Showing 360001 words to 363000 words out of 411050 words
Chapter 121 - MAFARI COMPLETE BOOK HAUSA NOVELS BY UMMU MUAZ.txt
rasa ƙima da darajarka ta ɗan sarki da hakan zai sa ka gaza wajen hawa kujerar mulkin Maradi , a wayi gari Mammadou shi ne Sarki.
"Duk abunda nake faɗa maka a yau gaskiya ne babu ɗigon ƙarya ko ɗaya a ciki, ita da bakin ta ta faɗa min idan kuma kana son samun tabbaci da kuma hakan zai kai ga karya duk wasu sihiri da aka maka kuma har yau suke aiki a kan ka , ka koma Maraɗi ki tafi tsohon sashin Hajiya Uwa a babban falon ta cikin ɗaki na biyu daga hannu hagu ka bincika ɗakin a cikin armoire asirin da aka maka yake .
" Ka je ka fasa kome , Ka ɓata kome , muddin kana son cigaba da yin rayuwar da babu dabaibayin sihiri a cikin ta .
"A ƙarshe ina baka tabbacin Hajiya Mama tana da hannu wajen ɗarsuwar duk wani baƙin-ciki a rayuwar ka dan haka ba tamtama a wannan karon ma ita ta sace Fatima .
Sakwaf ! Youssouf ya sake ta ta faɗi a ƙasa kalamanta na ratsa duk wasu jijiyoyin cikin ƙwaƙwalwar sa suna aikawa da saƙon gaugawa zuwa cerebrum na kwakwalwar sa har zuwa temporal lobe da anan take ya fara ƙoƙarin tuno masa da duk wasu motsi da lamurarran Hajiya Mama a kan sa .
"Yadda take kyarar sa tun yana ƙanƙanin sa , da ya fara girma ya mallaki hankali sai yana lura da ko ganin sa bata son yi sannan duk wani abu na farin-ciki idan ya same shi bata taya shi murna haka kuma na baƙin ciki , kai ko jinyar da yayi na kwanan nan ma bata taɓa masa ya jiki ba , bare ta jajanta masa , a duk lamuransa idan ba ɓacewar Falmata ba bai taɓa jin ta sanya bakin ta ciki ba ya daɗe da sanin bata ƙaunar sa .
"To amma anya hakan ya isa ya sa shi yarda da cewa Hajiya Mama Matar Mahaifinsa ita ce ta sace Matar sa ?
Girgiza kan sa yayi yana jin haɗuwar kalaman su su biyun masu cin karo da juna a can Maradi Hajiya Mama tace Maimounatou ce ta sa aka ɗauke Fatima , anan kuma Maimounatou tace Hajiya Mama ce ta sa aka ɗauke Fatima .
"Waye mai gaskiya a tsakanin su ?
Abu mafi girma da ya fahimta a tsukin lokacin shine wata ɓoyayyar alaƙa da take tsakanin su biyun da bai taɓa kaiwa ga sani ba .
Kalaman Maimounatou akwai ɓurɓushin gaskiya a cikin su Musamman cikakken bayanin da tayi masa kan lokutan da munanan al'umuran da suka faru a rayuwar sa suka fara faruwa .
"Ya zama dole na koma Maradi , na koma domin samun tabbaci tsakanin ƙarya da gaskiya .
Da sasaarfa ya juya yana barin wajen , Maimounatou da take zaune dirshan a ƙasa tana mayar da numfashi cikin wata irin murya tace "Youssouf ka min afouwa ka yafe min ka sake bani dama .
Tsayuwa yayi ba tare da ya juyo ba yace "Na sake ki saki Ukku Maimounatou kada kuma kiyi fatan abunda zai sake nuna mana fuskokin juna a zahiri .
Ihun da Maimounatou ta sa sai da ya ƙarade harabar ofishin kafin ya bar da'irar wajen yana iya jiyo hargowar ta tana ƙiran sunan sa .
"Youssoufa.
"Youssoufa ka dawo wallahi nayi nadama .
Bata taɓa sanin cikin wasanni ta ta haɗo da zuciyar ta ba sai a yau da Youssoufa ya rayu bayan so da tayi ta gille masa rayuwar sa ya kuma dawo ya sake ta irin sakin da babu kome , a dai-dai lokacin da ita kuma zuciyar ta ta haƙaƙe da cewa ta daɗe cikin mayen son sa tun tana ƙaryata kan ta akan haka har a ƙarshe ta saduda ta kuma shiga addu'a ka'in da na'in Allah ya tashi kafaɗun sa ya dawo su cigaba da rayuwar su .
haƙiƙa tayi asarar Miji irin wanda ba zata samu madadin sa ba . To wa ma zai sake auren ta ?
Kenan ita bata ci ribar kome ba sai fa ta lalacewar suna a idanun al'umma ta zama mujiya abar zunɗe .
Zuciyar ta taji tana wani irin narkewa da nadama marar iyaka , tsoron halin da zata tafi ta tadda a rayuwar gidan su na huda ta da tun da ta kwashi tsawon satika bakwai a kulle babu wanda ya leƙo daga gidan su ko wani dangi nata ta san cewa kurar ta tayi kuka ta kuma riga ta dusashe tayi duhu a idanun kowa na ta .
Kwanciya tayi a ƙasa tana wani irin kuka tare da jin yadda zuciyar ta ke zogi kamar zata fashe a tsukin lokacin zaɓar mutuwa take son yi akan rayuwar da zata tarar a gaba .
Kai tsaye Youssoufa ainashin cikin ofishin ya koma inda ya nemi da a ba shi takaddun neman belin waɗan da ake tsare da su .
Baya cikin nutsuwar sa ya ciccike inda ya bada tabbacin yin afuwa ga Masu laifin su biyu da ake tuhuma da yunƙurin kashe shi a matsayin sa na wanda suka yiwa laifin ya sanya hannun ya janye ya musu afuwa a sake su .
Bayan gajerar muhawarar da Youssouf bai bada hankalin sa ba ya ƙirgo wasu kuɗaɗe ya ajiye a gaban teburin ya miƙe yana barin wajen bayan sun yi Sallama.
A waje ya tarar da Bilal cikin motar direban da Mijin Ubbo ya turo ya ɗauke su idan sun gama bai shiga motar ba ya ƙira Bilal ya fito .
"Ka shigga ciki za'a fito da Mammadou ku tafi gidan ubbo tare ni akwai inda zan tai .
Bai jira amsar sa ba ya taka da sauri yana barin wajen .
Wani ƙaramin Hotel ya je ya kama ɗaki na kwana guda (HOTÈL TÉNÉRÉ) tun da ya shiga ɗakin ya kashe wayoyin sa yayi sallah yayi zaune tunaninnika na masa rubdugu .
ji yake kamar ya buɗi ido ya gan shi a maraɗi wani irin hali ya kasance a ciki tsawon ƙarshen yinin zuwa cikin daren da ya tsinci tsawon sa fiye da na darare uku a wajen sa .
Asubar farko ya miƙa mukullin ɗakin ya bar otel zuwa tashar mota .
Mota ta farko da ta tashi zuwa Maraɗi da misalin ƙarfe shidda na safe cif sun kama hanya tare da Youssoufa da ya kasa jiran karfe biyun ranar jirgi ya tafi da shi .
Ya zaɓi tafiyar motar saboda ya san duk inda ƙarfe biyu na ranar tayi yana cikin Maraɗi .
Maradi .
Tun ajiya da Hajiya Umma da shi kan sa Maimartaba suka kasa samun layin Youssoufa suke cikin fargaba duk kuwa da cewa sun yi waya da Bilal har ma da Mammadou cewar suna lafiya kuma Youssoufa ma yana lafiya sai dai su ma basu san inda yake ba kuma basu samun wayar sa.
Bayan addu'a babu abunda Hajiya Umma take yi saboda jikin ta yana bata wani abu ya faru ko kuma zai faru ko mai kyau ko marar kyau .
kuma kawo yanzu ta fahimci ƙaunar da ɗan ta yake yiwa Falmata marar misaltuwa ce ba yadda ta iya dan dole ta fara addu'ar Allah ya bayyana Fatima ko dan Youssouf ya samu nutsuwa .
Ga Hajiya Mama kuwa yau ranar farin-ciki ce a wajen ta dan kuwa har 'yar ƙaramar walima ta haɗa na farin-cikin dawowar ɗan ta mafi soyuwa a wajen ta da aka yiwa sharri aka garƙame ta gayyaci ƙawayen ta na ƙud da ƙud dan su zo taya ta murna .
Matar Mammadou da ake ƙira Zainaba ita ma a nata gidan sai murna tare da shirin taryar Mijin ta .
Kamar kullum yau ma bayan an tafi Sallar Azahar Hajiya Mama ta kashe jiki ta nufi shiyar Hajiya Uwa ta buɗe ta shiga .
Ƙarfe biyu saura mintuna goma taxi da ta ɗauko Youssoufa daga tasha ta sauke sa baya cikin nutsuwar sa ya biya mai taxi .
Da sassarfa yake taku ya nufi cikin gidan kallo ɗaya zaka masa ka matsa daga hanya ko da kuwa ba ka san ko shi wanene bane .
Ta gaban Fada ya zo ya wuce akan idanun Maimartaba da kowa na cikin fadar wanda hakan shine na farko da Youssoufa ya zo ya wuce ta gaban Mahaifin sa bai ƙarasa ya gaishe shi ba , abu ne da bai faruwa mutum ya taka ƙofar fada bai shiga ya kai gaisuwa ba .
Shiru Fadar ta ɗauka kafin cikin abunda yake ƙasa da mintuna biyu wani daga cikin manyan bayun gidan ya taho a sukwane ya yi gurfano yana kai gaisuwa kafin ya ɗora da cewa "Ran Sarki ya dade yau da alamun ɓacin-rai mai girma ga Yarima Biyamuradi domin kuwa ga shi can riƙe da bindiga a tsirarar ta ya nufi shiya......
Miƙewar da Maimartaba yayi babu shiri ita ta sa sauran 'yan Fada suka miƙe tsaye su ma su na cewa "Allah ya huci zuciyar ka jagoran Al'umma Yaa Sarkin mu mai Adalci .
Cikin ɗago taku Sarki Abdoul-azizou ya wuce gaba bayan yace "mu tai ka min jagora zuwa inda yake .
Hajiya Mama da Biyamuradi Youssouf ƙiris ya rage su ci karo a tsakanin hanyar sashin Hajiya Uwa ,
ita tana fitowa shi kuma yana ƙoƙarin shiga da sauri ta jaa baya idanun ta a waje take bin sa da kallo .
Shi ma tsare ta yayi da ido yana bin ta da wani irin kallo mai kaifi da yasa nan take laɓɓan ta suka ɗauki rawa kamar wacce take gaban alƙali .
"Kai..kai kuma la..lafiya ? Ina..ina za ka tai ?
Bai amsa mata ba ya wani irin kewaye ta ya wuce , wani mummunan bugu zuciyar ta ta hau yi ganin inda ya nufa kai tsaye ƙofar falon Hajiya Uwa .
Taƙi barin fargabar da take bin duk lakkar jikin ta tana kassarawa tayi nasarar duƙusar da hanzarin ta , ta bi shi da ɗaga takun da ta ƙara da gudu ta sha gaban sa lokacin da yake ƙarasawa gaban ƙofar ta shiga tsakani sa da ƙofar ta raba hannuwan ta cikin wata irin buɗaɗɗiyar murya tace
" Ba zaka shiga ba ka koma inda ka fito nan ba hurumin ka bane , nace ka koma.
Idanun sa da suka yi jawur ya ɗago yana kallon ta da wani irin yanayi da ya fara fita a saiti na hankalin sa ya sanya hannun sa ɗaya ya ture ta gefe tayi taga-taga zata faɗi amma ta tokare.
Sai dai me ? Ture ta da yayi da ƙarar ɓalla ƙofar da yayiwa duka ɗaya da kafar sa ya shiga falon basu ruguza mata zuciya kamar taron mutanen da ta hango sun yi ɗango suna tahowa ba wanda halin ɗimuwar da take ciki bai hana ta gane Maimartaba , Hajiya Umma tare da kakaf 'ya'yan su da suke gida a dai-dai lokacin zuwa manyan bayu da ma ƙanana da suke danno musu baya ba .
Jin ƙarar kamar Youssoufa yana karya wata ƙofar ya sa ta runtumawa da gudu ta faɗa falon ba tare da ta damu da taron mutanen da suke iya hango duk abunda yake faruwa ba , hankalin ta a dai-dai lokacin ya kasa yarda da abunda ke shirin faruwa da ita .
Tana shiga ta riƙo rigar Youssoufa ta baya tamau ta cukuikuye shi ta hana shi shiga ɗakin da ya riga ya karya ƙofar kawai sai ta saki wani irin ihu dai-dai da shigowar Maimartaba .
"Maimartaba ka hana shi ka hana shi nace wayyo Allah na , nace ka hana shi kar ya min lahani ga rayuwa ta.
Wata irin fincika da Youssouf ya yiwa rigar sa sai da ya kai Hajiya Mama ƙasa da sauri Hajiya Umma ta tare ta cikin ɓacin rai tace
"Kai Youssoufa mene ne kake yunƙurin yi hakka ? Hala bakka cikin hayyacin ka ?
Bai saurari kowa ba sabod idanun sa daga na zuci har na zahiri a makance suke.a lokacin ƙudirin da yake gaban sa kawai yake son cimmawa .
Yana danna kai a ɗakin ya shiga yin fatali da duk abunda ya tarar a cikin ɗakin da bai wuce wasu itatuwa da wasu ƙwarrai da babu kome a cikin su ba.
Dube-dube ya shiga yi har idanun sa suka sauƙa kan wardrobe irin ta jikin gina na shekaru aru-aru .
Duk da ƙarfin da yake da shi da jarumta irin na sojin ƙwarai da kyar ya iya buɗe ta ya shiga yawo da idanun sa a ciki lokacin da Hajiya Mama ta sake yin kukan kura ta kufce daga Hannun Hajiya Umma ta faɗa ɗakin .
Idanun sa suna sauƙa akan wata ƙatuwar ƙwarya da take ajiye daɓas da duwawun ta bata wani tangaɗi ba'a ce ƙwarya bace lokacin kuma Hajiya Mama ta sake riƙo rigar sa ta baya cikin wata irin murya mai firgitarwa tace
" Kar ka taɓa , wallashi ina kashe ka idan ka taɓa .
Kalmomin ta suka sauƙa a kunnuwan Maimartaba da Hajiya Umma da suke shigowa ɗakin sauran mutane na biye da su domin kowa ya shiga ɗimuwa tare da ƙaguwa kan son fahimtar wai me yake shirin faruwa ?
Hannun sa biyu ya sa ya cicciɓi ƙwaryar yana juyowa Hajiya Mama ta jawo rigar sa da iyakar ƙarfin ta da har sai da ta ɓarke .
Ƙwaryar kuma tayi tangal-tangal a hannun sa lokaci ɗaya ya sake ta ta tafi baki ɗaya ta kwaranye a rabin jikin Hajiya Mama kafin ta kai ƙasa ta tarwatse .
Wani fitinanne wari marar daɗi da yake tada hankali ya cika ɗakin da yasa sai da kowa ya toshe hancin sa wasu suka yi baya da sauri .
Maimartaba da yake tsaye ƙiƙam da idanu ya bi wasu kwaɗi biyu da suka fito daga cikin ruwan mugunyar sai tsalle suke suna neman wajen ɓuya .
Kafin yayi wani yunƙuri Liman da shi ma hankalin sa ya kai kan su nan take ya fara addu'a .
Chak suka tsaya suka bar tsallen yayin da warin da ya cika wajen kuma ya fara raguwa sai tsamin giyar burkutu da ya maye gurbin warin gum kai kace a tsakiyar gidan Madam Saly -fara ake .
Umarni yayiwa wasu bayi biyu da su ɗauke su su fita da su su riƙe .
Jin haka yasa Hajiya Mama da tayi suman tsaye tun lokacin da ƙwaryar ta fashe cikin wani irin sauti mai faɗi fashe da matsanancin kuka tana duban jikin ta cikin tashin hankali da wasu zuƙa-zuƙan tsutsotsi da suke yama-yama a cikin ruwan suka hau jikin ta .
Ihu ta sake kurmawa lokaci guda ta fara cewa "ku bani ruwa dan Allah kar su shige min cikin jiki wayyo Allah na shiga uku , Youssoufa Allah shi tsine maka ɗan bala'i .
Jikin sa yana mazari ya taho gaban ta ya tsaya yana gyara riƙon bindigar sa yace
"ina Mata ta ?
"Ina kin ka kai min Mata ta ?
"Ina Mata ta nake tambayar ki ?
Bangaje shi Hajiya Mama tayi cikin yanayin da yake nuna ta daina fahimtar kome da gudu ta nufi hanyar fita mutane suka dare a tsorace suka buɗa mata hanya ta fita a guje .
Wani irin duka Youssouf ya shiga kaiwa bango da hannun sa yana wani irin huci gaba ɗaya jijiyoyin jikin sa sun miƙe yana wani irin tsuma da duk ya tsorata mutanen wajen .
Nan take hawaye ya fara sauƙa a fuskar Hajiya Umma .
Maimartaba ne ya tako a hankali ya dafa kafaɗun sa kafin ya zarce da riƙe hannun sa da har ya fara fitar da jini .
"Innalillahi wa inna ilahi raji'oon ,Lahaula wala kuwata illah billah huwal aliel azim ya fara maimaita masa cikin nutsuwa kafin ya kai hannu ya zare bindigar da yake riƙe da ita a ɗayan hannun sa .
Wani irin kuka ya fashe da shi yana damƙe hannun Maimartaba da yake cikin nasa yace " Baba me na mata ? Meyasa ta min hakka ? Itta ta ɓata min rayuwa ta tayi sanadin da suna na ya ɓaci ƙima ta ta zubbe , iyayena sun ka yi fushi da ni , Baba me na mata ?
" Ka ƙira ta ta dawo ta faɗi inda ta kai Mata ta , Ita tayi enlevé na Fatima
" Me Fatima ta mata zata badda ta ? Ina ta kai Fatima ?
Ya ƙara cewa haka da wata irin buɗaɗɗiyar muryar da tayi amsa kuwwa a baki ɗayan sashin .
Falmata da take tsakiya da yin kuka cikin tsoron ko Hajiya Mama ta turo mata Aljannu ne su kashe ta kamar yadda ta faɗa mata a yanzu? domin da ta shigo ta ji tana karatun Alkur'ani .
Shine ta mammake Mata baki ta ɗora da tsorata ta da cewa zata mata turen ifiritai su zuƙe jinin ta muddin ta sake karatun kur'ani .
Jin tashin muryar Youssouf yana ƙiran sunan ta ya sa ta zabura ta miƙe zafin da ya ratsa ƙafar ta ya sa ta saurin komawa ta zauna wasu sabbin hawaye na sake zubo mata .
Da rarrafe ta ƙarasa bakin ƙofar ɗakin ta soma bubbugawa da ƙarfi tana ƙiran sunan Youssouf .
Da gudu Youssouf ɗin ya fito saboda shirun da wajen ya ɗauka ya bashi damar jin muryar ta a kusa .
Duka ɗaya ya yiwa ƙofar ta karye da ƙiris ya rage bai faɗa mata akai ba .
Yana shiga ɗakin ya zube guiwowin sa a ƙasa ya ɗago ta "Fatima-Zahra Est-ce que ça va? Alhamdulillah , Alhamdulillah '
Wani irin kuka ta fashe da shi tana ƙan-ƙame shi kamar zata koma jikin sa cikin kuka ta fara cewa " Dan Allah ka fitar da ni anan ka mayar da ni gida wajen Mamana, waccan matar ita ce ta kawo ni nan ta kulle ni yau kwana huɗu tace min zata kashe ni ,idan na yarda nayi magana , kai ma ita ta yi ma asiri kai da Yakaka ita tayi , ita tayi muguwa ce bata da kirki ....
Jijjiga ta yayi da sigar rarrashi yace "va bien mon amour Votre protégé en toute sécurité maintenant babu abunda zatta sake iya yi miki kin ji Fatima ki nutsu ki daina kuka ? Tayi miki ciwo ? Ina yake miki ciwo ?
Ya furta hakan yana ɗaga kallon sa zuwa kan Maimartaba da Hajiya Umma waɗan da suke ganin kome kamar a shirin film wai Hajiya Saratu da suke rayuwa da ita shekara da shekaru ita ce ta yiwa ɗan su duk wannan mugun ƙullin ?.
Ko Hajiya Umma