin wayar ta dake ƙara lokaci zuwa lokaci tsawon yinin amma ba damar fitowa ta ɗau wayar saboda tirƙeƙen karen da yake ta shawagin sa a ɗakin har gado yake hawa yana sauƙa .

A hankali ta saki wani sabon kukan da aƙalla tayi irin sa fiye da sau goma daga safe zuwa yanzu da ta tabbatar yamma tayi rana kuma tana gaf da faɗuwa .



Assalamu Alaikum masu karatu da fatan kuna lafiya ?

Yau dai bakina da goro ba zan ce kome ba bayan fatan alheri da nake muku a koyaushe.


Nagode.
[4/15, 10:16 PM] Zuraiyah Zuzu 🌟: Mafari.

. ( Hargitsin Rayuwa )


Umm'muaz



53







Tsayuwar minti ɗaya zuwa biyu tayi tana kallon ta kafin ta ƙaraso gaban gadon ta zauna ba tare da tace mata ƙala ba .

Hakan da tayi ya sake ƙular da Sofia dan haka a fusace tace " zaɓi na zo baki ko dai yini tare da Sam ko kuwa ki fice daga gidan nan ki tafi can inda kika saba zuwa yawon ki a garin nan idan shi da ya ajiye ki ya dawo kin dawo dan yinin ki da ni a gidannan bana jin zan iya jurewa .

Yakaka wacce kan ta ke ƙasa har Sofia ta gama bayanin ta bata ce mata kome ba tamkar dai bata jin yaren da Sofia take yi

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login