Showing 27001 words to 30000 words out of 276165 words

Chapter 10 - GIDAN DAN LITI BOOK COMPLETE BY HAMIDA SANUSI AHMAD.txt

liti ya gan ki a haka ai sai ya tsine miki ya haɗa da ni da zuri'a ta dika,"

Ganin Billy ta saki ranta har tana murmushi da jan ta da wasa ne ya sanya Mommy itama sakin ranta kaɗan, dan kuwa a da duk ta takura ta damu, ga jimamin sanin Billy ba aikatau take yi ba karuwanci take yi ga kuma Billyn na fushi da ita saboda ta yi maganar lokacin sallah.

A hanya ne Mommy ke jinjina lamari irin na mutanen duniya, ashe dai komai iskancin ka kana samun wanda ya fi ka?

A da da tana gidan su sallah sai ta ga dama take yi, ko kuma ta haɗe azahar, la'asar, magariba, watarana se zata kwanta ma ta haɗa duk har da isha'i,sai gashi anan yin maganar lokacin sallah ma ya zama tashin hankalin da ake d'aga jijiyar wuya akai,lallai rayuwar duniyar nan ta na da ban ta'ajibi.

Sun isa gida a matuqar gajiye, dan haka suna isa Billy ta fito ta wurga wa Sallau makullin motar tace ya fitar da kayan ciki ya kai d'akin Mommy, da sauri ya cafe makullin motar ya fara bin umarnin ta, Mommy kuwa na biye da ita kamar raqumi da akala.

Suna shiga suka ga Hajiya K'waisa da wani kyakkyawan matashi suna manne da juna kamar mata da miji, Hajiya K'waisa sai shagwab'a take yi wa matashin shi kuma yana lallashin ta tare da sumbatar ta a duk inda ya samu a jikin ta.

A kasalance Hajiya K'waisa ta d'aga kan ta daga jikin kyakkyawan matashin ta na duban Billy wadda ta b'oye Mommy a bayan ta ta na murmushi,cikin wani irin yanayi Hajiya K'waisa ta miqe a ɗan firgice bayan Billy ta matsa Mommy ta bayyana.

"Ke Billy wannan halittar daga ina haka? Ke..ke...tsaya, kar ki ce min...laaa kar ki ce min wannan wagirarriyar yarinyar ce ta koma haka? Allah mai iko ! Ahayyeeee washhh Allah maraba gasasshe wai kura ta ga baƙin jaki"

Dariya Billy kawai take yi ta jin daɗi dan kuwa ta san idan Hajiya ta yaba dole a yi mata ruwan nerori.

"Billy ina motar can da kike maita na hana ki? To ki ɗauka na baki kyauta"

Ihun murna Billy ta sanya ta tafi da gudu zata rungumi Hajiya Saurayin Hajiya ya zabga mata harara, harar da ta dakatar da Mommy daga dariyar da take yi ta farin ciki, dan kuwa a ganin ta ko za a kashe ta ba zata iya yin wannan hararar ba a matsayin ta na mace.

Cikin wata muryar da Mommy ta zata mace ce ke magana matashin yace wa Billy,

"Ke dakata anan, na yi maki iyaka da wannan naman, domin kuwa naman giwa ya fi ƙarfin kaza ta ja shi,tsaya can kiyi murnar ki bana son gwalangwason banza"

Kafin Billy ta yanko tata maganar Hajiya K'waisa ta shiga tsakanin wannan 'yar qaramar taqaddamar dake son ta kaure tsakanin Billy da saurayin Hajiya K'waisa,

"To ya isa haka, table ɗin mu is ready mu kaɗai abinci ke jira tun ɗazu mu je mu ci kar ya yi sanyi,Billy kin cancanci wannan kyautar shi yasa na yi maki ita, na sani kina so ki wanke min bakin cikin da Any ta sanya min a raina ne kafin ta bar gidan nan, na tabbatar ke da kan ki a yanzu idan kin so zaki iya kafa taki harkar amma halacci ya sanya ki ke ci gaba da zama a qarqashi na,dan haka ba abinda ba zan yi maki ba dan ki ji daɗi kema sai abinda bani da shi"

"Ina godiya Hajiya ta,dole ne na ci gaba da yi maki biyayya domin kece ki ka tsamo ni daga mummunar rayuwar zama a gidan qananan karuwai ki ka ɗaukaka daraja ta na dawo ina zama a irin wannan mashahurin gidan, kuma ki ke yi min duk abinda nake so dan haka dole ne nima na faranta maki....ai baki sani ba, mun haɗu da yaran Any a saloon har da yada min magana,"

"Rabu da su, zan basu mamaki a taron new year na Abuja ina nan ina wani babban tanadi,Mommy nake so ta yi mana wannan babban kamun saboda ita sabuwar fuska ce,da ita zamu yi amfani mu kece raini"

Yaqe Billy tayi dan kuwa ta jima tana targeting wannan babban taron da za a yi na manyan 'yan duniya irin su,kuma a wannan taron ne ake saka ran zuwan babban matashin ɗan siyasan nan mai suna Alhaji Yasir Mai Nasara,matashi ne mai ji da kyau da nera, a taron ne zai zaɓi yarinyar da zai dinga hutawa da ita a wannan shekarar, a tunanin ta Hajiya K'waisa za ta aika ta sai kuma ta zaɓi Mommy, wani irin yawu ta had'iya mai d'aci ta wuce gaba tana yaqe,kujera ta ja wa Mommy Mommyn ta zauna a d'arare, dan kuwa sauraron su kawai take yi amma tabbas tana buqatar fashin baqi dalla-dalla akan lamarin nan da suke magana akai.

Murmushi Hajiya K'waisa ta yi tace wa Mommy,

"Kar ki damu da sannu zaki gane inda komai ya dosa,watarana ke zaki gayyato wasu suma su dangwali arziqi kamar yanda Billy ta yi miki"

Yaqe Billy ta sake yi dan ita wannan yabon be wadatar da ita ba sam.

Abinci suka fara ci Mommy na ta kallon yanda kowa ke sarrafa wuqa da cokali mai yatsu ita dai ko da cokali mara yatsun ma ba zata iya zagewa ta ci yanda zata qoshi ba, dan haka sai ta faki idon su ta sanya hannu ta damqi nama ta jefa a baki ta hau muzurai,Hajiya K'waisa na kallon ta amma ta kauda kai ta yi kamar bata gani ba, da ido ta kalli Billy ta yi mata alama da,

'A koya mata cin abinci a table'

Itan ma da ido ta amsa mata da,

'An gama'

Wayar Mommy ce ta hau ringing wadda gaba ɗaya ta ma manta tana tare da wayar a cikin qaramar purse ɗin ta da suka fita da ita, qarar ce ta razana Hajiya K'waisa har sai da ta zubar da abincin da zata kai bakin ta a jikin ta ,cikin ɓacin rai da haɗe haqoranta waje ɗaya ta kalli Mommy, da sauri Mommy ta miqe tana bada hakuri ta nufi hanyar sama dan zuwa amsa wayar ta...............


GIDAN ƊAN LITI










PAGE 10:










A natse Billy ta dafa kafaɗar Mommy ta ce,

"Mommy ki natsu ki kalli dai-dai inda zaki ajiye ƙafar ki kawai kar ki kalli can ƙasa,to wai ke yanzu a haka zaki waye ki na tsoron bene fisabillahi? Meye a cikin hawa bene sai kace wata wadda zata taka girgije?"

Cikin rawar murya da jiki Mommy ta qanqame hannayen Billy gabaki d'ayan su ta ce,

"Ba zaki gane ba ne billy ji nake yi kamar ana waina ni,riqe ni kar ki sake ni, ni da za ku taimake ni ko a d'akin mai gadin gidan nan ku ajiye ni bana son wannan d'akin da sai na yi cinikin rayuwa ta sannan na hau shi"

A haka suna surutu har suka sauka Mommy bata san ma an sauka ba, ganin ta sauka lafiya ne ya sanya ta sakin wata ajiyar zuciya mai qarfin gaske sannan ta fashe da dariyar farin ciki ta ce,

"Ashe ma ba wani wahala,"

"To dama in ba dan ke ba ma meye a hawa bene dan Allah? Yanzu dole ne mu koma ki sake gwadawa,saboda bana so ki hasala Hajiya ta gaji da shirmen ki ta yi maki korar kare, gidan nan ya ajiye 'yammata iri na da irin ki sun fi goma wasu sun samu nasara a irin rayuwar da muke yi har sun jawo wasu a jiki suma sun zama wasu, wasu kuma wauta da rashin rabo da qauyanci irin naki yasa ba aje ko ina da su ba aka rabu rayuwar su ta yi munin da ta fi ta kare, dan haka ki maida hankalinki ki zama k'wararriya akan abinda ki ke yi ta haka ne zaki yi ta samun ci gaba har ki jawo wasu kema kamar yanda na jawo ki ni kuma Hajiyata ta jawo ni cikin wannan harkar"

(Ci gaban mai haqon rijiya kenan)

Duk abinda Billy ke faɗa yana shigewa cikin kan mommy kuma ta gamsu da bayanan ta dan haka cikin rawar jiki ta kama qarfen benen ta sake gwada hawa, idanun ta na zubar da hawayen tsoro bakin ta ɗauke da kiraye kirayen sunayen duk wanda take ganin zai zo ya kawo mata agaji a wannan yanayi da take ciki,dan kuwa hatta da sunan Ameerah sai da ta kirawo a wannan yanayin, takaicin ta kuwa kamar ya kashe Billy, gajiya tayi da tsayuwa ta samu kujera ta zauna ta fakaici idanun Mommy ta kunna camera ta na yi mata video,ta na gamawa kuwa ta yi posting a account ɗin ta na TikTok, dama ta rasa content ɗin da zata yi creating ta yi posting a ranar,nan da nan kuwa mutane suka hau gani ana yin comments kala-kala da likes, ta na nan zaune sai sheqa dariya take yi har Mommy ta yi sakkowa ta qarshe, a wannan lokacin kuwa ta na jin ta wasai ba wata fargaba balle tashin hankali dan kuwa ta gano hawan benen ba wani kayan gabas bane ba, tana sakkowa tace da Billy,

"Ashe ma ba wani wahala hawa da saukar,da fari na tsorata ne kawai,yanzu kuwa ina jin ko wanda yafi wannan laulayawa ma ina iya hawan shi"

"Good muje to?"

Makullin mota Billy ta zara guda ɗaya a inda suke ajiye makullayen motocin gidan suka buɗe qofa suka fita harabar gidan cike da yanga,wajen motar da za su hau suka nufa Mommy na biye tana kallon ikon Allah,bata gama tsinkewa da lamarin Billy ba sai da taga ta shiga motar ta kunna ta da kan ta sannan ta buɗe wa Mommy gefen direba ta yi mata izinin shiga, a rikice Mommy ta kalli Billy da ke toshe idanun ta da wani baqin gilashi ga kid'a na tashi cikin hauragiyar yaren mutanen kudu, da qarfi Mommy ta d'aga murya tace,

"Billy yaushe ki ka iya mota? Billy lamarin ki na nema ya fi qarfi na fa?"

Wani shu'umin murmushi Billy ta saki sannan ta ce,

"Dan Allah ki shigo kina b'ata mana lokaci, akwai abubuwan da baki sani ba da yawa game da ni,amma a hankali lokaci zai bayyana maki su,fata na ki rage wannan qauyancin da kike yi dan zai jawo maki raini a gaba a irin wannan duniyar tamu,ina fatan kin gane?"

Zama mommy tayi tana gyad'a kai zuciyar ta fal tsoro da fargabar anya ba zata juya ba daga wannan makauniyar tafiyar da ta faro a cikin rayuwar ta?

Mai gadi ne ya wangale musu gate Billy ta take mota suka bar harabar gidan,tun a hanya Mommy ta kula da yanda manyan motoci ke shawagi a cikin wannan hamshaqiyar unguwar, banda kallon su da gine-ginen dake wajen ba abinda Mommy ke yi,tafiyar da suka yi bata kai ta rabin awa ba suka isa wani makeken waje wanda Mommy ta kasa yarda wai iyakar gyaran kai ake yi a wajen saboda girman shi da tsaruwar shi, tunda suka fito ta ga manyan mata da 'yan mata kyawawa da kuma wanda kwalliya ta rufawa asiri sai nera da ta qara gyara sufar su suna shige da fice a wajen.

Suma shiga suka yi cike da jin kan su su wasu ne, Billy sai qoqarin nuna wa Mommy yanda zata yi tafiya take yi a fakaice,a haka suka shiga Billy ta gabatar da Mommy a matsayin wadda take so a yi wa gyaran ciki da waje,(gyaran kai ,waxing, gyaran qafa da hannu da kwalliya) sai tace musu zata je ta dawo kafin magariba su wuce.

Mommy na jin Billy zata tafi ta barta a wannan wajen sai ta ji wani irin tashin hankali da damuwa ya mamaye ta, da sauri ta damqi hannun Billy tana muzurai, murmushin yaqe Billy tayi ta kama Mommy suka koma gefe tace mata,

"Ki zauna anan yanzu zan je na dawo akwai abinda zan gabatar mai mahimmanci kar ki ji komai na ce su yi maki duk abinda ya dace, kin ga na bada kati na su cire kuɗin su dan haka na biya kud'in yi maki komai,zaki gode min da zarar an kammala, dan Allah ki dena abinda kike yi ki saki jikin ki nan wajen Hajiyata na da maqiya sosai a wajen,da zarar aka ga abinda kike yi sai ki zubar mata da aji kuma ni zata yi wa faɗa, ki kama kan ki dan Allah"

Yaqe Mommy ta yi sannan ta saki hannun Billy ta bi matar da ke tsaye tana jiran su gama sallama, Mommy na shigewa wajen da ake gyaran jiki Billy ta fita daga building ɗin ta wuce wajen Man ɗin ta dan kuwa sun yi kewar junan su matuqa bata fatan su kwana basu gana ba,ta tabbata kafin nan kafin a gama gyara Mommy sun gama abinda za su yi sai ta dawo su wuce gida, bata so ta b'ata wa Hajiyan ta rai tunda har ta sanar da su za su yi dinner tare, da ta jira su gwanda su su jira ta.

Tinda aka shigar da Mommy wajen gyaran jiki basu fito ba sai da Billy ta dawo ta nemi inda suke aka ce suna wajen yin k'walliya, direct d'akin da ake yin kwalliya Billy ta shiga, sanda idanun ta suka sauka akan Mommy da ta sauya kamanni saboda gyara da kwalliya da ta sha sai da ta rikice, nan take ta ji wani irin kishi da hassada ya d'arsu a ran ta, cikin jimanta lamarin ta ayyana,

'Anya ban d'akko ruwan dafa kaina ba kuwa? Kar fa naje garin taimako ta ture gwamnati na ta kafa tata sai dai na jira ta kwashi babban kaso a bani qarami'

"Ranki ya dad'e gata nan an kammala duk abinda ki ka ce a yi mata, amma fa wannan qanwar taki akwai ta da tsoro da raki,"

Yaqe Billy tayi tace,

"Haka take, ina godiya gaskiya kun yi aikin da ya dace ku yi harma da qari,dan haka dole ne a qara maku wani abu"

Ta faɗa tana mai zuge jakar ta ta dakko kuɗi kimanin dubu goma ta baiwa mai kwalliyar, godiya mai kwalliyar ta yi mata sannan Billy ta yi wa Mommy umarnin su wuce su tafi shopping, gashin dokin da aka sanya wa mommyn ta kawar da wanda ya sauka a saman fuskar ta ta miqe tsaye ta na qara kallon kanta a madubi da kyau, tabbas ita ɗin mai kyan diri da fata ce ta sani, amma bata taɓa zaton tana da kyau a fuskar ta irin haka ba sai yanzu,sai a yau ta ke ganin ashe ma bakin nata da ake yi wa iya shege wata kadara ce ta daban da Allah ya yi mata,dan kuwa ya ɗauki kwalliyar da aka yi masa tsafff ya qawatu ya qawata fuskar ta.

"Hahaiiiii ! son a sani ne fa ba wani abu ba, matar da har yau a qarqashin wata take bata da gidan kan ta ai barikin nata bai kai ko ina ba"

A fusace Billy ta juya ta kalli 'Yan matan dake danna waya suna cin chewing gum suna dariya qasa qasa tare da kallon Billyn suna ci gaba da yi da ita a gaban idon ta, har zata tanka su ta tuna da gargad'in Hajiya K'waisa na ta kiyaye yin qananan faɗan da za a kai ta wajen police, dan kuwa hakan ba k'aramin taɓa mata qima yake yi ba a gan ta kullum tana neman alfarma a wajen 'Yan sanda manyan su da qananan su.

K'wafa ta yi ta ja hannun Mommy suka bar wajen, ko da suka fita sai Mommy ta ji ana ta kiraye-kirayen sallar magariba, kallon Billy da ranta yake a matuqar b'ace ta yi tace,

"Yanzu idan zan yi sallah wannan faratan za su ɗauki ruwa kuwa? Sannan shi wannan gashin na ga kamar hula ce aka sawa gam ya manne da kai na ta ina ruwa zai shiga na yi shafar kai?"

(Tambaya zuwa ga masu sanyawa faratan su fenti da kuma sanya attachment daga mommyn gaye)

Cikin fushin dake cin ranta ta juya ta kalli Mommy tace,

"Idan Sallah kika biyo ni yi nan garin sai ki yi bayani sai na kai ki gidan manyan malaman garin nan a buɗe maki masallacin mata kina jan su sallah,kin ga Mommy bari na buɗe miki wannan harkar tamu ki ji ya take idan kin ga zaki iya ki bini tun yanzu ki san ina ki ka shigar da kan ki da kan ki, idan kuma kin ga baza ki iya ba gwanda tin yanzu mu rabu kowa ya san inda dare ya yi masa.

Maganar gaskiya Mommy ba wani aikatau da nake yi da ya wuce aiki da jiki na da Allah ya bani ina biya wa mace ko namiji buƙatar su, su kuma su zube min kud'ad'e maqudai na biya tawa buqatun na yau da gobe,ina kuma yin hakan ne ta hanyoyi da dama,kamar  su wayar nan ta zamani da ki ka gani a hannayen mu ina nufin ta social media kamar su WhatsApp, TikTok, Instagram, Telegram ke har ta Twitter yi muke yi,sannan ina iya bin mutum duk qasar da yake so dan na taya shi shaqatawa ko kuma a nan gida Nigeria,ni ɗin nan da ki ka ganni ba qaramar yarinya bace, tsoron zagin da za a yi wa iyaye na ne yake sanyawa nake rage wasu abubuwan,wannan shine dalilin da yasa kika ga sai na yi shekaru ban je gida ba,saboda iyayen da suka haife ni ma basu san asalin me nake aikatawa ba,dan haka idan kin ga zaki iya ki yi in baza ki iya ba ga hanya nan kafin komai ya yi nisa ki koma qauyen Ba mugu ki ci gaba da bawa Yah Shamsu jikin ki yana lalubewa babu ko sisi"

Tana gama fad'ar waɗannan maganganun da suka sanya Mommy yin suman zaune ta ja motar da mugun gudu suka isa wani shopping mall dake kusa da saloon ɗin da suka je ta samu wajen parking ta yi ta fita ta tsaya tana jiran Mommy da har a wannan lokacin bata gama fita daga cikin rud'anin da ta afka ba.

Sigari ta fitar ta kunna ta hau busawa abinta hankalin ta kwance, masu wucewa na kallon ta, abinda ya sake d'aure wa Mommy kai kenan, dama Billy na shaye-shaye,sannan a bayanan ta ta ji kamar maza da mata dika take

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login