Showing 21001 words to 24000 words out of 411050 words

Chapter 8 - MAFARI COMPLETE BOOK HAUSA NOVELS BY UMMU MUAZ.txt

10 Sep 2025

14343

haram ya baza garin su aka fara guje guje da ƙokarin barin garin ɗaya daga cikin ƙannen mahaifin ta shi ya basu tabbacin idan suka tafi birnin maiduguri akwai mafaka agaresu da musamman gwamnati ta tanada ,"

Dan haka take taku zuciyar ta cike da son ganin sun isa mafakar ta su ,"

Ga bangaren Falmata kuwa ita ba ganin garin take yi ba amma hayaniyar muryoyin jama'a tare da ƙarar wucewar ababen hawa da suka cika mata kunnuwa sun isa sanar mata cewa ta shigo wani wuri da ya sha bamban da mahaifar ta me rangwamen hayaniyar jama'ah , ƙarar ababen hawa kuwa sai ranar cin kasuwar garin su take iya jiyo su daga nesa-nesa ," nan take taji tsoro ya kamata sakamakon tunowa da tayi da fannah ƴar makotar su wacce mota ta taɓa bigewa ta karya mata kafafu " , nan take ta lalubo jikin rigar yakaka ta haɗa da jikin tata rigar ta sake ƙullewa ," sannan ta sake jefa hannun ta cikin na yakakar wacce ita ma ta rike hannun falmatan gam-gam .

Cikin mutuwar jiki suke tafiya a lokaci guda yunwar da take ƙwaƙular cikin su tana tuno musu da rabon su da sanya wani abu a cikin su tun madarar da suka sha da safe ga shi dai yanzu azahar ta yi domin suna iya jin kiran sallah daga massalatan da suke cikin unguwar,"Yakaka idan muka samu wurin da ake sayar da abinci mu tsaya mu saya kafin mu isa ga masaukin mu ,"

Uhm yagana wane masauki kike zance a yanzu bayan duk alamu sun bayyana a garemu bamu da hanyar da zamu bi ta sada mu da gidan gwamnatin ,"idan kuma kina da hanyar sai ki faɗa ," cewar falmata ,

Yagana Jaan bakin ta tayi ta tsuƙe domin ta lura ba wani birge falmata take yi ba a kome ," a gefe guda kuma na zuciyar ta ,tana me gaskata zancen falmatan tabbas , ganin kitse take yi wa rogo a duk zaton ta suna tako kafafun su cikin garin maiduguri zasu tadda jami'an da aka ce suna bada tsaro ga mutanen maiduguri zasu chafe su ,tare da sada su da masaukin su cikin farin ciki da walwala ,"

Sai dai tabbas a yanzu tana iya hango yiwuwar sauyawar tunanin ta "wanda ya sanya ta hango kanta a matsayin wacce tayi masauki a kan bola " da hakan ya sanya ba shiri ta fara zare idanu tana kallon mutanen da ta lura su ma a halin yanzu kallo suke bin su da shi a duk inda suka gifta .

Duk ba wannan ba yanzu abun da yakamata mu fara yi shine mu samu wuri muyi sallah daga nan sai mu fara tambayar mutane hanyar masaukin da kika ce an tanada ga irin mu ,"koh me kuka ce ,"Yakaka ke furta hakan bayan ƴar gajeruwar muhawar da taji falmata da yagana suna yi ,

Cigaba suka yi da kutsawa cikin unguwar suna neman wurin yin alwala har dai suka yanke shawarar tsayawa a dai-dai wata mahaɗar da ta fi kama da tashar tsayuwar motoci saboda yawan ababen hawan da suka gani a wurin ,"sai dai yawan masu saye da sayar a wurin kama tun daga kan masu ɗanyen kaya ,da masu kayan abinci na awu ,"har ma zuwa masu saida dafaffen abinci da kuma masu toye-toye , ga kuma ƴan tebura nan dangin su masu saida biredi da sauran su ya sanya su hasashen ƙila kasuwa ce," tsayawa suka yi a wurin suna rarraba idon neman wurin da zasu samu damar Alwala ,

Daga gefe kaɗan da su , suka hango masallaci wanda rumfar kwano ta kare gaban sa mutane suna ta Alwala wasu kuwa sun kammala alwala suna sallolin su a cikin rumfar ,"

Ɗan yawatawa da idanun ta yakaka tayi tana neman ruwan Alwala ,"sai dai yawan idanun da ta gani akan su ya saka ta cikin firgici ,"kusan illahirin mutanen wurin hankulan su da idanuwan su akan su yake ," kuma idan ba idanun ta suke mata ƙarya ba kusan duk mutanen wuri ɗaya suke kallo a jikin su", daga kan kirjin su zuwa cikin su ,'!

A hankali ta sauke idon ta tabi inda suke kallo a jikin su ta gani koh wani abun ne a jikin nasu ,"

Hannu ta kai tare da gyara wuyan rigar ta da ya ɗan saɓule lokaci ɗaya kuma tana kai hannu ta gyarawa falmata ita ma nata wuyar rigar , duban ta 'ta mayar kan yagana wacce ta fahimci ita ma ta lura da irin kallon rashin yaddar da illahirin mutanen wurin ke bin su da shi ,"

Ƙasa tayi da muryar ta "yagana kin lura da irin kallon da mutanen nan ke bin mu da shi ? Koh daman haka mutanen birni ke yin kallon su ?

Ina lure da su nima ,"amma ina ga haka suke kallon su "dan yaakura na tace a lokacin da ta kawo ni asabitin tsatsareni da ido likitan nan yayi a cewar ta saura kaɗan ta ɗauke ni mu tafi dan tayi zaton ma koh karama ne (maye ) ɗan guntun tsaki ta jaa a lokacin da suka haɗa ido da wani matashi majiyi karfi yana kallon su tsakar ka, lokaci ɗaya kuma yana danna wayar sa tare da kara ta a kunne ","

Jibe shi dan Allah ya wani tsare mutane da ido toh kurwar mu kur ," Falmata kawo kuɗin nan na ƙarasa can na sayo mana ƙosai da doya nan wurin ma jama'a sun yi yawa mun ƙara gaba kawai muyi sallar ,"

Falmata bata ce ƙala ba ta miƙa mata gudar ɗari biyun da take duƙunƙune a hannun ta "sashi guda na zuciyar ta! Yana gaskata mata zancen su yakaka na cewa da suka yi an zuba musu ido domin kuwa ita ta riga su sanin ana kallon su ,dan tun da suka nufo wurin jikin ta ya bata akwai wani abun cutarwa ko kuwa idanun mutane akan ta ,'duba da yadda taji tsikar jikin ta tana ta faman miƙewa,'hakan shine alamun da ita take fahimtar akwai matsala a wuri "baiwar ta kenan" , a gefe ɗaya cikin ranta kuwa cike fal! Da haushin yagana akan yadda take nuna ita fa ala dole ta fi su sanin maiduguri Alhalin kuwa su da ita duk sammakal tilo ," basu da wani bambanci.

Taku biyu yagana ta yi suka fara jiyo tsuwwar wani abu wanda basu san ko meye bane ,"yayin da hankalin su ya kasu biyu ɗaya akan mutanen da suka ga sun fara guje guje wasu ma har suna barin kayayyakin sana'o'in su ,gefe guda na hankalin su na ga kan tsuwar nan da suke ji tana sake durfafo inda suke , so suke su fahimta akan wannan tsuwar ne mutanen ke gudu koh kuwa meye dalili ,?

Yakaka ƙarar meye ne wannan ɗin kuma meyasa naji kamar takun gudun mutane ?falmata ta furta hakan a dai-dai lokacin da take lalubar jikin yakaka tana gyara ƙullin da ya haɗa bakin rigunan su 'da alamun shirin gudu take "
Nima ban sani ba Falmta,"
Yunƙurin buɗe baki yagana take cikin cewa wani abu amma sai maganar ta maƙale mata a fatar baki.' sakamakon ganin manyan motocin da suke ɗauke da irin fentin da suka gani a jikin jirgin saman nan da yayi musu ɓarin wuta a daji ," a take suka fahimci ƙarar nan da suke ji daga jikin motocin nan take fitowa .

Ɗurum dum ,"bugun sautin zuciyoyin yakaka da yagana a lokacin da suka yi idanu huɗu da tarin motocin da suke da tabbacin na waɗannan mamallakan jirgin saman ne ,"shikenan mun mutu mun lalace yakaka , shikenan wallahi sun biyo mu ne su kashe mu ,"
Su waye suka biyo mu ? Yagana wai meke faruwa ne ,"cewar falmata da maganganun yagana suka yi mugun ruɗa ta ,"
Sojojin da suka biyo mu da jirgi a daji sune gasu nan a mota ....
Sauran maganar maƙalewa tayi a fatar bakin yagana a lokacin da ta ga gungun sojojin nan suna durƙowa daga bayan manya manyan motocin su hannayen su duk riƙe da bindigogin su da ya sanya cikin yagana ba da wani sautin ƙululu lokacin da tayi arba da su ,"wannan fa shi ake cewa anyi gudun gara an tadda zago ,"

Jeruwa sojojin suka yi daga nesa kaɗan da inda su yakaka ke tsaye a sandare ko numfashi da ƙyar suke jaa ,"
Da gudu wani soja ya fito daga cikin gaban wata mota hannun sa riƙe da wata jibgegiyar bindiga ," ɗaga ta yayi gami da jaan kunamar bindigar ƙaraƙat ,'ya saita ta akan su yakaka da zuwa yanzu suke ta ɗigar gumi kamar an tsamo su daga rafi ,"

Remove your clothes all, "

Sasarai su dukkanin su suka yi suna wulwulga idanu cikin rashin sanin takamaimai ɗin abun yi lokaci guda kuma tsoro ya sake cika zuciyoyin su a sakamakon lura da suka yi cewa duk yawan mutanen wurin nan a yanzu basu ga ko mutum guda ba daga su sai sojojin nan ,"ji suka yi zuciyoyin su na barazanar faso kirjin su .,

Fahimta da sojojin nan suka yi su yakaka basa jin turanci ya sa ɗaya daga cikin su ɗaga murya ",
Ku cire kayan jikin ku idan ba haka ba zamu harbe ku mu kashe ku ,"
Cikin tsananin firgita yakaka da yagana suka kalli juna lokaci ɗaya suka ji falmata ta rushe da kuka ,"
Ji suka yi an sake daka musu tsawa
Zamu harbe ku idan kuka sake minti ɗaya ,"

Ba shiri yagana ta fara cire tun daga ɗangalallen hijabin ta har zuwa rigar ta da yanzu take kan cirewa ,"

Satar kallon yagana ,"yakaka tayi kafin cikin rawar jiki ta miƙa hannu tana warware kullin da yake tsakanin rigunan su ita da falmata lokaci guda tana me cewa falmata ki cire kayan ki idan ba haka ba zasu kashe mu ,:

Tsaye suke daga su sai siket din ciki hannayen su rumgume da kirjin su ,fuskokin su kuwa shaɓe shaɓe da ruwan hawayen da ya chakuɗa da majina gami da gumi ,"

Magana sojojin suka yi a tsakanin su bayan sun gama ƙare musu kallo Daga wurin da suke ,"

Sir I think they're not Boko Haram girls , there was no bomb in their bodies,"
( shugaba ina tunanin waɗan nan. ba ƴan matan boko haram bane , babu nakiya a jikin su )

Yes they're not ,

(ƙwarai ba su bane )

Daga inda sojan nan ya yake tsaye ya sake ɗaga murya tare da basu umarni su sanya suturun su ,"

Koh kafin ya ida rufe bakin sa har sun yi nisa wurin sanya kayan nasu ,"tsayawa suka yi suna jiran su sake jin umarni na gaba ,"idanuwan su kuwa basu bar zubar ruwan hawayen wannan tozarci da tashin hankalin da suke ciki ba ," ba ma dai kamar falmata wacce har karkarwa take tsabar kuka ,"

Gani suka yi ɗai ɗaya da ɗai ɗaya suna komawar su cikin motocin su ,"yayin da suka ga waɗan nan biyu da suke yi musu magana ɗaya da hausa ɗaya cikin yaren da basa fahimtar sa sun nufo inda suke bindigogin su saɓe akan kafaɗun su ,"

Suna ƙarasowa wannan me jin hausan yace musu ", daga ina kuke kuma ina zaku ?
A wannan karon shiru yagana da ta kasance jaa gaba wurin mayar da amsa tayi tana zazzare idanu tare da satar kallon bindigogin hannun su ,"

Jin yagana tayi shiru ya sanya yakaka ta buɗe bakin ta cikin maƙyarƙyatar murya tare da gurbatatciyar hausar ta tace ",
:Umh daman mu ƴan hijira ne daga garin mu shine-shine muka zo nan neman gwamnati ta taimaka mana da masauki ,"
Inane garin naku ?
Ƙauyen mairambiri

Magana sojojin nan biyu suka yi a tsakanin su cikin harshen turanci ,"

Ku zo mu kai ku camp mu ajiye ku saboda idan kun cigaba da yawo haka a gari mutane baza su yadda da ku ba a karshe ma ana iya yi muku dukan tsiya da tunanin ku irin ƴan matan da boko haram suke ɗaura musu nakiya ne , su shiga cikin kasuwa koh taron jama'a su yi ƙunar baƙin wake ," bayanin da sojojin nan suka yi musu kenan bayan sun gama shawara a tsakanin su

Nan fa aka shiga kallon-kallo tsakanin yakaka da yagana ," camp ina ne camp ?koh dai gidan horar da mutane ne sojojin nan zasu tafi da mu ? Wannan ne zancen da yake ta kai kawo cikin zuciyoyin su dukkanin su uku lokaci guda kuma suka ji wata sabuwar nadama baki daya ta kama su ,"daman haka mutanen cikin birni suke azzalumai haka kawai sai su hau jibgar mutum ?

Tsawar da aka daka musu ita ta sanya ba shiri yakaka ta kama hannun falmata suka bi bayan sojojin nan da su har sun yi juyawar su sun kusa isa ga motocin su tun bayan da suka basu umarni ,"

Wani irin mahaukacin gudu motocin sojojin nan suke akan tsakiyar titin na Maiduguri ," duk inda suka gifta motoci da sauran ababen hawa darewa suke suna basu hanya ,"

Tsugunne su yakaka suke a bayan hilux ɗin, sojoji biyu sun sanya su a tsakiya a zaune a kan ɗan tudun da aka tanada domin zama ," ji suka yi iskar shaƙa ta musu yawa a saboda gudun da motar ke yi ,"nan take maƙoshin su ya bushe ƙemas , idan ban da sharar hawaye babu abun da suke yi ,tun da suka hau motar babu me cewa ƙala ,"

Gware yakaka da falmata suka yi ," a sakamakon wani irin birki da motar da suke ciki ta jaa," wani marayan kuka falmata ta fashe da shi a dalilin zafin da ya ziyarci ƙwaƙwalwar ta a dalilin gwaren da suka yi ",

Dira sojojin da su ke tare da su a bayan motar su ka yi kafin su yi musu umarni akan su sauƙo ,

Tsayawa yakaka-da-yagana suka yi suna ƙarewa wurin da aka kawo su kallo ,"wata babbar kofa ce a gaban su me kama da kofar gari a ganin su, sai da ƴaƴan hanjin cikin su yakaka ya kaɗa sakamakon ganin wasu gungun sojoji da suka yi daga cikin wata rumfa a gefen kofar ,"
Yakaka ina aka kawo mu ,? Inji falmata ,"
Nima ban sani ba falmata ,amma dai kamar wani babban gari ne shima gashi dai har da wata babbar kofar sa ," ta furta hakan tana me satar kallon sojojin da koh kula da su basu yi ba,"

Ku zo mu je nan shine camp (sansanin ƴan gudun hijira ) inda gwamnati ta tanadar ga ire-iren ku ," a cewar wannan sojan da ya wuce gaba ,"

Da sauri su ka bishi ransu yana wani ɗan motsin daɗi-daɗi ! Duk da cewar dai basu gama aminta da zancen sa ba domin basu tabbatar ba ,'

Yakaka da yagana su na sanya kafa cikin wurin suka fahimci ba ƙaramin babban fili bane ta ciki , a yayin da suka fara yawata idanun su zuciyoyin su cike da mamakin ganin mutane birjik fululu iyakar ganin su suna ta harkokin su ,"

Hayaniyar jama'ar da falmata ta fara ji yana tashi cikin yaren su , shi ya sanya ta ji kaso goma na tsoron da yake cike da ranta ya kau ,!

Bayan ƴar gajeruwar tafiyar da suka yi , bakin wani gini sojan nan ya tsayar da su yayin da shi ya taka ya shiga cikin ɗan wurin mai kama da ɗaki ,"(Office)" bai kai minti biyar ba ya fito ba tare da yace da su kome ba yayi wucewar sa cikin rashin kulawa da gaisuwar da wasu mutane maza da suke zaune turmus a cikin ƙasa da suke yi masa ,"

Cigaba da tsayuwa su yakaka suka yi a wurin har dai zuwa lokacin suka fara jin ƙafafuwan su sun fara sagewa a gefe guda yakaka da yagana cikin ransu suna nazarin tsarin wajen ," daga gefe gine ne a jere reras tamkar ɗakuna da barandar su doguwa wanda aka yi ginin da bulok tare da rufin kwanon da suke iya hango rufin sa da duk rana da ruwa suka gama illata sa ya zama jazir ," babu abun da yafi yawa a sararin wurin irin bishiyoyin darbejiya wanda suka lura karkashin kowacce bishiya a cike yake da mutane maza waɗan da suke zazzaune wasu kuma a kwance ,yayin da wasu suke a kishingiɗe turmus a cikin ƙasa ," daga inda suke tsaye suna iya hango matan da suke cike a cikin kowanne ɗaki har zuwa barandar ,' dukkanin su mata ne da ƙananun yara da kallo ɗai-ɗaya su ka yi musu suka fahimci halin tagayyara da wahalar da suke ciki ( makamanciyar ta su ),

Daga farfajiyar wurin da babu wadatar bishiyoyi wasu manyan ɗakuna ne wanda aka yi su da ƙarafuna tare da rufin leda mai nawi ,"tantinan wucin gadi ", nan ma a cike yake da mutane maza da mata ," wata boyayyar ajiyar zuciya yakaka ta sauke lokacin da taga wasu maza sun zo sun wuce ta gaban su ,"hannun su riƙe da buhun-hunan da ta gane na abinci ne ,

Yakaka wai tsayuwar nan kam ba ta ƙare ba ce koh ? Yagana ke furta hakan a lokacin da ta karya gwaiwar ta da nufin tsugunnawa , "sai dai bata kai ga tsugunnon ba taji ɗaya daga cikin mutanen da suke zaune karkashin bishiya daga gefe ya ce ," kai kai ku tashi daga nan chan za ku tafi ku nemi wurin zama," yana yi musu nuni da sashin ɗakunan nan. "

koh kafin yagana ta samu abun faɗi ,"suka ga an fito daga wannan ɗan ɗakin da daman suke dakon jirin fitowar mutum daga cikin sa ," da sauri suka zube ƙasa suna gaishe da ɓakin jibgegen mutumin da yake yi musu kallon sheƙeƙe ,"

Ba tare da ya amsa gaisuwar ta su ba ya fara cewa to menene ,? Menene kuma ? Kai Duba ni fa na fara gajiya da ku da ƙorefe-korefen ku , ku koma can daga wurin ku idan waɗanda Alhakin faɗa musu ƙorefe ƙorefen naku ke wuyan su , sun zo kuna iya zuwa kuyi dafifi ku faɗa musu

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login