Showing 258001 words to 261000 words out of 276165 words

Chapter 87 - GIDAN DAN LITI BOOK COMPLETE BY HAMIDA SANUSI AHMAD.txt

ma gida yanzu haka, bamu jima da dawowa daga asibiti bama."

"To ki ɗan tsaya na kawo maki abun gayyatar biki ki kai musu,muna gayyatar ku ai yanzu mun zama ɗaya."

Wani irin yawu Mommy ta haɗiya,tare da kallon yanda Innah Laminde ke magana cikin kwanciyar hankali,ba dan kar a ga rashin kunyar ta ba,to tabbas da ta gaggawa Innah Laminde baƙar magana,taya zata bata abun gayyatar auren namijin da take mutuwar so a ran ta wai ta kai gidan su? Wannan ai cin fuska ne,daurewa Mommy ta yi ta tsaya tana jiran Innah Laminde a tsakar gida,Amir ne ya dawo ya riƙe mata mayafin ta,babu ɓata lokaci ta duƙa ta ɗauke shi,ƙamshin turaren Abdussaboor dik ya cika mata hanci, lumshe idanun ta tayi ta sake rungume yaron tana sumbatar shi. Abdul ne ya fito daga ɗakin shi ya yi hanyar waje riƙe da makullin mota.

A haka Innah Laminde ta sami Mommy ta miƙa mata leda cike da goro da alewa da chewing gum har da biscuits tace ta kai gida, godiya ta yi mata tare da sanya alkhairi a auren ta miƙa mata Amir da ya fara rikicin zai bita ta fita da sauri,tana isa soron gidan ta fashe da wani irin kuka mai cin rai,dik yanda taso ta danne kukan kasawa ta yi,kanta ta fara tambaya a fili tana faɗin,

"Shin wai ni wace wautar ce ma ta sanya ni zuwa ganin Amir a irin wannan lokacin? Tinda na yi haƙurin watanni ban gan shi ba me zai hana na ƙara haƙuri har a gama bikin kafin na zo,yanzu gashi zuwana be amfana min komai ba sai tada min da tsohon mikin dake cikin zuciyata da ya yi."

"Zuwan ki ya yi amfani mana Hadiza ! tinda gashi kin ganewa idanun ki shirye-shiryen aure na,a zaton ki tinda kin nakasa ni kin yi gaba babu wadda zata aure ni ko?"

Cikin kuka Mommy ta juya tana kallon Abdussabour da ya harɗe hannayen shi a ƙirjin shi ya tokare ƙafar shi ɗaya a jikin gini yana bin ta da kallo,kallo ne dake huda dika wata sura ta jikin ta yana shigewa cikin jikin ta,da ace suna da aure a wannan lokacin da ta fassara irin kallon da yake yi mata da kallon ƙauna da soyayya,kallon ina son kasancewa dake Hadiza. Sai dai kashh wannan Abdul ɗin dake a gaban ta ba Abdul ɗin da ta sani bane a baya. Ba tare da ta ce komai ba ta ɗauki ledar ta da ta faɗi a ƙasa ta gyara zaman mayafinta zata fita daga soron,cikin sauri ya riƙe mata mayafin ya ce,

"Me yasa kika zo gidan mu a yau? Me yasa kike son ki dawo min da hannun agogo baya? Na tabbata ba ganin Amir bane kaɗai ya kawo ki gidan nan,duk yanda akai kin samu labarin zuwana gari yau shi yasa kika fake da ganin Amir kika zo gani na."

Wata iriyar harara Mommy ta buga masa sannan ta ce,

"Allah ya kiyaye na zo ganin ka Abdussabour,lokacin da na yi begen ka,na so ka aure ni na koma zaman gidan ka saboda ina jin babu daɗi akan abinda na yi maka ya wuce,yanzu sai dai in ce Allah ya baku zaman lafiya da kai da sabuwar amaryar ka."

Cike da ɓacin rai Abdul ya sakar mata hijabi,ita kuma ta sa kai ta fita ta bar gidan cikin sauri ba tare da ta waiwaya ba,rintse idanu Abdul ya yi sannan ya ƙanƙame jikin shi waje ɗaya,wani irin abu yake ji a jikin shi game da Hadiza wanda ya jima be ji ba,ji yake yi wani irin karfi na shigar shi wanda ya jima yana neman irin wannan ƙarfin a tattare da shi tin lokacin auren shi da Huzaimah,a hankali ya shafa jikin shi ya ce,

"Kenan hakan yana nufin na warke? Na dawo cikakke kuma lafiyayyen namiji kamar yanda nake a baya?".............GIDAN ƊAN LITI








RUBUTAWA : HAERMEEBRAERH ✍️✨










PAGE 104:










Kamar wadda ake ingizawa haka ta tashi ba tare da ta damu da kurjewar da ta yi a ƙafar ta ba. Hijabin ta ta sanya da nufin ta tafi gidan Sarkin ta tarar da Abdul ɗin ta roƙe shi ya yafe mata a maida auren su,da sauri Sadeeq ya riƙe ta ya ce,

"Dan Allah Yah Mommy ki kwantar da hankalin ki,kar ki manta da halin da Innoh ke ciki na rashin lafiya,kina tunanin yanzu idan taga halin da kika shiga hankalin ta zai kwanta ne? Kin ga ai se jinyar da ake yi mata ta koma baya ko? Sannan shi fa Baban Amir baya garin nan,Sultan ne ke rabon katin ya ce na kawo."

Waje Mommy ta samu a bakin ƙofar ɗakin ta ta zauna ta rintse katin ɗaurin auren a hannun ta da ƙarfi sai da ta ji ya yage,kuka mai matuƙar ƙona zuciya ta saki tare da juya kan ta cike da ƙunar rai ta ce,

"Na shiga uku ni Hadiza ina zan tsoma zuciyata taji sanyi ne? Shikenan yanzu Abdul aure zai sake yi da wata macen ba ni ba? Da na san haka zan sha wahala a rayuwa ta da ban yiwa Allah butulci ba akan ni'imar da ya yi min ta aura min nagartaccen namiji kamar Abdul da ya yi,tabbas Abdul namiji ne da kowacce mace zata so ta samu kamar shi,yana da kulawa,tausayawa,tare da shagwab'a mace,abun hannun shi be rufe masa ido ba,komai nashi nawa ne,me yasa na manta dika wannan alkhairin nashi na rufe idona na yi rashin mutuncin da ya janyo min wulaƙantacciyar rabuwa da miji na?"

Baaba ce ta fito daga ɗaki ta yafito Mommy da hannun ta,kamar Mommy ba zata tashi taje ba saboda yanda take jin jikin ta kamar na mara lafiyar da ta shekara tana jinya,a hankali ta miƙe ta isa ɗakin Baaba ta zauna a ƙasan carpet ta ci gaba da kukan ta,goro Baaba ta ɓantara ta watsa a baki sannan ta ja ruwan roba dake ɗakin ta miƙawa Mommy ta ce,

"Haƙuri zaki yi yanzu Mommy,saboda aikin gama ya riga da gama addu'a ce kawai zata karkato miki da kan Abdussaboor."

Cikin sauri Mommy ta ce,

"Dan Allah ki faɗa min kalar addu'ar da zan dinga yi har ya dawo gare ni Baaba."

Murmushi Baaba ta yi sannan ta ce,

"Dan Allah ki ga yanda ki ka koma yanzu Hadiza. Mu fa iyaye da muke yawan baku haƙuri idan kuka kawo mana ƙarar mazajen ku ba wai dan bamu son ku bane,soyayyar da muke yi muku ce ta jawo muke baku haƙurin saboda muma shi muke yi a namu gidajen,amma turawa sun nuna muku kar ku ɗauki raini wajen namiji daya yi maku ku rama,sannan kar ku wahaltawa namiji ba aikin ku bane. To ina son ki sani idan har a aure namiji baya dukan ki,baya zagin ki da iyayen ki,yana baki ci da sha ya ɗinka maki sutura ke da yara dai-dai ƙarfin shi,yana biya maki buƙata a gado koda ba koda yaushe bane,to kiyi haƙuri ki zauna a ɗakin ki,saboda duk wadda zata ce maki ki yi masa rashin kunya dan ɗan saɓani ya haɗa ku ba masoyiyar ki bace,tinda bata san rashin kunyar nan me zata jawo maki ba. Idan kuma ke da kan ki ne kike ganin bai isa ya ja zare ba ba tare da kin tsinka ba,to kin tafka babban kuskure,domin kuwa daga karshe zaki faɗa ƙaton ramin danasani ne a lokacin da ba zai yi maki amfani ba."

"Maganar ki gaskiya ne Baaba,ni a yanzu na yi nadamar dik abinda na yi,inshaa Allahu zan san hanyar da na bi na jawo hankalin Abdul waje na,ya taimaka min ya yafe min na koma ɗaki na na rungumi yaro na."

"Allah ya sa Mommy, idan hakan ta faru ai sai kowa ya yi farin ciki a gidan nan,dan kuwa kin yi dacen miji me son ki,kece kika yi wasa da damar ki. Na tabbata yanzu kinga illar mummunan kishi,daga ƙarshe kika ga illar bin bokaye da malaman tsibbu."

"K'warai Baaba na ga illar su,kuma har abada ba zan gushe ba face na ci gaba da neman gafarar Allah,idan Allah ya ƙara bani damar auren Abdul Baaba ko mata uku zai ƙaro bayan ni ba zan taɓa d'aga kai na kalle shi ba balle na hana."

"To da kyau,ni kuma na yi maki alƙawarin zan ci gaba da taya ki addu'a Allah ya dawo maki da shi ku komawa auren ku idan da alkhairi,idan babu alkhairi Allah ya kawo maki wanda ya fishi alkhairi."

A sanyaye Mommy ta amsa da,

"Amin Baaba,inshaa Allahu shine ma alkhairin."

Dariya Baaba tayi wadda ta sanya Mommy jin kunyar kalaman ta,cikin sauri ta miƙe tana faɗin,

"Bari naje na duba Innoh ko tana buƙatar wani abun."

Ba tare da Baaba ta ce komai ba ta ci gaba da taunar goron ta tana dariya. Mommy na fita kuwa sai ta leƙa Innoh taga tana bacci,ɗaki ta tafi ta kwanta a katifar ta tana tunanin Amir,cikin hawaye mai dauke da murmushi ta ce,

"Ko ya iya gudu yanzu? Idan mun haɗu da wanne suna zai kira ni? Ko yanzu ya kai girman wa? Anya kuwa ba zan je na ga yaro na ba gobe?"

Tashi tayi zaune ta na sake nazari akan zuwa ta ga ɗan nata. Daga karshe ta yanke shawarar ko ana muzuru ana shaho sai ta ga Amir a gobe, dan haka cikin ƙanƙanin lokaci ta miƙe ta hau duba kayan ta, kuɗi ta d'akko ta fita tsakar gida,Sadeeq ta kirawo ta aika ya siyo mata kayan ƙwalama da ta san yaron na so. Cike da ladabi Sadeeq ya karɓi kud'in ya tafi shago dan siyowa Mommy abinda ta aike shi.

Kamar yanda ta ƙudirta kuwa washegari da rana bayan ta kammala gyara gidan, ta yiwa Innoh wanka ta sauya mata kaya,sai ta zauna ta bata abinci da maganin ta suka ɗan gwada tafiya a tsakar gidan,suna kammalawa ta kama Innoh suka koma ɗaki,babu jimawa bacci mai nauyi ya ɗauke ta saboda maganin da ta sha da motsa jikin da tayi,tana ganin haka sai ta leƙa tsakar gida taga babu kowa, ledar da aka yo mata siyayyar tsarabar da zata kaiwa Amir ta ɗauka ta duba komai ya yi dai-dai,sai kawai ta fita tsakar gida ta shiga wanka daga nan ta yo alwala sannan ta yi sallar azahar. Tana idarwa ta hau kwalliya sassauƙa ta sanya wani material ɗin ta mai tsada da Abdul ya taɓa siyo mata a zuwan shi kaduna da ya yi saboda aiki,kalar material ɗin ta karb'i farar fatar ta,sai ta yafa mayafin ta ta zira baƙaƙen takalman ta ta ɗauki ledar tsarabar ta ta bar gidan.

Tafe take tana addu'a Allah yasa ta haɗu da Abdussaboor ta sanya shi a idanun ta ko zata ji sanyi a ranta,da wannan tunanin ta isa gidan Sarki. Da Innah Laminde ta fara cin karo a tsakar gidan suna hira da sauran matan gidan,ga goro da chewing gum da alawa nan ana ta ɗaurawa a leda za a kai gida-gida saboda a gayyaci mata auren Abdul ɗin.

Cike da dakiya Mommy ta durƙusa har ƙasa kamar yanda ta saba a baya ta gaishe da Innah Laminde da sauran matan Sarki,kallon ta kowa yake yi kamar sun samu sabuwar halitta,babu wanda ya taɓa tsammanin ganin ta a wannan lokacin,duba da yanda labarin auren Abdul ya karaɗe ƙauyen.

Tana nan duƙe ta jiyo ƙamshin turaren shi kamar a mafarki,kasa tashi tayi daga wajen da take tsugunne sai da Innah Laminde ta miƙe tsaye ta fara takawa ta ce wa Mommyn,

"Shigo ciki ku gaisa da ɗan naki mana."

Sarai Mommy ta gane Innah Laminde bata son Mommyn ta haɗu da Abdussaboor dake shirin shiga cikin gidan ne shi yasa ta yi mata tayin shiga ciki,dan haka tana miƙewa sai ta yi dabarar sakin ledar hannun ta a ƙasa har abun ciki ya watse a ƙasa,cikin wani irin salo Mommy ta duƙa tana kwashe biscuits da chocolates ɗin da suka zube tana mayarwa ledar su,Abdul kuwa da shigar shi gidan kenan idanun shi suka sauka akan Mommy wadda ta juya bayan ta tana kwashe abu a kasa.

Wani irin yawu ya had'iya sai da maƙoshin sa ya yi sama da kasa a fili kafin ya hau ƙyafta idanu da sauri da sauri kamar wanda yake son ya farka daga mafarkin da yake ciki. Mommy kuwa na gama kwashe komai sai ta yi gaba ba tare da ta juya ta kalli inda Abdul ɗin yake ba,tana shiga ɗakin Innah Laminde sai ta zauna a ƙasa tana wani sunne kai,murmushi Innah Laminde ta yi dan kuwa taga dik abinda ya faru,har da halin rikicewar da Abdul ɗin ta ya shiga akan ganin Mommy,gaisawa suka sake yi sannan ta k'wala wa mai aiki kira aka karɓo Abdul a wajen Baban shi aka kawowa Mommy.

Koda ta ɗauke shi ta zaci zai manta da ita ko kuma ya yi mata ƙiwa,sai taga yana ta shafa fuskar ta yana surutai irin na yara. Wasu irin zafafan hawaye ne suka dinga sauka a idanun ta wanda suka yi matuƙar karya zuciyar Innah Laminde har ta ji rashin kyautawar ta akan kaiwa Mommy ɗan ta da bata yi ba har na tsawon watanni masu yawa haka.

Cikin kuka Mommy ta fashe da dariya da ta ga Abdul ya tashi yana tafiya sosai da ƙafafun shi har yana haɗawa da gudu zai fita waje,ƙamshin turaren Abdul ne ya tabbatar mata da wanda yaron ya gani har yake son fita waje. Cikin sauri Mommy ta miƙe tsaye tana share hawayen ta ta ajiye ledar tsarabar da ta kawo a gaban Innah Laminde ta ce,

"Ni zan koma,sai kuma watarana,ina fatan za a dinga kawo min shi ina ganin shi ko da sau ɗaya ne a wata dan Allah."

Tausayin ta ne ya kama zuciyar Innah Laminde,cikin sanyin murya ta ce,

"Inshaa Allahu za a dinga kawo miki shi lokaci zuwa lokaci dan ku gaisa,fatan mu shine Allah ya raya shi ya yi masa albarka."

"Amin ya Allah na gode."

Da alamun sauri a tattare da Mommy amma Innah Laminde ta sake tsaida ita ta hanyar tambayar ta jikin Innoh,cikin sauri Mommy ta ce,

"Da sauƙi alhamdulillah,tana ma gida yanzu haka, bamu jima da dawowa daga asibiti bama."

"To ki ɗan tsaya na kawo maki abun gayyatar biki ki kai musu,muna gayyatar ku ai yanzu mun zama ɗaya."

Wani irin yawu Mommy ta haɗiya,tare da kallon yanda Innah Laminde ke magana cikin kwanciyar hankali,ba dan kar a ga rashin kunyar ta ba,to tabbas da ta gaggawa Innah Laminde baƙar magana,taya zata bata abun gayyatar auren namijin da take mutuwar so a ran ta wai ta kai gidan su? Wannan ai cin fuska ne,daurewa Mommy ta yi ta tsaya tana jiran Innah Laminde a tsakar gida,Amir ne ya dawo ya riƙe mata mayafin ta,babu ɓata lokaci ta duƙa ta ɗauke shi,ƙamshin turaren Abdussaboor dik ya cika mata hanci, lumshe idanun ta tayi ta sake rungume yaron tana sumbatar shi. Abdul ne ya fito daga ɗakin shi ya yi hanyar waje riƙe da makullin mota.

A haka Innah Laminde ta sami Mommy ta miƙa mata leda cike da goro da alewa da chewing gum har da biscuits tace ta kai gida, godiya ta yi mata tare da sanya alkhairi a auren ta miƙa mata Amir da ya fara rikicin zai bita ta fita da sauri,tana isa soron gidan ta fashe da wani irin kuka mai cin rai,dik yanda taso ta danne kukan kasawa ta yi,kanta ta fara tambaya a fili tana faɗin,

"Shin wai ni wace wautar ce ma ta sanya ni zuwa ganin Amir a irin wannan lokacin? Tinda na yi haƙurin watanni ban gan shi ba me zai hana na ƙara haƙuri har a gama bikin kafin na zo,yanzu gashi zuwana be amfana min komai ba sai tada min da tsohon mikin dake cikin zuciyata da ya yi."

"Zuwan ki ya yi amfani mana Hadiza ! tinda gashi kin ganewa idanun ki shirye-shiryen aure na,a zaton ki tinda kin nakasa ni kin yi gaba babu wadda zata aure ni ko?"

Cikin kuka Mommy ta juya tana kallon Abdussabour da ya harɗe hannayen shi a ƙirjin shi ya tokare ƙafar shi ɗaya a jikin gini yana bin ta da kallo,kallo ne dake huda dika wata sura ta jikin ta yana shigewa cikin jikin ta,da ace suna da aure a wannan lokacin da ta fassara irin kallon da yake yi mata da kallon ƙauna da soyayya,kallon ina son kasancewa dake Hadiza. Sai dai kashh wannan Abdul ɗin dake a gaban ta ba Abdul ɗin da ta sani bane a baya. Ba tare da ta ce komai ba ta ɗauki ledar ta da ta faɗi a ƙasa ta gyara zaman mayafinta zata fita daga soron,cikin sauri ya riƙe mata mayafin ya ce,

"Me yasa kika zo gidan mu a yau? Me yasa kike son ki dawo min da hannun agogo baya? Na tabbata ba ganin Amir bane kaɗai ya kawo ki gidan nan,duk yanda akai kin samu labarin zuwana gari yau shi yasa kika fake da ganin Amir kika zo gani na."

Wata iriyar harara Mommy ta buga masa sannan ta ce,

"Allah ya kiyaye na zo ganin ka Abdussabour,lokacin da na yi begen ka,na so ka aure ni na koma zaman gidan ka saboda ina jin babu daɗi akan abinda na yi maka ya wuce,yanzu sai dai in ce Allah ya baku zaman lafiya da kai da sabuwar amaryar ka."

Cike da ɓacin rai Abdul ya sakar mata hijabi,ita kuma ta sa kai ta fita ta bar gidan cikin sauri ba tare da ta waiwaya ba,rintse idanu Abdul ya yi sannan ya ƙanƙame jikin shi waje ɗaya,wani irin abu yake ji a jikin shi game da Hadiza wanda ya jima be ji ba,ji yake yi wani irin karfi na shigar shi wanda ya jima yana neman irin wannan ƙarfin a tattare da shi tin lokacin auren shi da Huzaimah,a hankali ya shafa jikin shi ya ce,

"Kenan hakan yana nufin na warke? Na dawo cikakke kuma lafiyayyen namiji kamar yanda nake a baya?".............
[09/08, 10:39 pm] Aunty Hameeda: GIDAN ƊAN LITI










RUBUTAWA : HAERMEEBRAERH ✍️✨









PAGE 105:







Cikin dabara Abdul ya samu ya bar soron gidan nasu ya shige motar shi yana maida numfashi da ƙyar kamar wanda ya yi gudun ceton rai. Wata iriyar zufa ke karyo masa jikin shi na rawa ya tada motar shi ya wuce gidan shi,tinda ya isa ya hau tina rayuwar su ta baya da shi da Mommy, tsoro ya fara ji


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login