Showing 396001 words to 399000 words out of 411050 words

Chapter 133 - MAFARI COMPLETE BOOK HAUSA NOVELS BY UMMU MUAZ.txt

10 Sep 2025

14278

fata ki sa na faɗi na mutu tun kwanana bai ƙare ba .

Gyara fuska Samy Baby tana ƙoƙarin shanye fushin ta saboda tarkon da take son ɗanawa kar ya lalace ta sassauta muryar tace

"Wallahi tallahi I swear Sofi Yarinyar nan ciki ne da ita ki nutsu ki dawo hankalin ki tun wuri mu yiwa tufka hanci kafi....

Wani razanannan ihu da Sofi tayi da ya amsa gidan gaba ɗaya sai da yasa Yakaka wacce take kitchen ta zabura tana dafe ƙirji a take taji zuciyar ta ta hautsina da daman tunda tafara girkin warin Albasa ke ɗaga mata hankali.

Ba shiri ta bar baro kitchen ta wuce ɗaki tana mayar da numfashi "anya Sofi kan ta ɗaya ?

"Samira da gaske kike ? da gaske kike da gaske ?

Kamar an safure ta ta miƙe tayi hanyar fita daga ɗakin da gudu Samy baby ta bita ta riƙo ta .

Kufcewa tayi tana watsa mata wani mugun kallo kafin cikin muryar da ta buɗu kamar ba ta ta ba tace "ki bar ni naje na kashe ta na farka mata ciki na zo miki da ɗan tayin cikin na ta wallahi sai na kashe ta.

Kallon baki da hankali Samy baby ta jefa mata kafin ta ce .

"Dallah Sofi ki nutsu ya kike abu kamar wacce ba tayi karatu ba ? Kina abu kamar wata jahila kina tunanin yanzu idan kika je kika kashe 'yar mutane ke ma za ki rayu da Hamzan ne ba tare da an miki ɗaurin rai da rai ba ko kuwa ke ma a kashe ki.

"Na yarda a kashe ni idan na kashe ta akan dai mu rayu ni da ita alhalin ta raba ni da farin-ciki na ina ji ina gani bakin-ciki zai kashe ni na mutu na bar mata duniyar su rayu ita da Mijina .

"Na yarda za ta mutu amma ba ta irin wannan hanyar da kike son bi ba ko da kashe ta kike son yi ki bari sai an kauda-bara ta yadda za ki kashe ba tare da an samu mai iya ɗaga ido ya dube ki ba ko kuwa ma kawai a mata abunda zai kashe ta ba tare da an zarge ki ba .

"Ta yaya faɗa min hanyar ?

Sofi ta furta hakan jikin ta har wani mazari yake , a kaikaice Samy baby ta dube ta cikin ran ta kuwa dariya take kwasa "Yau Sofi uwar bin Bokaye har wata nahiyar ita ke tambayar ta yaya za'a yi ? Lalle notikan cikin kan Sofi sun kwance baki ɗaya .

Gyara zama tayi tana jin Allah ne ya kawo mata hanyar warwarewar tata matsalar da kome ya kwaɓe mata bariki tana ƙoƙarin kwashe kayan ta daga kanta ta juya mata baya ta bar ta a cikin rana dan kuwa ko Alhaji Gali a halin yanzu fiye da watanni uku kenan ta daina ganin ƙeyar sa alhalin lokacin biyan kuɗin gidan haya yayi haka tana ji tana gani bayan ƙara mata sati biyu da masu gidan suka yi suka zo a ƙarshe suka kore ta sai gidan ɗaya daga cikin abokan shaiɗanan ta ta koma da ko kaɗan ba jin daɗin zaman gidan take ba saboda ba shi da wani hali sosai irin mazan nan ne da Zina ta aure su wanda ko basu da sisi sai sun yi ta.

Fahimtar hakan da tayi yasa ta fara ƙulla wacce za ta fissheta idan zaman Abujan ya gagara ne tana iya komawa ko Damaturi ne ta karkaɗe kwalin ta ta shiga neman aikin da za tayi ta riƙe kan ta dan kuwa ko a mafarki ta san bata doshi Maiduguri gidan Ubanta ba bata ma da matsugunni a gidan sannan ita a karan kanta bata jin za ta iya rayuwa ƙarƙashin iyayen ta.

Sai dai me ? Kuɗaɗen da suke account  ɗin ta ba zasu ishe ta yin irin rayuwar jin daɗin da take tsarawa kan ta ba ko da ta koma Damaturu domin so take ta shiga gari sosai ta wataya a ƙarshe ta samu wani ɗan Matashin kyakkyawan Saurayi haka ta chaka masa su yi aure .

Dan haka ido rufe take neman kuɗi tunda kuwa yanzu dama ta samu da zata iya samun su daga Sofi to me za ta jira ?

Muryar Sofi ta katse mata tunani ta da take cewa " Ni kin hana ni naje na aiwatar da manufata ke kuma kin yi zaune shiru baki kawo wata hanyar ba ki faɗa min ya zan yi ?.

"Sofi ki buɗe bakin Aljihu kiyi ɓarin kuɗin na san dai kin Fahimceni ni kuma na miki alƙawarin ko nan da birnin Sin ne zan je miki wurin Boka ba sai kin ma tafi da kan ki ba bare har a iya zargin ki .

Da wata irin Murya Sofi ta ce " ki koma min karnataka Samira gurin Bokan da ya min aiki akan zuciyar Doctor zan baki adireshin sa da kome sannan zan bayar da kuɗin da zai ishe ki har kije ki dawo da kuma kuɗin aikin sa , bana so na motsa ma daga tsakanin su domin ko kallo bana so ya sake shiga tsakanin su ....

Samy Baby wacce tafi zaƙuwa da zancen kuɗin jin tarkon ta yayi kamuwa tace "amma fa kin san kuɗaɗen dayawa Friend..

"Ko miliyan ishirin ne zan sayar da gwalagwalai na na baki kuɗin bana so a ɗau lokaci nasan kin san manyan mutane a ƙasan nan dan haka samun visa ba zai miki wahala ba idan son samu ne cikin satin nan ki tafi kai ni idan zai yiwu ma cikin kwanaki biyu masu zuwa saboda bana so bana kuma fatan yarinyar nan da ita da abunda ke cikin ta su sake yin sati ɗaya a duniya .

Nisawa tayi tana gatsa gefen bakin ta da haƙori tace " Sannan so nake na kashe ta da hannun na Samira da hannu na nake son kashe ta shine kaɗai abunda zan iya mata da zai sa zuciyata ta wanku daga baƙin-cikin da ta samu a ta sanadin ta dan haka daga kin isa can an yi aikin kawai ki ƙirani ki sanar min ina mai tabbatar miki da sai dai ki dawo ki tarar ana zaman makokin mutuwar ta .

Shiru Samy Baby tayi tana kallon Sofi cikin ran ta tana girmama rashin Imani irin na Sofi yau ta zama rana ta farko da ta fara jin shakkun samuwar cikakken hankali ga Sofi to kodai tana da rauhanai ne ????? Ko kuwa Mai rabon shan duka ne da baya jin Bari




Assalam Alaikum masu karatu.

Albishirin ku ?

Na san kun ce goro goriya goro .

Yau Maman 'yan biyu tagwayen shafuka ta muku.

Ina nufin kar ku motsa shafin nan tare yake da ɗan uwan sa da yakasance kuma murfi na baki ɗayan littafin Mafari insha Allah .

A sha karatu lafiya .
[4/15, 10:16 PM] Zuraiyah Zuzu 🌟: MAFARI
......... HARGITSIN RAYUWA


UMM' MUAZ


54







MAI RABON SHAN DUKA










Ganin irin mummunan kallon da Doctor Hamza yake yi mata bai karya guiwar Sofi ba da zai sa har ta gaza yin wani yunkuri kare kanta ba .

Dan kuwa zuruf ta miƙe bayan ɗan taƙaitatatcen tunanin da ya gifta mata da bata yi ƙasa a guiwa ba ta fara ƙoƙarin tattaro nata makaman yaƙin "ai ba zata bari Yakaka ta ci ta da yaƙi ba haka nan take .ta aiyana hakan a zuciyar ta

"Doctor ka ga'.....

Wata irin tsawa Doctor Hamza yayi da ba ita Sofi kaɗai ba ,hatta Sam sai da yayi zillo yana ɗan kuka ya koma bayan kujera ya laɓe.

"Kar ki ce min kome Sofi , bana buƙatar jin ƙaryar ki ta banza abunda nake so kawai shine ...

Ɗan jim yayi yana kallon ta yadda ta wani irin saƙare cikin rashin madafa matsanancin tashin hankali gami da wani nisassashen yanayi shimfiɗe akan fuskar ta inda take bata motsa ba , ba domin tazarar dake tsakanin su na da ɗan yawa ba da babu abunda zai hana ya iya jin sautin bugun zuciyar ta..

"Ki tafi gida Sofi .

Ya ce da wata irin kakkaurar murya yana ɗauke ganin sa daga kan ta ya zagayo da Yakaka daga bayan sa yana sake bin jikin ta da kallo kamar dai yana yiwa Sofi nuni da mummunan laifin da ta aikat ,yana kallon fuskar Yakaka tamkar ita yake yiwa maganar ya ɗora da cewa.

"Ki je gida akwai buƙatar ki sake samun ƙarin tarbiyya irin ta masu hankali da cikakkiyar koyarwar Islama ko ɗaya ba zan iya sake jimirin ɗaukar salon haukar da kike yi ba .

"Ki tafi gidan ku Sofi.

Ya furta hakan da buɗaɗɗiyar muryar da yasa kuka tahowa Yakaka da sauri ta shige cikin jikin sa tana zagaye shi da hannunwan ta , matsanancin tsoro na ɗarsuwa a ran ta ganin ɓacin ran sa Mai tsanani irin wanda ta daɗe bata gani ba.

"Ga Sofi kenan  matar son sa da ita ce ta kora ta layin.

ina ga ita kuma ? Da ta yaga kayan ta da kan ta ? Watakila idan ya gama da Sofi  ya dawo kan ta "shikenan Hajja ta jawo mata .

Hannun sa da ya sauke a bayan ta yana ɗan buubbuga ta alamun rarrashi yasa ta ji nutsuwa ta fara dawo.mata da sauri ta ɗago kan ta tana kallon fuskar sa da shi ma ita yake kallo.

Zata yi magana ya hana ta ta hanyar jaan hannun ta zuwa hanyar ɗakin sa ba tare da yace  ƙala ba

A ɗan tsorace ta dubi sashin Sofi har lokacin tana nan a tsaye inda take tamkar an dasa ta kallo ɗaya ta yiwa fuskar ta tayi saurin janye idanun ta tana jin yadda zuciyar ta ta doka da ƙarfi babu shakka ta hango wani lamari mai kaifi daga cikin idanun Sofi da suka tara ruwan hawayen da basu kai ga zuba ba '

"Ki tafi tare da dabban da kika kawo min gida bana so na fito na ga ɗayan ku .

Doctor Hamza ya furta hakan kafin su kai ga shiga ɗaki.

Wani irin tsuma jikin Sofi yake so take Allah ya kawo wani ya wanka mata marin da zai farkar da ita daga mummunan mafarkin da take yi "Doctor Hamza ne da kan sa yau yace ta fita ta bar gidan sa ? Razanar da ta tsinka mata gudun jikin jikin bai wuce dalilin korar ta ta ba " akan wannan kuchakar 'yar gudun hijirar  'Yar talakawa 'yar ƙauyen ne Hamzan ta ya kore ta?

Kai ina ƙarya ne lokaci yayi da zata farka daga gyangyaɗin da take yi da har yasa tayi saken da wankin hula ke shirin kai ta tsakar dare akan Yakaka.

Ihu take son kurmawa amma tana ganin a halin da take ciki babu lokacin ihu , da gudu ta taka ta hau sama ɗakin ta mukullin motar ta kawai ta ɗauka sai fa wani siririn mayafi da ta rufa akai ta fita daga gidan .

Wani irin gudu take yi a kan titi da ya zarce ka'ida tana yi tana dukan kan ta da hannun ta ɗaya .

Lokacin da ta shiga gidan su kai tsaye falon Momy kori ta zarce wacce bata san da shigowar ta ba sai da ta ji ana mata rotse a falo ta yunƙura daga kwanciyar hutun da take yi akan gado ta fito tana cewa "meye haka ? Meke...'

Sauran kalmomin sun maƙale ganin 'yar ta Sofiya ce take mata wannan aika aikar duk ta farfasa mata show-glass

Da gudu ta ƙarasa tana riƙo ta Amma sofi sai sake fisgewa take da alamun fitar hayyaci a tare da ita .

Hankali tashe take kiran sunan ta

"Sofi , Safiya ke Safiya meye hakan ? Kin yi hauka ne dan ubanki.?  Nace hauka kike ?

Ganin taƙi saurararta yasa Momy Kori ta cire hannu ta wanke ta da marin da yasa Sofi wani irin juyowa a fusace ta tunkuɗa Momy kori tayi zaman dirshan a kujerar gefen ta .

"Momy ki rabu da ni wallahi sai na tarwatsa rayuwar Yarinyar nan yadda nake tarwatsa wannan show-glass din naki.

"Wallahi sai na kashe ta , kafin ta kashe min aure ta raba ni da Hamza a ƙarshe tasa baƙin-ciki ya kashe ni .

Wani irin kallo Momy kori take bin ta da shi da yake nuni da zunzurutun takaicin da take ciki da kyar ta buɗi baki ta ce .

"Yanzun nan ke dan Ubanki akan kishiya kike wannan haukar ? Akan kishiya kika min wannan ɗanyen aiki ? Kika min wannan ɓarnar Sofi ? To billahil azim sai kin biya kuɗin abubuwan duk da kika rotsa dan buhun ubanki.

Miƙewa tayi tana jin gara ta bar gurin kafin zuciya ta ciwo ta ta jawo ta ta fara kirɓa .

Tana barin wajen Sofi da take tsaye ta silale jaɓar ta zauna a ƙasa kafin ta saki wani irin ihun da farkon sa kururuwa kafin ya miƙa da wani irin Kukan da yake siƙewa ta maƙollotan ta .





...
[4/15, 10:16 PM] Zuraiyah Zuzu 🌟: MAFARI

           ( HARGITSIN RAYUWA)


UMM'MUAZ



KARSHE



(A)







A daren ranar Doctor Hamza bai dawo daga aiki ya tarar da Sofi a gida ba saboda tunda rana suka fice ita da Samy ko Yakaka bata san fitar su ba .

Hakan ba ƙaramin ɓatawa Doctor Hamza rai ya yi ba saboda ai tsagoron raini ne matar auren ka ta fita unguwa ta kai har dare ba tare da ta nemi iznin ka ba .

Sai dai halin rashin lafiyan da ya zo ya tarar da Yakaka a ciki ya ɗauke masa hankali daga kula haukar Sofi .

Nan take ya shiga bata duk wata kulawar da ta dace domin samun tabbacin abinda yake zato .

Maƙurar farin-cikin da zai iya cewa bai taɓa jin yanayin sa ba ya tabbata a zuciya da kewayen jinin jikin sa baki ɗaya lokacin da gwajin fitsarin da ya yiwa Yakaka ya bayyana masa da tabbatuwar zaton sa

Yakaka tana ɗauke da gudan jinin sa a Mahaifar ta nan da wasu watanni zai zama uba bayan shekaru bakwai da ya kwashe da yin auren sa na farko wanda hakan ya sadar da shi cikar shekarun sa arba'in cif ba tare da ya samu ɗan kan sa ba .

Sai fa yanzu da Allah yayi tsiron halittar gudan jinin sa a tare da Yakaka shi kuwa da wacce irin kalma zai miƙawa Ubangiji godiyar sa ?

Ganin sa ya mayar kan Yakaka wacce take bacci hankalin ta kwance da ba domin larurar saurin bacci na mata masu ƙaramin ciki ba a ɗan zaman su da yanzu-yanzu tayi fitsari ta ba shi yayi awu bai ci ace kafin ya gama gwajin har tayi bacci ba .

Fuskar ta ya tsirawa idanu yana jin wani ƙaunar ta mai ƙarfi tana sake fisgar sa har yana jin kamar babu wani sarari da yayi saura a zuciyar sa da ƙaunar ta bata riga ta cika ba .

A hankali ya ɗaga hannu yana shafar kumatun ta da suka sake yin suɓulɓul suna ƙyalli na musamman .

Zazzaɓin da ya dawo ya tarar da shi ya rufe ta sosai a yanzu ya sauƙa saboda ya bata maganin sauƙe zafin jiki ta sha .

"Wafaa .

Ya ƙira sunan ta a hankali yana ɗan hura mata iska a fuskar ta '

Buɗe idanun ta da suka yi nawi tayi tana kallon sa a raunace .

"Wafaa yaya kike jin jikin yanzu ? Za ki iya tashi muyi sallah ?

"Habibi nayi sallar isha ina jin bacci sosai ni.

"Na san kin yi wannan Sallar miƙa godiyar mu ga Ubangiji za muyi da yayi mana kyautar sa mafi girma .

Hannun sa ya kai ya ɗora akan cikin ta kafin cikin taushin murya yana kallon idanun ta ya cigaba da cewa

"Allah ya arzuta mu da samun rabo , Wafaa we are going to have a baby, zan zama Baba Wafaa za ki Haifa min Baby .

"Da gaske ?

tace da shi tana ƙoƙarin miƙewa zaune ya taimaka mata ta zauna.'

Yana murmushi ya amsa mata "Da gaske Wafaa na baki Baby i am gonna be a Daddy.

Wani irin yanayi ta ji mai sanyi tundaga ƙasan ran ta da ya chakuɗu da kunyar ta ta halitta dan haka ta tafi da sauri ta shige jikin sa tana ɓoye fuskar ta a ƙirjin sa .

Dariyar da bata da sauti yayi yana riƙe da ita ya miƙe kafin ya sake cewa " Alhamdulillah for blessing us in the most special way as a Mum and Dad.

Ya ɗago ta a hankali ya sumbanci goshin ta sannan ya sake cewa "muyi Sallah Wafaa domin mu nunawa Ubangiji godiyar mu.

Gyaɗa kai tayi ba tare da ta amsa ba .

Tsananin farin-cikin da yake ciki a daren ya mantar da shi takaicin Sofi dan ko da ta dawo tana wani kame-kamen ta lokacin da ta shigo falon ta tarar da shi yana aikin sa a laptop Yakaka kuma tana bacci a jikin sa .

Wajen ƙarfe goma saura na dare za ta fara masa ƙwarƙwasa ya ɗora hannun sa akan laɓɓan sa yace "shittt please Sofi kar kiyi hayaniya ki tayar da ita a bacci tana buƙatar hutu Sosai bana son abinda zai dame ta .

Wani sakototo Sofi tayi baki sake tana kallon sa .

"yau ga sabon salo kuma , kullum abun daɗa lalacewa yake , ta aiyana hakan daga cikin ran ta .

kafin ta mayar da ganin ta kan Yakaka wacce ta juya baya tana kwance akan kujera tayi matashin kai da cinyar sa fuskar ta na fuskantar jikin sa'

Hayaƙi-hayaƙi ta ji yana safko mata yana sanya ta gani dusu-dusu .

"Bata da lafiya ne ?

Ta furta hakan a shaƙe tana tattaro duk wata sauran juriya da ta rage mata .

Murmushi Doctor Hamza yayi da har take Iya hango ƙyallin haƙoran sa da muryar sa mai cike da nutsuwar da bata ɓoye halin farin-cikin da yake ciki ba yace "Sofi we are pregnant insha Allah in nine months we will welcome a new bundle of joy into our family.

Kamar wacce aka dokawa guduma a ka haka Sofi ta ji, kunnuwan ta suka rabu da ji na ɗan wani lokaci duk kuwa da cewa a ɗazu Samira ta faɗa mata batun cikin Yakaka amma bata ji dukan zancen irin yanzu ba dan kuwa a ɗazu tana da ƙarfin jikin iya yin zabure-zabure a yanzu kuwa da  zancen ya tabbata cewa dai Doctor Hamzan tane ya yiwa Yakaka ciki ji tayi

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login