Showing 174001 words to 177000 words out of 411050 words

Chapter 59 - MAFARI COMPLETE BOOK HAUSA NOVELS BY UMMU MUAZ.txt

10 Sep 2025

14383

ta tsiya ko ta arziki zai tafi da ƴar sa !

Gyaran murya prof yayi kafin ya ɗora da cewa ,
    Ɗa na mai zai hana idan har ka amince ka bar jaririyar nan a hannun ƴar uwar mahaifiyar ta har zuwa lokacin da ta ɗan tasa tayi wayo shekaru biyu zuwa uku sai ka dawo ka ɗau ƴar ka , baka ganin yanzu idan aka raba yarinyar nan ƙanwa ga mahaifiyar ƴar , zata shiga damuwa me tarin yawa ganin cewa har zuwa yanzu ba ta kai ga gyagijewa daga ruɗanin da mutuwar yayar ta ya jaza mata ba ,bugu da ƙari bata da kowa nata a halin yanzu sai ita wannan ƴar ta ka , ka duba magana ta da kyau ,
   Ya ƙarasa zancen da bada zaɓi ga Biyamuradi ,

Ba domin tun ganin farko da Youssouf ɗin ya yiwa prof ɗin ya riga ya cika masa ido da ƙwarjinin sa tare da cikar kamalar sa ba , sannan halin dattaku da mutuntaka da ya dunga nuna masa a kowacce haɗuwar su , mafi muhimmanci kula da rayuwar ƴar sa da yayi na wani lokaci ,

bayan haka da babu abunda zai hana ya kartawa prof rashin mutunci , ya kuma gwada ƙarfin ikon sa na soja , sannan da ƙafafar su ta sarakai da koyaushe abunda suka so shi ake mu su ba'a musa mu su , ya ɗauke ƴar sa yayi tafiyar sa , to amma girma prof nada yawa a idanun sa dan haka ya sassauta murya tare da saita nutsuwar sa yace

   Baba nan ba kassa ta ba , sannan ni kuma ai ma'aikaci ne , idan na tafi na bar ɗiya ta nan hankali na basshi kwanciya , chan inda zan tahi da ita nan ai shi tushe da assalin ta , kayi haƙuri baba zan tahi da ɗiya ta na ɗau Alƙawarin zan wanzu ina kawo ta lokaci zuwou lokkaci ta ga innon ta da yardar Allah ,

Shiru prof yayi yana jin tausayin falmata na kawo masa , bashi da wani ƙarfin iko akan yaran , bai haɗa kome da su ba idan banda taimakon su da ya biyo ta hannun sa dan haka shi baya da ƙarfin hanawa Biyamuradi ɗiyar sa ,
    Toh bari a ƙira ita uwar riƙon ƴar ta ji daga bakin ka , kafin gobe da zaka dawo ɗaukar ƴar ,

Rahima ce ta rako falmata a yau da kallo ɗaya za'a mata a gane gaf take da ɓarkewa da kuka saboda ƙiran da aka mata ta kawo baby mama
  
Daga gefe ta gurfana bayan ta gaishe da prof , tayi shiru ,

Fatima ga baban jaririya nan ya sake dawowa yau , miƙa masa ƴar sa ya gan ta ,

    shiru tayi bata ce ƙala ba

    A hankali Rahima ta zare baby mama daga hannun ta wacce take ta wasa da hannuwan ta idanun ta tar a buɗe , shirye take tsaf cikin jar riga ta jarirai mai haɗe da wondo da safa , kan ta lulluɓe da farar hular sanyi mai ratsin ado da fulawoyi jajaye ,

Hannun Youssouf har rawa yake lokacin da yake ƙarbar yar jaririyar , yana ƙarbar ta ya zarce da ita zuwa fuskar sa inda ya sumbanci kumatun ta zuwa goshin ta , bakin sa ɗauke da addu'o'i ya kama wannan ya Sake waccen ,

Farin cikin sa ya yawaita da har ya gaza boyuwa ya bayyana akan fuskar sa dake ɗauke da murmushi mai bayyana haƙora ,

maida ita ƙirjin sa yayi ya rungume ta rungumar da ke bayyana tsantsar so da ƙaunar da yake mata , ji yake kamar ya buɗe cikin ƙirjin sa ya ɓoye ta ,
   Da dariya akan fuskar sa ya ɗago cikin cewa
    Ɗiya ta girma sossai , hala wanni sinadarin ƙara wa jarirai girma da lafiya kuke bata ?  Madallah Madallah da ku , "
  
  Ɗan murmushi prof yayi , kafin ya maida ganin sa kan falmata wacce ta ƙagu a miƙo mata baby mama suyi tafiyar su ,

  Fatima kina ji na ko ?
Ina ji Baba
  Ta amsa da ladabi cikin muryar ta ,

Baban jaririyar nan ne ya zo yau yake shaida mana ya gama aikin sa da ya kawo shi nigeria nan ƙasar mu , dan haka gobe yake son komawa tare da ƴar sa , a shiryawa jaririya kayan ta kafin gobe ,

Tamkar kunnen ta ya toshe haka ta ji dumm , cikin kan ta , tana jin yadda kalmar a haɗa kayan baby mama za'a tafi da ita gobe yana bin duk wata gaɓɓa mai kuzari a jikin ta yana kassarawa ,
 
wanne azzalumi ne yake neman ta ƙarfi da yaji sai ya raba ta da jinin ta ɗaya tal da ta rage mata a duniya , ?

Da wani nisasshen yanayi cikin muryar ta ta ɗago kan ta tana saita idanun ta inda ta ji tashin muryar youssouf ɗin a ɗazu tace

Wanene kai ? Me muka maka kake son raba mu ? Aina kasan yakaka na ?meyasa kake ƙarya ?

  Shiru tayi tana jin yadda fitar numfashin ta ke sauyawa kafin ta ce cikin ƙarajin kukan da ya taho mata ,

ƙarya kake baby mama bata da BABA kai ba baban ta bane , yakaka ita kaɗai ta haifi baby mama , ina kake lokacin da yakaka take rashin lafiya akan cikin baby mama ? Ina kake lokacin da yakaka take shan wahala alhali baby mama tana cikin ta ? Aina kake lokacin da Yakaka na ta mutu sanadin haihuwar baby mama ??  Ƙarya kake kai mugu ne , ba kai bane baban baby kana so ne ka gudu da ita ,

   rarrafawa tayi inda ta ji sautin baba prof yana ƙoƙarin son katse mata maganganun ta ,

Illahirin jikin ta rawa yake lokacin da ta dangana da jikin kujerar da yake zaune ,

   ba-ba-Baba bani da kowa sai baby yakaka dan Allah kar ku bari ya raba ni da ita wallahi ƙarya yake yi maka , Baba ni miskiniya ce dan Allah kar ka bari ya zalunce mu ni da baby yakaka dan Allah Baba ,!
 

Wani irin yanayi me wuyar fassara prof ya tsinci kan sa a ciki ƙwarai da yana da iko da yau ya hana youssouf ɗaukar jaririyar nan ya bar ta a hannun yarinyar nan , "

Idon sa ya sauke akan Youssouf ɗin wanda kan sa yake sunkuye yana kallon fuskar ƴar sa ,tamkar bai san da bulayin da Falmata ke yi ba, sam baya so tausayin falmata da ya fara tsirga masa ya sanya shi barin ƴar da Allah ya jarabbe shi akan ta  hannun mutanen da ba shi da tabbacin zasu iya riƙon ta har tsawon rayuwar ta ba , kar watarana ta walakanta ko ta sha wuyar rayuwa , ƴar sa mace ce ƙwarai tana buƙatar uba a halin tafiyar rayuwar ta nan duniya ,

shi ya barranta daga samari irin sa waɗanda zasu samu haihuwa ta haramtatciyar hanya su ƙarawa kan su zunubi ta hanyar yin watsi da abunda suka haifa ko ma su kashe baki ɗaya , yana so ya ubangiji ya yafe masa akan zunubin da yayi ma ta hanyar samar da ita baya fatan shaiɗan ya sake jaan sa ya aikata wani zunubin da yafi wanda ya aikata a baya muni ,

Mayar da ganin sa prof yayi ga Falmata cikin sigar rarrashi yace fatima ki daina cewa jaririyar nan bata da Baba , alhalin ga baban ta nan a zaune  yana jin ki babu kyau haka , kiyi haƙuri ki bari ya tafi da ƴar sa yayi alƙawarin zai dunga kawo ta nan gidan gurin ki kin ji ko ?

sai lokacin Youssouf ya ɗago kan sa ya dube ta ,
   Ƙwarai nayi alƙawari ƙanwa ta,  zan dunga kawo ta zouwa gare ki har girman ta , ke ai har abada uwa kike a gare ta ,

Zumbur ta miƙe tsaye , cikin takun da kafafun ta ke harɗewa ta nufi inda take jin tashin muryar sa ,

  Hannun ta duka biyu ta miƙa da zummar riƙe sa yayi saurin kaucewa yana sake boye baby mama cikin ƙirjin sa ,
    Gefen rigar sa tayi wa wani ƙaƙƙarfan riƙo ba da wasa ba , Cewa take

  Dan Allah ! Dan Allah ka ji tausayi na ka bar min baby , Dan Allah kar ka raba ni da ita , zan mutu idan ka ɗauke ta , dan Allah .....
       Numfashin ta ne ya fara tsarƙewa dai-dai da ƙarasowar Rahima wacce prof ya yiwa umarni da ta janye Falmata  , hawayen tausayin Falmatan suna zarya a kumatun ta ,

Luuuu ta tafi baya ta faɗi bisa jikin rahima suka ƙarasa bajewa a ƙasa tare babu alamun numfashi ga Falmata ,

  subahannalahi innalillahi wa inna ilaihi raji'oon sune kalmomin da prof ke jerowa
   Rahima ƙira direba maza a kai ta asibiti ,
   Da sauri Youssouf ya waigo tare da sunkuyowa kan falmata ya tabbatar dai bata numfashi nan take ya sanya hannu a aljihun sa yana ƙiran direban sa , lokaci guda fuskar sa na bayyana ruɗanin da yake ciki yake cewa

   Daman bata da lafiya ne Baba ??
 
Prof bai amsa masa ba ,

Direban youssouf shi ya fara shigowa dan haka rahima ta fara ƙoƙarin ɗaga falmata sai dai ta kasa , saboda tayi mata nawi ,

Baby mama Youssouf ya miƙawa Rahima ,
   Lokaci guda ya sanya hannunwan sa biyu ya ɗaga falmata wacce take sume  ya fice da ita wajen motar su , direban sa ya buɗe gidan baya ya shimfiɗe ta ,

Ya karɓi baby mama daga hannun rahima tare da yi mata umarnin ta shiga su tafi ta gwada musu asibiti mafi kusa da zasu kai falmata ,

tafiyar mintoci biyar suka isa wani asibiti mai zaman kan sa , inda nan take likitoci suka rufu akan falmata suna ƙoƙarin dawo da numfashin ta dai-dai ,

Hankalin Youssouf baki ɗaya a tashe yake ya kasa zaune ya kasa tsaye , sai zirga zirga yake tsakanin kofar ɗakin da Falmata take yana rungume da baby mama , tsoron sa ɗaya kar yarinyar nan ta mutu a sanadin raba ta da yace zai yi da ƴar sa , idan haka ta faru bai san inda damuwar sa zata kai ba , "  ko kusa bai san haka take ƙaunar ƴar sa ba ,

ya kasa kintata yawan ƙaunar da ke tsakanin ta da yayar ta wanda yake da tabbacin son da take mata ne ya shafi ƴar ta , idan kuwa haka ne lalle falmata abar a tausayawa ce , ƙwarai ya kamata yayi adalci ya kuma duba anya idan ya raba ƴar sa da ita ya kyauta kuwa ?? Anya bai so kan sa dayawa ba kuwa ?

mintoci arba'in da shigar da ita ɗakin suka fara jiyo gunjin kukan ta , tana surutai ,
    Da sauri Biyamuradi youssouf ya ƙarasa gaban ɗakin dai-dai da fitowar babban likitan ,

Mun samu numfashin ta ya dai-daita kamar yadda muke zaton kun sani tana da asthma , toh ta samu attack ne , yakamata a dunga kiyayewa da duk wani abu da zai iya kawo mata wahalar numfashi , yanzu ku shiga akwai wanda take son gani a tsakanin ku , nan da ɗan wani lokaci kaɗan ma zaku iya tafiya gida ko awa ɗaya haka nan gaba !

Biyamuradi youssouf ne a gaba sai Rahima biye da shi , suna shiga rahima ta ƙarasa ta rike hannun ta , tace ga ita
   Ki daina kuka haka fatima , ai ga baby nan ba'a tafi da ita ko ina ba ,

Tana ina ??
   Tace tana lalube da hannuwan ta biyu idanun ta har sun rine tsabar kuka ,

A hankali biyamuradi youssouf ya tako zuwa gaban gadon ya ɗora mata baby mama a cinyar ta tare da cewa

   Ungo ta ! karɓe ta fatima daina kuka , ke ai uwa ce a gare ta ,

  Chak ta ɗauke ta ta rungume ta tana ajiyar zuci tare da shafa bayan baby mama tana ɗan bubbugawa ,

Juyawa yayi ya fita yana jin yadda tsananin tausayin ta yake ratsa kowanne saƙo da lungu na zuciyar sa yana samun mazauni , ji yake kome yana neman kunce masa , tausayin ta kuma yana neman yin tasiri akan sa , mafita yake nema ,

Zuwa yayi ya biya kuɗin magungunan da aka mata ,
    Daga nan ya sake ganin likitan da ya bata taimako , ya sake yi masa bayani tare da sake jaddada masa a kula da lafiyar ta,  nan ya rubuta musu sallama zasu iya tafiya daga zarar an sake duba yanayin numfashin ta ,

A bakin ƙofa ɗakin ya tarar da rahima tana zaune ,
   Da sauri ya tura ƙofar ya shiga idanun sa suka sauƙa akan ta , har yanzu tana zaune rungume da jaririyar da take ta bacci abin ta ,

waye anan ?  Tace tana sake rungume ƴar ,

   Fatima ,
ya ƙira sunan ta muryar sa babu amo ,
   Ƙwalla ce ta sake kawo mata a ido , ita dai wannan mutumin ya fi ƙarfin ta ,

  Dan Allah , Dan Allah ka bar min ita , kar ka raba ni da ita ,

  Shiru yayi yana kallon ta , idan har yace zuciyar sa bata yi laushi ba akan tausayin yarinyar ya faɗi ƙarya ,

Fatima za ki bi ni mu tafi ??  Za ki bi ni na tafi tare da ku ke da ɗiyar ki  ?? ?

Inda take jin sautin muryar sa ta saita idanun ta tamkar tana ganin sa ,

Muryar ta ƙasa-ƙasa , ta juya tambayar kan sa ,

Za ka yadda na bi ka , ? Idan na bi ka za ka bar min baby a tare da ni ??

Idan za ki bi ni zan bar ki miki ita har abada a hannoun ki , babu mai raba ku ,!

NA YARDA ZAN BI KA ,!

****

ƙarfe huɗu suka dawo gida , numfashin falmata ya samu daidaito , tana maƙale da ƴar ta tsam , lokaci zuwa lokaci tana ɗan jijjiga ta saboda kukan yunwa da ta fara ,

Suna shigowa prof wanda tunda suka tafi yake ƙiran rahima ya ji halin da suke ciki , ya ji hankalin sa ya kwanta da ya ga falmata ta warware ,

kai tsaye falmata da rahima suka wuce cikin gida domin su haɗawa baby madarar ta ,

Shi kuma Biyamuradi ya shiga wajen prof ,

   Cikin nutsuwa youssouf ya yiwa prof bayanin yadda suka yi da falmata akan amincewa da tayi zata bi shi , ya ɗora da cewa

    Na ɗauki Alƙawarin zan kula da ita tamkar yadda zan kula da ɗiya ta , da yardar Allah ,
  
Gyaran murya prof yayi bayan ya gama jin sa ,
    Ɗana ka so kan ka dayawa , kuma a wannan gaɓar inada ikon yin hani , saboda yarinya amanar Allah ce a hannu na , shi ɗa na kowa ne , abunda baza ka so ya samu ɗan ka ba idan kana da ikon hanawa kar ka bari ya samu ɗan wani ,

ni a matsayina na wanda wannan yarinya take a ƙarƙashin iko na a yanzu , bazan amince maka ka ɗauke ta ka tafi da ita ko ina ba , tana matsayin ƴa mace , kai ko namiji ce bazan yadda ba bare ƴa mace , to a wanne dalili ? Ka tafi da ƴar ka wannan ƴar ka ce ,kana da iko da ita  amma fatima kam baza ta bi ka ko'ina ba !

Shiru youssouf yayi kan sa a ƙasa , shi tausayin falmata yake ji matuƙa , sannan yana da kyakkyawar niyyar sauke ƙudirin sa na tun farko da ya so cikawa akan yakaka , a yanzu da bata nan zai so ya tallafi falmata , ko da babu baby mama zata samu taimakon sa sanadin yakaka ,!

Baba ayi haƙuri a duba da kyau dai ita ɗiyar nan idan an raba su da jaririyar nan matsala ce babba zata auku , lafiyar ta abun dubawa ce ,

  Babu alamun sassauci a muryar prof ya ce idan ka ga na bar ka ,  ka tafi da fatima , to ka ɗauke ta ne ƙarƙashin amincewar shara'a

  amincewar shara'a ?

Youssouf ya maimaita

Ƙwarai ina nufin igiyar AURE ta ƙullu a tsakanim ƙu , ta zama halalin ka , ta maye gurbin ƴar uwar ta a gurin ka , to a lokacin kana da ikon da zaka tafi da ita tare da ƴar ka duk inda kake so cikin duniya ,bazan hana ba,  idan kuwa ba haka ba ka janye batun zuwa da ita ko'ina idan Allah ya kai mu gobe ka zo ka ɗau ƴar ka kamar yadda ka ce , na gama magana !

Ɗago kan sa yayi yana kallon prof tamkar  sassaƙen mutum mutumi ,

AURE ?
    AURE TSAKANIN sa da wa ? Wannan ƴar ficiciyar yarinyar ? Ƙanwar yarinyar da yayiwa ciki ?  Makauniya ƴar gudun hijira ? Marar gata marar galihu marar dangi ??

  Wani irin yanayi yake ciki akan tunowa da yayi da wacece ita , ?

Bugu ƙirjin sa ya shiga yi gumi yana tsattsafo masa har yana ɗiga daga goshin sa duk kuwa da sanyin ac da ya wadaci falon , "

  Youssouf mutum ne da yake jajirtatce mai kafiya akan cikar burin sa bai cika duban yadda gaba zata kasance ba idan yaso aiwatar da wani ƙudiri nasa , a yanzu tafiya da ƴar sa shine a gaban sa , so yake ya tsira da ƴar sa ba tare da ya bar baya da ƙura ba , ba tare da ya ci karo da wani abu da zai iya yi masa shamaƙi ba ,

raba fatima da baby mama wani abu ne da idan yayi

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login