Showing 408001 words to 411000 words out of 411050 words

Chapter 137 - MAFARI COMPLETE BOOK HAUSA NOVELS BY UMMU MUAZ.txt

10 Sep 2025

14287

a jikin Baban ta tana wasa girman jikin ta da wayon ta sun wuce na watannin ta shidda sai dai a kai ta watanni goma .

Noƙewa tayi tana ƙin zuwa ta faɗa jikin Baban ta da sauri tana ƙyaƙƙyala dariya irin ta yaran da lafiya da jin daɗi ya wadace su .

A lokaci ɗaya iyayen nata su ma suka sa dariya suna bin ta da kallon dake cike da ƙauna Falmata ta ɗan jaa kumatun ta "Ukhtee yau ni kike yiwa ƙyauya ? Ai anjima kaɗan za ki zo ne .

Shafa kan ta Youssoufa yayi wanda ya sha adon ribbons irin na yaran gata da ya dace da lallausar sumar kan ta mai tarin yawa da yake sake fiddo kyaun ta da ido bai gajiyawa wajen kallon ta.

"Ki rabbu da ita Fatima kin iya shigga tsakanin ɗiya da Mahaifin ta ?

Girgiza kai Falmata tayi tana mai matsowa jikin sa ta kwantar da kan ta ta ɓarin jikin sa na dama ita da ukhtee fuskokin su na kallon juna akan ƙirjin sa .

Haɗa su yayi ya rungume bayan ya sumbanci kan Falmata da yake ƙirjin sa. "Fatima-zahra ina son ku irin son da ba shi da iyaka.

"Biyamuradi Youssoufa mu ma haka muna ƙaunar ka irin ƙaunar da bata da iyaka.

Direban da yake iya jiyo sautin su sai ya ƙara volume ɗin radio da waƙar matashiyar mawaƙiyar nan camelia jordana mai taken mens moi take tashi cikin baitukan ta inda take cewa  :

"Je rougis je rougis je rougis
Quand tu me souris
Ô tes yeux menthols
Me mentent et m'affolent

"Oh mens-moi si tu m'aimes
Mais me manque pas
Me manque pas
Me manque pas

"Je défaille à tes mots fous
Mots doux vaudous
Quand je suis dans tes bras
Hé dis, tu penses à quoi ?

Abuja

Sofi lokacin da ta bar gida bayan ta ci uwar wahala kafin ta samu ɗan tasi ɗin da zai yadda ya ɗauke ta taje ta sayar da ɗankunnen gwal ɗin da ya rage mata tal a kunnen ta ta biya shi kuɗin sa .

Daga nan wani ɗan ƙaramin hotel mai sauƙin kuɗi ya kai ta ta kama ɗaki ta shiga ta zauna a cikin dabarar ta da tayi niyyar ƙullawa na rufewa kowa maganar saki ukun da Hamza ya yi mata har sai zuwa lokacin da aikin boka ya ɗau wuta akan Hamza shi da kansa ta san zai fara neman ta daga nan idan ta gama wana shi ta rama duk irin cin mutumcin da ya mata sai ta nemi da su rufe zancen sakin a tsakanin su kada kowa ya ji su koma su cigaba da zaman su..

Tasha alwashin sai ta walakanta rayuwar Yakaka dan ta ma fasa kashe ta da wuri sai ta mata gashin ƙuma sannan za ta ƙarar da numfashin ta a doron ƙasa..

Kashe wayar ta tayi ta kwanta amma ta gagara bacci saboda tsamin da jikin ta yayi yana mata ciwo na fitar hankali .

Dole ta sa ta tafi asibiti aka bata magunguna ta zo ta sha .

Daren ranar haka ya ƙare mata tana surutan iska .

Washegari kuwa da farar Safiya ta dasa zaman ƙiran Samy Baby sai dai layi ya ƙi shiga wasa-wasa sai da ta shafe tsawon yinin ranar da waya a hannun ta tana ƙiran layin da Samy Baby ta ƙira ta da shi har wayar chaji ya ƙare ta mutu bata samu ta shiga ba

Ta lallaɓa ta sayo kan chaja ta zo tasa bata jira wayar ta cika ba ta dasa daga inda ta tsaya wajen ƙiran layin Samy Baby .

Kafin cikar kwanaki uku Sofi tayi ƙaramar hauka a ɗakin otel saboda dai babu wani saƙo daga Samy baby babu alamar sa kuma ita ta gagara samun ta sannan kuma ko alama bata ga ƙira daga wani nata ba da da har kashe wayar take dan kar a ƙira ta.

Doctor Hamzan da take hasashen aiki ya fara cin sa kuwa duk lokacin da taga alamun Kamfanin Sadarwa sun tura mata saƙo zato take shine .

Haka zata yini sambatun ƙiran sunan sa.

Kafin cikar Sati kuɗin hannun ta ya ƙare da daman fiye da rabi zama take da yunwa tana biyan kuɗin ɗakin da take kwana .

Ala tilas ta fita daga Otel ɗin kawo yanzu kwakwalwar ta ta ƙara birkicewa ta kasa yarda da abun da ya faru da ita yake kuma sake faruwa da ita .

Ciwon mazaunan ta da suka ɗuri ruwa tun ranar da ta yanke shi yafi kome ɗaga mata hankali saboda azabar da take sha kullum dare bata iya bacci .

Ba arziƙi ta kama hanyar gidan su a birkice kamar sabuwar mahaukaciya .

Da zuwa zata sake dasa sabuwar ƙarya ta tarar da ashe tuni kome ya jima da kwaɓe mata asirin ta ya daɗe da tonuwa kowa kuma yasan abunda ya faru abunda ta aikata da irin hukuncin da Hamza ya yanke mata .

Babban tashin hankalin ta yadda tana ji tana gani Baban su da ya dawo ƙasar kwanaki biyu da suka wuce ya kore ta a gidan bayan ya ƙare mata tanadi .

Gidan wata dangin dangau ɗin Hajiya Kori da take mata kore a can irin unguwannin kusa da ƙyaukan Abuja nan Hajiya Kori ta sa direba ya kai Sofi ba tare da sanin Mahaifin ta ba domin idan ta shi ne kawai Sofi tayi tafiyar ta Momy kori ta ce ta zauna a can kafin Baban ta ya huce ya saurare ta .

Bata haƙƙaƙe da babu wata sa'a da ta rage mata a rayuwa ba sai da aka shafe fiye da kwanaki arba'in tana ƙirgawa babu Samy Baby ba labarin ta .

Zuwa lokacin ta haƙiƙance cikin biyu ɗaya ne ko dai Samira ta yaudare ta ta mata damfara ta gudu a duniya ko kuwa ta gamu da mummunan hatsarin da ya rutsa da rayuwar ta a can india ba tare da an mata aikin da ta aiketa yi ba .

Ƙurunƙus sai gaba ɗaya mummunar zuciyar ta da shaiɗan da bai riga ya gama cika aikin sa akan ta ba suka cigaba da mata raɗa cewar ai babu wani amfanin da rayuwa za ta iya sake mata nan gaba .

Dan haka sai kawai ta afkama shaye-shayen miyagun ƙwayoyin da basu cika tsada ba sai mugun aiki dan da haka kaɗai take iya samu ta hasko kan ta a irin rayuwar da ta kwashi shekaru tana tsarawa a kan ta ita da Doctor Hamza.

Kafin wasu watanni ta yiwa rayuwar ta illa ga kuma ciwon da yake daɗa cin jikin ta gaba ɗaya ta sururuce ta koma irin mutanen da ƙwaya ta gama musu illa a rayuwa suka zama marasa amfanin da ba zasu iya yiwa kan su ba ma bare su yiwa wani .

To ai daman a rayuwa muddin Shaiɗan ya zama jagorar ka ba zai kauce ba har sai ya kai ka tsakiyar kogin nadama da ba kuma za ka iya fiddo da kan ka ba.

***

Yakaka da Doctor Hamza kamar kullum suna kitchen da safe suna aikin su tare da dai mafi yawan aikin Doctor Hamza ne ke yi saboda kome Yakaka ta ɗauka za tayi sai ya hana yace kar ta wahalar da kan ta da Babyn sa .

Suna gaf da kammala haɗa abun Breakfast ɗin su tattabarun rannan suka sauƙo sai dai a yau su uku ne tare da su da 'yar wata matashiyar tattabara da duk alamu ba'a jima da fara fita da ita kiwo ba.

Da sauri Yakaka ta nuna masa su tana cewa "Laa Habibi ka ga tattabarun mu na rannan har sun samu baby ko ba su bane .?

Da sauri Doctor Hamza ya mayar da ganin su kan sa yama dariya yace "ai kuwa sune wai har sun haihu ? Gaskiya sun yi ƙoƙari .

"Ba dan nima dai ga nawa Babyn yana hanya ba ai da sai nace sun cinye mu a wasan .

Dariya Yakaka tayi tana ɗiban 'yar shinkafa ta watsa musu kafin ta taya shi su kwashe abincin karyarwar su kai falo .

Bayan sun gama brakfast suka yi wanka Yakaka ta taya shi ya shirya suna yi suna 'yar soyayyar su da ba'a cika magana a cikin ta sai da suka fito za ta masa rakiya yana riƙe da kunkumin ta sannan yace "Wafaa  kin ga na manta har zan fita ban sanar da ke ba ƙanwar abokin aikina da yake nan unguwar ai kin san shi ko Doctor Abdallah ?

Gyaɗa kai Yakaka tayi tana jin zuciyar ta na sauya bugu da ba ma zata iya bada amsa da baki ba.

Murmushi Doctor Hamza yayi yana mayar da ƙofa ya rufe ya jawo ta jikin sa ya matso da ita Sosai cikin ta ne kawai ya tokare ya hana haɗuwar ƙirjin su .

Muryar sa a ƙasa-ƙasa yace faɗa min meye a zuciyar ki na ji ta sauya bugu me kike tunani ?

Girgiza kai ta sake yi cike da ƙagautuwa ta ji ƙarshen zance tace "ba kome , habibi me ya faru da ƙanwar Doctor Abdallah ?

'Yar sassauƙar dariya yayi ya jaa karan hancin ta kafin yace " sunan ta Madina ma'aikaciya ce a ƙungiya mai zaman kanta da take bada tallafi ga kasashen da annoba ta fadawa a sakamkon yaki ko na ɓullar cutuka watau NGOs babbar ma'aikaciya ce a kungiyar da bata dade da da dawowa daga...

Cike da gundura Yakaka ta Katse shi "Habibi mana to ni meye alakata da ita?

Wannan karon dariyar da yake gintsewa ita ce ta bayyana ya shiga kyakyatawa ganin haka yasa idanun Yakaka cika da ƙwalla ta fara ƙoƙarin zamewa ta bar gurin .

Da sauri ya riƙo ta gaba ɗaya ya rungume ta a jikin sa yana dai-daita nutsuwar sa daga barin yin dariyar da yake yace "Wafaa aina kika koyi kishi haka un ?? Haka kike sona ashe ? Ki kwantar da hankalin ki Wafaa ni naki ne ke kaɗai da yardar Allah babu wacce zata sake ratsa tsakanin mu ke kaɗai kin isheni rayuwar duniya kin ji ko ?

A tare suka yi ajiyar zuciya kafin ya cigaba da cewa "Abdallah shine ya bani labarin ƙanwar sa da shirin da take yi na tafiya Maiduguri domin yin aiki dalilin da yasa ya min zancen domin ya ji yaya lafiyar garin yake ? To bayan na ba shi amsar da ta dace shine har ma na ɗan ba shi bayani akan labarin rayuwar ku yadda kuka kasance a matsayin 'yan gudun Hijira har ma ya sake jimantawa to ashe ya faɗawa ita ƙanwar ta shi sai jiya yake shaida min cewar wai na nemawar Madina izni idan har kin amince tana so ta zo yau ta ɗan tattauna da ke kan yadda rayuwa ta kasance muku a Sanadin Boko Haram .

Ya ɗan tsahirta kafin ya ɗora da cigaba da cewa "Wafaa da fatan ban saɓa miki ba da na bada wani ɓangare na labarin ku ba tare da amin....

Da sauri Yakaka ta rufe masa baki da lallausan hannun ta tana girgiza masa kai  tace "Habibi kar kace haka ni wallahi baka min laifin kome ba ina maraba da Madina kace ta zo insha Allah za ta iya samun duk wasu bayanai daga bakina daidai gwargawdon yadda rayuwar mu ta kasance .

Sumbatar ta yayi a goshi kafin ya sake ta yana jin yadda take ƙara shiga ransa saboda sanyin halin ta .

Daga nan rakiya ta masa ya tafi cike da kewar juna da suke ji a koyaushe idan zasu yi rabo da juna ko da na awa guda ne .

Bayan ta dawo cikin gidan da ƙwazo irin nata ta gyara gidan tsaf tana yi tana hanzari tana duba waya dan kar lokacin ƙiran ta kula da Ukhtee yayi .

Ta gama ƙarfe tara cif tana zama kuma Falmata ta ƙira ta a skype bayan sun gaisa Falmata tana tsokanar ta Maman biyu sai ta haɗa Su da Ukhtee ita ta shiga lectures.

Da kamar kullum idan za ta shiga lectures da take yi a sati sau uku Ukhtee bata yarda da mai rainon ta ta riƙe ta har Falmata ta gama ihu za tayi ta yi tana kuka .

Sai fa idan an ƙira Yakaka a Skype an haɗa su nan ne kuma babu ruwan ta da Falmata bare wata mai raino za tayi ta damuƙar wayar tana gwalatu da dariya Yakaka na biye mata tana mata wasa har tayi bacci idan ta farka kafin Falmata ta fito Yakaka za'a sake ƙira ta kula da ita ta waya .

Wata irin ƙauna da shaƙuwa ce ta ban mamaki a tsakanin Su biyu yadda Ukhtee ta gane da Falmata da Baban ta haka ta gane da Yakaka haka kuma take son ta .

Sai da ta gama mata wasa ta samu tayi bacci sannan suka yi sallama da mai rainon ta ajiye wayar fuskarta ɗauke da murmushi tana jin ƙarin ƙaunar Ukhtee na bin jikin ta "daga an yaye ki zan je na ɗauko ki takwara koda kuwa Baban ki baya so sai dai yayi haƙuri sa samu wasu bayan ke amma ke kam tawa ce 'yata 'yar gidana.

Ta furta hakan a sarari dai-dai lokacin da aka ƙwanƙwasa ƙofar gidan.

A hankali ta miƙe tana ɗan tura cikin ta gaba da duk cikin watannin sa biyar amma yayi girma sosai "Matar likita ko 'yan tagwaye zata haifa ?

Lokacin da ta buɗe ƙofar sai ta ci karo da wata kyakkyawar mace da zata girme mata da kaɗan a shekaru wacce kallo ɗaya tal za'a mata a hango tarin ilmin Boko da wayewar da suka samun wajen zama na dindin a tare da ita bayan hutu da yake numfasawa a jikin ta .

Daga kan takalman ƙafafun ta marasa tudu har kan ɗan farin gilashin da yake saƙale akan doron siririn karan hancin suna nuni ne da irin tsadaddiyar rayuwar da take yi ta 'ya'yan gata 'ya'yan manya.

"Madina ce .

Yakaka ta aiyana hakan a cikin ran ta kafin ta ɗan sake faɗaɗa fuskar ta da murmushi  cikin muryar ta mai sanyin ta ce "sannu da zuwa ki shigo mana .

Da taƙaitatciyar Sallama ta shiga gidan kamar yadda fuskar ta ma ke ɗauke da taƙaitatcen murmushi.

Bayan sun gaisa Yakaka ta kawo mata zoɓo mai sanyi da yake tashin ƙamshin kayan shai irin na mutan Ndjamena da take ƙamshin ya ɗau hankalin Madina '

Bayan sun ɗan taɓa hira lokacin da Madina take shan Zoɓon da daɗin sa yake ratsa ta "bata taɓa zaton irin wannan local juice ɗin yana da daɗi haka ba , ta aiyana hakan a cikin ranta.

Da ta gama sha sai ta fuskanci Yakaka sosai ta sake gabatar da kan ta tare da yi mata godiya da amincewar da tayi ta bata damar tattaunawa da ita .

Cikin jin daɗi Yakaka ta ce ita ma tana godiya daga haka shiru suka ɗan yi Yakaka tana ɗan satar kallon Madina wacce take shafa fuskar haɗaɗɗiyar ipad ɗin ta har dai ta kai inda take son zuwa ta ɗago kanta.

Fuskar ta a sake tace "Amina zan so ki bani labarin yadda rayuwa ta kasance muku bayan da 'yan tawayen Boko-haram suka tarwatsa garin ku wanne irin tallafi kuka samu daga ƙungiyoyin bada agaji na ƙasa da ƙasa ? shin kun samu taimako ?  sannan a wane hali kuka kasance kafin taimako ya zo muku da kuma bayan taimakon ya riske ku.?

Shiru Yakaka ta ɗan yi sannan ta mayar da ganin ta kan kyakkyawan agogon hannun Madina tamkar mai nazarin lokaci kafin ta buɗe bakin ta a hankali cikin sanyi muryar ta tace .

"Mafarin Hargitsin Rayuwar mu ya fara ne ni da ƙanwata Falmata sanadin 'yan tawayen Boko haram da suka sa muka tsinci kan mu a matsayin 'yan gudun Hijira.


Tammat Alhamdulillah .

Alhamdulillahi.Alhamdulillah. Alhamdulillah Godiya ta tabbata Ga Allah Maɗaukakin Sarkin wanda ya bani ikon Farawa da gama litaffin nan da na ɗau tsawon watanni Ashirin da kwanaki shidda  ina rubutun sa tsakanin faɗi-tashi na rayuwar yau da kullum tare da juyin yanayi tsakanin zafi da sanyi da ruwa da iska babu shakka Allah shine abun godiya .

Ina roƙon Allah ya yafe min daga abunda ya kasance kuskure na rubutu kasantuwa ta 'yar Adam mai cike da rauni da tarin laifuka ( Allah na tuba ) sannan abunda yake na lada Allah Ubangiji ya karɓa ya ɗora shi bisa mizanin kyawawan aiyukana ( Amin )

Sannan godiya ta marar yankewa ta tafi ne gare ku masoyan rubutu na da baki ba zai iya lissafa adadin ku ba Wattpidians wanda da kuka yi jimirin bibiyar rubutuna tsakanin lokaci mai tsawo da yake cike da tsaiko mai tarin yawa daga gareni , babu shakka ƙauna ce sila kaunar da ku ka nuna ita ta ban ƙwarin guiwar da har ta kai a yau muka kawo ƙarshen littafin tare da ku ,  hakika kalmar nagode tayi kaɗan wajen bayyana muku godiya ta sai dai nace Allah ya saka muku da alkhairi nima Ina ƙaunar ku saboda Allah .

Godiya ta musamman ga ƙawa kuma 'yar uwa Fatima Salim aka Batul Mamma da ba domin ita da tarin gudumawa da alkhairin ta a bisa rubutun littafin nan ba da fa tafiyar bata miƙa ba nagode ƙwarai ƙwarai Sister Fatima Allah ya bar ƙauna.

Yabo tare da Fatan Alherin ya tafi ne baki ɗaya ga Yayana kuma Malamina Sheikh Muktar Yaa Allah ya saka da alkhairi Yaa Mukhtar kalmar nagode tayi tsororo a tsakanin mu sai fatan Allah ya bar ƙauna .

Sannan akwai tarin masoya masu daraja da littafin Mafari ya zama sanadin haɗuwar mu amma ƙaunar mu sai tayi ƙarƙon da ta zarce dalilin haɗuwar Littafi daga cikin su Akwai baki ɗayan jama'ar group ɗina na Mafari fans .

Sannan  'Yar uwa kuma jagorata a harkar rubutu Sumayyah Abdulkhadir Takori , tare da ke da dukkanin jama'ar ki na Takorities ina godiya a gare ku tare da ƙaunar ku Allah ya bar zumunci .

Jama'ar Batul Mamman na KDM ina godiya da yawan ƙaunar ku .

Nafeesa Tafeeda tare da jama'ar ta na Maman Mama novels.

Sister Amina Mafari fans Group admin Jameela aka Meela ,Raliya Garba Zulaihat rano , Zahra aka donutfairy ,Maryam Talba ,Auntie Aisha , Fadeela Khabeer godiyar ku ta musamman ce Allah ya bar Kauna.

da da da da Masoya haƙiƙa kuna da yawan da ya wuce fa na ƙirga ku musamman dai da yake ai kun san ƙyuiya irin tawa ah to da ya muka sha a

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login