Showing 252001 words to 255000 words out of 411050 words

Chapter 85 - MAFARI COMPLETE BOOK HAUSA NOVELS BY UMMU MUAZ.txt

10 Sep 2025

14337

a ƙasar su kuma mai ilmin addini da na boko tun a wancen zamanin .

" Bayan auren mu mun zauna shekara guda a N'Djamena kafin aikin mahaifin ku ya ƙare da ƙasar mu , muka kuma fara shirin komawa ƙasar su ,

"a kuma tsukin wannan lokacin Allah ya yiwa Mahaifin mu Rasuwa sakamakon sukar sa da wuƙa da wasu ga cikin 'yan firsina suka yi a ƙoƙarin su na gudu daga gidan yari .

"Mutuwar Baban mu ta gigita mu ganin cewa duk wani gatan da muke da shi ya ƙare ,

"a ƙarshe dole muka haƙura , riƙon Rahima kachokam ya dawo hannun mu da duk wasu ɗawainiyar ta Al-Mustapha ke yi ,

"Sauran ƙannena maza suka raɓu da gidajen 'yan uwa  , ,

"Ba mu jima ba bayan nan muka koma Nigeria tare da Rahimatullah da   kuma kai a lokacin kana ɗan jariri .

"na fuskanci tsangwama da ƙiyayya iri-iri daga kakar ku , da dangin mahaifin ku da baki ɗayan su basa ƙaunar auren mu , idan aka ɗauke Salman wanda ƙani ne na uku ga mahaifin ku da shi babu ruwan sa da duk wasu lamura da suka shafe ni .

"Haka shekaru suka yi ta tafiya tare da nasarar rayuwa , matsala mafi girma da ta zama sanadin rabuwar auren mu da mahaifin ku ya samo asaline daga lokacin da Soyayya ta shiga tsakanin Salman da Rahimatullah ,

"lokacin Rahima ta gama makarantar gaba da primary , kai kuma ka shiga makarantar kwana ta gaba da primary ,

"rikicin an ɗauki lokaci ana yin sa tun bayan bayyanuwar soyayyar su da suka yi shekaru biyu suna boyen ta a tsakanin su ,

"Salman ya doshi mahaifiyar su da sauran 'yan uwan sa da batun auren Rahimatullah , ƙaramin yaki aka yi a tsakanin su saboda lokacin kakan ku ya jima da rasuwa .

"Lamari yayi tsamari da yasa har kakar ku ta ƙira mahaifinku ta masa kashedi kan muddin yana son Albarkar ta , ya zama dole ya raba tsakanin ƙanwar matar sa da ƙanin sa ,

"daga lokacin shima Mahaifinku ya fara nuna adawar sa da soyayyar tsakanin Salman da Rahima domin bin umarnin Mahaifiyar su , da hakan ya kawo saɓanin a tsakanina da shi domin ni ɗari cikin ɗari nake tare da su akan lamarin soyayyar su .

"ana cikin wannan hatsaniyar uwar matar da aka so aurawa Mahaifin ku wacce take ƙanwar kakan ku ce ta zo da wani lamari mai yanayi da tsafi ko kuwa chanfi  , kan cewa muddin ba'a yi gaggawar raba tsakanin Salman da Rahima ba to babu makawa guda a tsakanin su zai mutu , domin Malamin ta yace babu aure a tsakanin su , '

"Maganar bata ɗaga min hankali ba sai da naga kamar Mahaifinku ya yarda da batun inda har ya fara maganar ko dai Rahimatullah zata koma N'Djamena na ɗan wani lokaci , idan kome ya lafa ta dawo ,ranar nayi kukan Maraicin mu da rashin gatan mu  ,

" an yi haka bai fi da wata guda ba , Rahima ta gama shan kukan ta akan wannan batun , Babban Al'amari ya afku,

"Ranar wata juma'a bayan Rahimatullah da Salman sun gama hira da rabin ta neman hanyar warwaruwar matsalar su suke tare da kaiwa ga cikar burin su ,

"ƙarfe biyu da rabi na ranar bayan sallar juma'a labarin Rasuwar Salman Dilmari matashin Saurayi, ya bazu tare da yin tambari a baki ɗayan birnin Maiduguri kasancewar sa matashin ɗan siyasa da ya yi suna a lokacin ,

"ya rasu a sakamakon mummunan haɗarin mota da yayi akan hanyar sa ta komawa daga masallacin juma'ah mintoci arba'in da rabuwar su da Rahima ,

" mutuwar data girgiza zukata da dama , ta kuma bar miƙi a zuciyoyin wasu da dama , Salman Mai Alheri ne , Allah ya gafarta masa ,

Shiru ne ya ratsa tsakanin su saboda kuka haiƙan da Rahima take yi , kukan tasowar tsohon miƙin dake zuciyar ta da ya tarad sabon ciwukan dake cin ranta a kullum kwanan duniya ,

Mutuwar  mijinta uban 'ya'yan ta da ta tarar da gawar sa a yashe cikin gona , haka kuma tana ji tana gani ta tsallake shi domin ceton ranta da na 'ya'yan ta ta tafi ta bar gawar sa a daji,  tare da ɓacewar manyan 'ya'yan ta da har yau bata da sanin haƙiƙani kan rayuwar ko mutuwar su ta ma fi haƙaƙewa akan Yakaka da Falmata sun mutu kamar yadda harsashi ya samu Baana yayar Bulama ta mutu akan cinyar ta ,

Bakin lafayyar ta Amne ta sanya ta sharewa Rahima hawaye sannan ta cigaba da cewa ,

"Fasalta irin halin da baki ɗayan zuri'ar Dilmari ta samu kanta a ciki bashi yiwuwa ,

  "ai ka san lokacin kana da wayo sosai kana secondary School ,

gyaɗa kai Hamza yayi wanda idanun sa suka yi jaa ,

" Rahima ta shiga ɗimuwa marar misali domin har suma ta dunga yi , sai da Maigadin gidan ku na lokacin ya dunga yi mata rubutu , cikin sati guda da mutuwar sa Rahima ta rame tamkar majiyanciya , ni da kaina ƙarfin hali nake yi , nake hana kaina tunani saboda tsohon cikin Rahima ƙarama da nake ɗauke da shi .

"abu mafi muni da ya biyo bayan mutuwar Salman shine takowa da 'yan uwansa suka yi har gida bayan kwana arba'in da mutuwar sa , suka ci mutuncin mu ni da Rahima , a ƙarshe suka danganta mutuwar Salman da cewa ni da Rahima muka lashe masa kurwa muka kashe shi , to waye ya san salsalar asalin mu ??

"Ni kuka Rahima kuka , sannan abun takaicin mahaifinka yana zaune ya gagara hana su ko ɗaukar wani mataki na ba mu kariya , wanda hakan ni kuma ya tunzuro ni , na yunƙuro domin maida musu martani a karon farko bisa duk abubuwan da suke min marasa daɗi ,

"Ga maɗaukakin mamakina sai mahaifinka ya hayyaƙo min ya takore ni daga yin magana har ma yace muddin nace wani abu kome zai iya faruwa ga igiyoyin auren mu ,

"bisa tilas nayi shiru sai hawaye da muke yi ni da Rahima suka gama zage mu tas har da dungurin Rahima da alama ma duka suke da niyyar yi mata sai ɗan uwansu ya rarrashe su ,

'tundaga wannan ranar Rahima ta sake yin sanyi duk ta susuce firgici ya bayyana cikin suffar ta bata da aiki sai tunani   ,

"duk da ceqa ina bin duk wasu hanyoyi domin kwantar mata da hankali duk da cewa nima hankalin nawa a tashe yake domin tsakanina da Mahaifinku babu daɗi , nema yake ƙarfi da yaji ya raba Rahima da gidan sa wanda nasan zugar 'yan uwansa ne da ni kuma ko kusa bazan lamunta ba , idan Rahima ta bar wajena ina zata ??

"har zuwa safiyar wata rana da na wayi gari Rahima kin yi gaban kan ki wajen barin Rayuwata , kin tafi kin barni cikin tashin hankalin da ya tunkuɗo min da naƙuda ,

"kika tafi ba tare da kin yi tunanin me hakan zai haifar ba cikin rayuwata ,

"duk wani wajen da nake tunanin zaki je Rahima naje neman ki har ms da wuraren da baza ki ba naje neman ki ,

" a cikin halin nan na matuƙar tashin hankali na haifi jaririyata da tun lokacin da na haife ta na shaidawa mahaifinku sunan ta Rahimatullah .

" da ɗanyen jego na dunga fita kusufa-kusufa neman ki da hakan ya tunzuro Al-Mustapha yace muddin na sake fita neman ki da kaina a bakin auren mu ,

" a wannan ranar nima zuciyata a taurare take da zafin rashin ki dan haka nima na taso masa , a take a wajen na nemi da ya sawwaƙe min auren sa tun a nan domin kuwa fita neman ki yanzu na fara har sai ranar da na ganki ,

"shima da alokacin yake ganin zallar laifin ki na cewar ai ke da kan ki kika ga damar tafiya dan haka zaki dawo ,

"a fusace a wajen ya datse igiyar auren mu ba tare da yayi la'akari da irin raunin dake tare da ni ba ,

"Ban kwana a gidan ba na tafi tare da jaririya Rahima , na bar masa Hafsa da Zainab Hamza kuma yana makaranta,

" nayi neman ki Rahimatullah har N'Djamena naje an tabbatar min da baki zo ba ƙarin tashin hankalina shine duk sauran ƙannena a cikin matsanancin talauci suke ,

" Na tattara musu duk wasu 'yan kuɗaɗen da na tafi da su na basu , na sake dawowa Nigeria , tare da taimakon ƙawayena biyu Hajiya Hadiza da Hajiya yaana , na sayar da tarin sarƙoƙi da ƴan kunnayena zuwa wara-waren zinare da nake da su , na sayi gidannan da muke ciki , na ɗora neman ki daga inda na tsaya saboda na tabbatar kina Nigeria wataƙila gari kika sauya , meyasa kika min haka Rahima ???? 

"aina kika rayu ? Ina mijinki kina da wasu 'ya'ya ne bayan wannan na cinyar ki ? Idan kina da su suna ina ??

Amnee ta ƙarasa bada labarin rayuwarsu da ɗora tambaya ga Khaalty Rahima wacce idanun ta yayi jazir tsabar kuka ,
B
Tausayin yayarta ya cinye zuciyar ta , ashe haka ta shiga damuwa akan rashin ta ??

ƙasa take son sharewa tayi rubutu ,

Amnee ta miƙe ta kawo mata takarda da biro , ta sanya hannu biyu ta karɓa ,

taƙaitatcen rubutu tayi a jikin takardar ,

" tsoron kar na zama sanadin rabuwar auren ku da Yaya mustapha yasa na tafi daga gareku ukhtee Amina ki yafe min , bansan ba zan zama sanadin tarwatsewar jin daɗin rayuwar ku .

"Mairambiri shine sunan ƙauyen da na rayu tsawon lokaci a cikin sa kafin zuwan yan tawayen boko haram su tarwatsa garin su kashe mijina da manyan yarana biyu mata da suma nake zaton sun mutu , Amina da Fatima shekaru shida yanzu da mutuwar su .bayan su ina da wata 'ya da ita ma harsashi ya same ta ta mutu , a yanzu Bulama shine kaɗai ɗana .

ASSALAMU ALAIKUM

'Yan uwa ina miƙo saƙon gaisuwata tare da fatan Alheri gare ku baki ɗaya , ina kuma mai yabawa bisa ga yadda kuke nuna ƙaunar ku ga littafin nan ,

nagode .

  [11/22, 12:05 PM] Zuraiyah Zuzu 🌟: MAFARI
( Hargitsin Rayuwa )

Umm'muaz






39





Duk yadda Falmata take tunanin daɗin dake ga mallakar idanu ta tadda shi ya wuce haka , jin kanta take tamkar sabuwar halitta ,

Har bata so bacci ya shiga tsakanin ta da ganin hasken duniya , karambani kuwa babu irin wanda bata yi , har girki take karambanin yi Yousssouf kuwa yana taya ta ,

Shima a ɓangarensa baya gajiya da duk wasu tambayoyi da ko karambanin da zata yi , wani irin son ta yake yana riritata ,

Mama da kanta tasan cewa yanzu Mamarta ta samu waraka saboda wata kulawa na musamman da idanun ta sun hango mata wani ɗan datti a jikin kayan Mama zata yi maza ta gyara ta ta sauya mata wani ,

A kullum ta Allah sai ta miƙa godiyar ta ga Youssouf kamar yadda cikin duk wasu sallolinta sai ta ƙara godewa Allah akan wannan babbar kyauta da ya yi mata na dawo mata da ganin ta ,

Godiyar da take yiwa Youssouf ba a fatar baki kaɗai ta tsaya ba , har a aikace take gwada masa ta yadda take nuna masa ƙauna tare da ɗaukar buƙatun sa ba tare da gajiyawa ko ƙorafi ba .

Kamar yadda likita yace tana cigaba da zuwa ana dubata , babu wata sabuwar matsalar da ta ɓullo tunda aka yi mata aiki .

Idan tana da wata damuwa to ta lafiyar Mama ce wacce kwana biyu ciwon ta yake ƙoƙarin tasowa suna danne shi da tarin magunguna gami da ƙara ƙaimi wajen kulawa da ita , amma duk da haka kallo ɗaya za'a mata a iya hango tarin raunin dake tare da ita tun daga cikin raunanan idanunta da suka ɗan sauya launi zuwa ruwan ɗorawa har zuwa ƙafafunta da hannayenta da suka ɗashe suke yawan ɗaukar sanyi ,

Gaba ɗaya Falmata da shi kansa Biyamuradi Youssouf basa tare da walwala sosai ,

"Baban Mama ko dai za'a sake komawa asibitin nan ne maganar aikin Mama ,

Youssouf wanda yake shafa kan Mama wacce take kwance cikin jikin sa lamo , ya ɗago kan sa yana duban idanun Falmata da suke nuni ƙarara da damuwar da ruhin ta ke ciki ,

"Fatima duk wassu bayanai da zamu sake samu daga Doctora basu wucce batun baya da sunka faɗi muna , wanda kouma mun bar Lamari ga Allah zouwa lokacin da za'a samu damar yin aikin ,

Shiru tayi tana cigaba da kallon sa , cike da damuwa , so take yayi wani yunƙuri kome ƙanƙantar sa ,

Ji yayi gangar jikinsa na karban sakon dake fitowa daga cikin ƙwarar idanunta masu kyaun kallo ,

"idanun ki suna da kyau idan kina kallon Mutum da su Fatima , lokacin da basu da Lafiya kyan su bai kai haka bayyana ba , kina da sassanyan kallo Mai cike da nutsuwa ,

Murmushi tayi kaɗan , kafin ta ƙira sunan sa ,

"Baban Mama ,

Sai kuma tayi shiru ,

Kamo hannunta da yake kusa da shi yayi ya riƙe ,

"Ummh ina jinki menene ?

" daman nace ko zamu je ni ɗin a gwada ni  ?

"gwaji Fatima wanne irin gwaji , akwai damuwa ne ga lafiyar jikin ki ?

Sunkui da kan ta ta sake yi tana jin nawin zancen akan harshen ta , sai dai tana jin zata iya yin kome domin ganin Mama ta samu lafiya , muryar ta a ciki tace ,

"ko Allah zai sa a dace un-un ko wai a jikina akwai abunda da za'a iya amfani da shi wajen yiwa Mama maganin ,

Kiris ya rage Biyamuradi Youssouf ya kwashe da dariya , sai dai ya gintse saboda yana son jaan ta ,

" Fatima kin manta likita yace ke baki iya bada jinin ki ?

Cikin sauri ta katse shi ,

" ai ba jini na ba , wai a auna ko akwai cikin ?

" ciki aina ?

Yace da dariya a cikin sautin sa,

Ɗago kanta tayi tana iya hango hasken haƙoransa da yake dariya,

" un-un a jikina ko ?

Dariya ya kwashe da ita , cikin ransa  ƙaunar ta na sake yawaita , kunya da kawaicinta yana burge shi haɗi da salon rashin wayewarta da baya sa ta fidda tsagoron ƙauyencin ta .

"Fatima ciki ai sai ya nuna Alamunsa tukun ake zouwa ayi gwaji , hakanan bai yiwuwa aje ga gwajji sai a mouna dariya ,

Shiru Falmata tayi tana ganin wautar kan ta , to ita ya zata yi ne ? Ta matsu Mama ta warke ta samu lafiya kamar sauran Yara , tsintar kanta tayi da addu'ar Allah ya nufe ta da samun ciki nan kurkusa domin lafiyar Mama ,

Daren ranar basu samu bacci ba saboda jikin Mama da ya tsananta idan banda nishe-nishe da ƙananun kuka babu abunda take yi , hankalinsu baki ɗaya a tashe , Falmata ta rungume ta anjima Youssouf ya ɗauke ta ya ɗora a jikinsa , haka suka yi ta fama .

Asubar farko a cikin tsananin sanyi suka nufi asibiti a take likitocin ta suka shiga bata kulawa ,

Ba'a fi awa guda ba ciwon ya lafa ta samu bacci , tana rungume a jikin Falmata

Ƙarar wayar sa ya sanya shi miƙewa daga kujerar da yake zaune ya ɗan taka zuwa wajen ɗakin yana ɗaga ƙiran da ake masa wanda yake daga Tafeeda ,

" Youssoufa akwai Al'amari maigirma da muni da yake tunkaro ka ,

Sune kalaman da Yaji Tafeeda ya furta masa ba tare da sun ko gaisa ba ,

Ji yayi ya cigaba da cewa ,

"Bayan tsawon shekarun da ka kwashe kana ɓoye kuskuren da ka aikata yanzu kome yana daf da bayyanuwa batare da ka farga ba mutanen da suka ɗau lokaci suna bibiyar sawun duk wani motsi naka ba tare da ka kai ga hankalta ba gaf suke da cimma nasara akan ka ,

"Ya zama dole ku dawo tare da kai da 'yar taka da matar da ka aurawa kan ka kafin kome ya lalace , mafi girman lamarin shine nan da kowanne lokaci Maimartaba tare da Hajiya umma zuwa kan iyalai tare da 'yan uwanka zasu iya sanin Mummunar Fuskar ka ,

" Maƙiya kuma zasu samu damar kassara ka , wanda kafi kowa sanin me hakan ke nufi ??

"Ta-Tafeeda , meke Faruwa ne yi gaugawar sanar min ,

"ni a matsayina na 'dan ouwa a gareka zan yi dukkanin bakin ƙokarina wajen ganin lamura basu munana fiye da ƙima ba , duk kuwa da cewa ni ai ba bakin koume nake gareka ba ,

Ɗut-ɗut !
Yaji ƙarar Alamun yankewar ƙiran
Tashin hankalin da ya zo masa a lokacin maigirma ne , me Tafeeda duk ya faɗa masa ??

"Tayaya ya san cewa tare yake da Fatima da Mama ? 

"Su waye maƙiyansa masu bibiyar rayuwar sa ?

"Fallasuwar Asirinsa a gurin iyayensa hakan na nufin ɗebe ƙaunar sa daga zukatan su ,

"wai shin me yake shirin faruwa ko kuwa ya ma riga ya faru  ??

Ya zama dole ya koma gida ,

Da sauri ya shiga neman layin Tafeeda sai dai har ta gama ƙara bai ɗauka ba , ya sake gwada ƙira a karo na biyu nan ma ba'a ɗauka ba ,

Tashin hankalin sa ya yawaita da har Falmata ma ta kai ga Fahimta , damuwar sa ta ƙara mata damuwa , sau biyu tana tambayar sa ko me yake damunsa ? Yana ce mata ba kome .

Kafin dare Mama ta warware dan haka suka koma gida ,

"Falmata ta haɗa ruwa mai zafi ta yiwa Mama wanka ta shirya ta cikin jibga-jibgan kayan sanyi , kasantuwar cikin magunguna da Alluran da aka yi mata akwai masu sa bacci bata jima ba bacci ya sake ɗauketa ,

Itama wankan tayi ta shirya cikin wondo wide-leg da

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login