Showing 21001 words to 24000 words out of 276165 words

Chapter 8 - GIDAN DAN LITI BOOK COMPLETE BY HAMIDA SANUSI AHMAD.txt

ta goge hancin ta da shi ta yar ta window sannan ta d'akko sabo ta mayar fuskar ta,a hankali jiki ba k'wari ta gyara fuskarta su Billy na ta yi mata tsiya.

Ta na gama gyarawa suka fita Billy ta riqe akwatin ta a hannu,mommy riƙe da ƙaramar jakar sallahn ta,tafe suke suna yanga kamar waɗanda za su yi tafiya da gaske,shi kuma saurayin Billy na biye da su ya na yi masu video, Billy dake ta saba a waye take da irin waɗannan abubuwan sai ta gyara wayar ta ta na yi masu video itama ta yanda mutane za su zaci tabbas da gaske wajen shiga jirgi za su domin komawa Abuja,Billy ce ta karkace baki ta na ta iyayi ta na video a cikin videon nata take cewa,

"Hello guys ya kuke? Ya kewa ta? To alhamdulillahi gani dai da sister na zamu koma gida mun gama shan hutu a kanon dabo, kanawa ina gaishe ku ina godiya da kulawar ku a gare ni sai na sake dawowa,ku dakace ni idan na isa gida lafiya na huta zan buɗe live a TikTok zamu gwangwaje yau yehhhh can't wait to see you my guys...muahhh love you byeee"

Ta na gamawa ta yi editing ta yi duk abinda ya kamata ta yi posting a social network accounts ɗin ta gaba ɗaya sannan suka yi wasu hotunan suka juya zuwa mota.

Billy ba k'aramin tashin kan Mommy ta yi ba da abinda ta aikata ko banza itama ta samu wani sabon ilimin kuma itama zata yaqi nata mutanen da wannan video da hotuna, a haka suka maida akwatinan su suka kama hanya suka tafi, ko da suka koma gate ba wanda ya tambaye su ina wanda suka d'akko ɗin haka suka wuce zuwa gida.

Tafiyar da suka yi bata da nisa sosai suka isa wata unguwa mai bala'in kyau kamar ba a garin kano ba, dan kuwa a ganin Mommy daga wannan unguwar babu wata unguwa da zata fita kyau a garin kanon,gidaje ne tsiraru kamar sababbi tafka-tafka, basu tsaya a ko ina ba sai a ɗaya daga cikin gidajen,a bakin gate motar ta tsaya mai gadi ya leqo ya duba su da kyau sannan ya yi musu sannu da zuwa suka shige cikin gidan da ya gigita tunanin Mommy, idanun ta har wani kwalla suke kawowa saboda farin ciki, bata taɓa tunanin zata shiga irin wannan gidan ba a rayuwar ta.

A wajen ajiye motoci taga sun tsaya saurayin Billy ya ajiye motar a cikin jerin manyan motocin da ta gani a gidan wajen guda uku.

Wani matashi ne sanye da uniform kalar ruwan ƙasa ya zo ya fitar da akwatinan su Mommy ya wuce da su cikin gidan, sannan su Billy suka riqe hannun juna da saurayin ta suka yi wa Mommy alamar ta bisu ciki, mommy kuwa ta saki baki tana kallon gidan da ya tafi da imanin ta,ginin bene ne mai bala'in girma da kyau, tin daga waje ta ke tunanin shin ya cikin zai kasance ne? A matse kuma a qage take cilla qafa ta na sauri dan tsabar matsuwa ta ga cikin gidan.

Babbar qofa mai jan katako da golden ado a jikin ta aka buɗe suka shiga, tsayawa Mommy ta yi cak saboda ganin kyawun wajen, duk yanda za a kwatanta wa mutum ba zai gane ba matsawar ba ciki ya shiga ya gane wa idanun sa ba,mommy ta shagala da kallon qafar benen da zai sada ka da koma wanne irin dukiya da kayan alatu ne a saman gidan ta ji Billy na wani irin nishi,juyawa ta yi ta ganta manne a jikin saurayin nan kamar za su cinye junan su saboda yanda suke sumbatar juna,bata gama dawowa cikin hayyacin ta ba ta ji takun takalmi masu tsini suna sakkowa daga saman benen nan da yake a laulaye kamar zubin maganin sauro, ta na d'aga kai sama idanun ta suka sauka akan wata baiwar Allah mai bala'in kyau da ado ta na sakkowa cikin yanga da natsuwa,qirjin ta Mommy ta kalla sai ta ji ta raina kan ta,duk da yanda mutane ke yaba kyawun halittarta jikin ta sai ta ga matar nan ta doke ta ta shanye dan kuwa jikin ta kamar na turawa ko kuma larabawa haka yake,kai koma wacce qabila ce wannan ba ta qasar mu Nigeria bace sam.

Qamshin jikin matar kaɗai ya isa ya jefa mai shaqa cikin yanayi na natsuwa da samun kwanciyar hankali,wasu riga da wando ne a jikin ta baqaqe rigar daga sama ba abinda ba a gani har bra ɗin da ta sanya ana gani, sai mazaunan ta da suka cika wandon ya yi fam da shi gwanin sha'awa,gashin ta kuwa har gadon baya yake ya na reto, nan take Mommy ta ayyana a ranta,

'Lallai dole a ga dukiya mai tarin yawa da kuma kayan more rayuwa irin haka,ashe gidan mutanen qasar waje ne, Allah ya sa abarni na yi aiki anan gidan ni ko me wanke-wanke aka ɗauke ni an gama min komai ba....'

Wata iriyar muryar da ta kasa tantancewa ce ta yi magana cikin yaren hausa ta yi nasarar katsewa Mommy tunanin da take yi,cikin sauri ta juya tare da zubewa a gaban baiwar Allah'n nan da ta qarasa sakkowa ta zauna a ɗaya daga cikin manyan fararen kujerun nan masu ratsin golden color a jikin su ta ɗora qafa ɗaya kan ɗaya ta kalli su Billy da ganin fitowar ta bai sa sun rabu da juna ba sai ma faɗa wa saman kujera da suka yi su na ci gaba da aikawa junan su saqonni masu sanya mommy jin kunya, dan kuwa duk iskancin ta bata taɓa bari wani ya gan ta a halin biya wa kan ta buqata ba ko kuma a kama su ita da shamsu suna romancing juna,ko mutum ya gan su to fa ba da sanin su bane amma ba wai su da kan su su yi diplaying abinda suke aikatawa ba a bainar nasi kamar na su Billy.

"Wai ku dan uwar ku ba magana nake yi muku ba tun ɗazu? Zan ci mutuncin ku fa dan iskanci mun yi bak'uwa ba za ku tsaya ku yi introducing ɗin ta ba a waje na sai ku kama juna kamar waɗanda suka shekara basu ga juna ba?"

Da kyar su Billy suka rabu da jikin junan su suna maida numfarfashi, cikin sarqewar murya Billy tace,

"Afwan uwar d'aki na,kin san lamarin ne in ka rabu da rijalu na kwana ɗaya sai ka dinga jin ka kamar ka fi shekara baku tare,to yanzu dai na cika alqawari na da na ɗaukar miki gaki ga Mommy mai suna Hadiza a qauyen Ba Mugu, ko dake ko a can qauyen namu ma da Mommy ake kiran ta,Mommy gaki ga uwar d'aki na Hajiya K'waisa danake baki labarin kirki da arziqin ta, wasu mutane kuma suna kiran ta da Hajiya 'Yar k'waisa,amma ni ina kiran ta da Hajiyata dan kuwa da ita nake taqama na ke tink'aho na ke jin nima wata ce a duniyar nan tamu da irin mu ne kawai ke shanawa"

Hannu Hajiya ta d'aga sannan ta ce,

"Ya isa haka Billy introduction ɗin ya yi yawa, ki bari a hankali zata gane komai, kuma za ta san komai, sannan za ta so komai da zata gane wa idanun ta,ai shi gani da ido ya kori ji ko? Ki barta kawai duk wanda ya yi hakuri da kunun maraice zai kai ga tuwon dare ai,yanzu ki kai ta d'akin da ke kusa da naki daga yau nan ne d'akin ta,kar ku manta ku shirya qarfe bakwai ku sakko yin dinner da ni,ni yanzu zan shirya ne na fita zan je wani waje mai mahimmanci ba zan samu yin lunch da ku ba,"

Ba tare da sun baiwa mommy amsar tarin tambayoyin dake cikin kai da zuciyar ba,ko su bata damar cewa alif, Billy da saurayin ta suka kama hannun juna suka fara tafiya zuwa sama, har sun fara taka matakalar benen inda Hajiyar da aka kira da Hajiya K'waisa ta haye sai saurayin Billy ya ce,

"Ke ! ki yi sauri ki zo dalla kar ki b'ata min lokaci ina da wajen zuwa"

Da sauri Mommy ta sa qafa ta bi bayan su zuciyar ta cike da tarin tambayoyi bakin ta kuma ta na jin shi kamar an d'aure mata shi saboda rashin damar magana da ta kasa samun yi.

Da kyar ta iya dafe qarfen jikin matakalar benen ta dinga bin bayan su har suka isa saman da aka lailaye shi da wani abu da mommy ta kira da katako mai k'yalli a ran ta, kamar dai yanda can ƙasan yake haka saman yake, jin kanta ta yi ya na wani irin juya mata kamar za ta yi amai ko kuma ta faɗi, da sauri ta riqe qarfen da ya raba mutum da hantsilowa ƙasa, ta na hango qasa kuwa sai kanta ya fara juyawa fiye da da,nan take ta zube a wajen a sume....................
[09/08, 10:37 pm] Aunty Hameeda: GIDAN ƊAN LITI










PAGE 9:













Ganin yanda Mommy ta faɗi warwas a qasa ta suma ne ya sanya Hajiya 'Yar K'waisa data kama knob ɗin qofar ta zata shiga d'akin ta tsayawa ta yarfa hannu ɗaya tare da kama hab'a tace,

"Toooh ! Wata sabuwa kaza taji shiqar dare,me zan gani haka ni K'waisan alheri? Ke tada ta maza mu gani, Allah ya sa dai ba jinginanniyar gawa kuka kawo min muhallina ba,"

Da sauri Billy ta wuce dispenser dake a parlourn ta tsiyayo ruwa mai shegen sanyi ta sheqawa mommy, a gigice mommy ta farke facemask daga bakin ta bayan ta farka ta wage bakin tun qarfin ta ta kurma uban ihu,ganin bakin ta ne ya sanya Hajiya K'waisa buga nata ihun tare da faɗin,

"Na shiga uku ni K'waisa me nake gani haka a fuskar yarinyar nan bakin ta kamar an watsa qashi a bola? Ina zan kai wannan ragadadar leb'unan nata? Billy biyo ni, kai kuma kama gaban ka ka dawo watarana ba zan ɗauki iskancin nan naku ba da ranar Allah ba na cikin yanayi na kallon fitsara,"

Jiki ba k'wari Man ya yi wa Billy mata sallama tare da alqawarin zai dawo da dare, d'akin da Hajiyarta ta ta shige itama ta shiga,Mommy kuwa na nan ta na rarrafe ta bar gaban benen har wannan lokacin jiri take ji ga wani amai da yake taso mata, da ta tuna cewa yanzu fa a sama take ba a qasa ba sai ta ji hankalin ta ya sake tashi ta kurma ihu kamar me shigar iska.

A can cikin d'akin Hajiya K'waisa da ya gaji da haɗuwa kuwa Billy ce tsaye ta na tura baki Hajiya dake tsaye ta na sauya kaya a gaban Billy tace,

"Ke Billy wannan wace iriyar halitta ce haka? Ya zaki kawo min matsala a cikin gida haka muka yi dake?"

Murmushi Billy ta yi ta ce,

"Haba Hajiya ai wannan ba wata matsala bace,bakin ne fa kawai sannan tsorata ta yi fa da ta natsu zaki ga ba wani girma ne dashi ba na azo a gani, kuma ko ba komai ai tana da kyan ta da bata da kyan ma ai ba zaki nace a kawo maki ita ba,sannan baki ga yanda take sake da facemask bane koda yaushe? Bayan haka ma yanzu fa irin su ake so ko kin manta ne? Ai wannan babbar kadara ce ki yi tunani da kyau ki gani"

Shiru Hajiya K'waisa ta yi kafin daga baya ta saki wani shu'umin murmushi ta ce,

"Kuma fa haka ne Billy ni nakan manta da cewa wata arhar ma tsada ce,ba komai na san yanda zan gyara baqar tukunyata ta fidda min farin tuwo,kama ta dan Allah kar ta mace min saboda tsoro ku garin ku ba ko dan irin benen nan ne na gidan me gari ko me unguwa ake cewa whatever? Allah dai ya wadaran naka ya lalace Jakin dawa ya ga na gida,wannan idan zuwa taro Abuja ya tashi sai dai a tura ta ta mota dan ba zan jera da ita ba ta kore min customers, maza maza jeki ni,"

Hajiya K'waisa ta qarasa maganar ta tana yarfa hannu tare da nuna wa Billy hanyar waje,cikin dariya Billy ta kama hanyar fita daga baya ta hau mita ta na faɗin,

"Yanzu da ki ka kore min Man d'ina ya kike so na yi fisabillahi"

"Ki kunna live a gidan ki na TikTok da ranar nan ba zaki rasa 'yan balaja'u ba irin ki sai ku yi wa juna abinda kuka saba har ku gamsu, ni jeki ina da appointment ne da likita."

"Ok to sai kin dawo,Allah yasa dai wannan karon a dace,"

"Ameeen kedai"

Billy na fita direct wajen Mommy ta nufa ta kama ta ta yi wani d'aki da ita wanda ya ke ɗauke da makeken gado, d'aki ne mai kyau sosai sai dai be kai na Hajiya K'waisa kyau da tsaruwa ba, a hankali wannan kyan d'akin ya fara ɗauke hankalin Mommy daga tunanin inda take, bayan wasu mintunan sai ga Mommy ta ware ana ta ganin d'aki da ita, babban abinda ya fi burge ta bai wuce band'aki da ta gani a cikin d'aki ba irin wanda take gani a waya,ga bathtub mai shegen kyau ga kayan wanka kala-kala, murna ce ta kama ta ta shiga bayin Billy na nuna mata komai na ciki da yanda ake amfani da shi, wajen heather ta kaita, ta dage sosai tana nuna mata yanda ake amfani da ita saboda kar ta je ta babbake kan ta da ruwan zafi, Mommy kuwa ta natsu sosai dan jin yanda ake amfani da komai cikin sauqi ta haddace komai saboda dama tana gani a waya, ko benen ma tana ganin shi a waya kalar wannan murd'ad'd'en ne bata taɓa gani ba, sannan kuma bata taɓa hawa ba shi yasa da ta ji ta a saman ta hango qasa da nisa ta fara jin jiri har hakan ta kai ta ga suma,a haka suka gama ganin d'akin ta kuma tabbatar wa da Billy ta gane komai da yanda ake amfani da komai sannan ta wuce ta bar Mommy na zuba qauyanci.

Billy d'akin ta ta shige ta yi wanka ta fito daga band'akin haihuwar uwar ta ta ɗauki laptop ɗinta ta kunna sannan ta shiga social Media, har na zauna na d'akko maku rahoton dalilin da yasa ta zauna babu kaya na ga abinda take aikatawa ya yi munin da hannu na ba zai iya rubutawa ba, saboda ban taɓa tsammani ko tunanin akwai 'ya'yan musulmin da ke aikata irin wannan lalatar ba, da sauri na ja mata qofar na koma d'akin mommy.

Kwance na ganta a gado tana mulmula daga wannan wajen ta koma wancan, can sai ta miqe da gudu ta d'akko jakar ta ta zaro wayar ta da ta sha faci da salatef ta kunna, No Sule ta lalubo ta kira, ta jima tana ringing kafin daga baya ya ɗauka, yanayin yanda yake magana kaɗai ya isa ya sanar da ita a halin da yake ciki dan kuwa ita ba baquwar shiga irin wannan yanayin bace, kuma ta san me yayan nata yake aikatawa a duk sanda ya rufe qofar d'akin sa da ranar Allah yace zai yi barci kar a dame shi.

Cikin jin wani irin shauqi da kewar shamsu tace,

"Sule dan Allah idan ka gama abinda ka ke yi ka kai wa su Innoh waya mu gaisa na faɗa masu na iso lafiya, Sule ka ga gidan da aka kawo ni kuwa? Innalillahi sule wannan shi ake kira da aljannar duniya, wayyoo Allah ka ji laushin gadon da nake kwance akai kuwa? Ka ga kyan makewayin su kuwa? Makewayin mugun zabgege sukutum da guda aka ce nawa ne ni kaɗai,sannan d'akin ma duk girman shi da tsaruwar shi wai nawa ne ni kaɗai"

Tun Sule na jin ya matsu ta kashe waya ya ci gaba da abinda yake yi sai ya ji kwad'ayin son ganin wajen dan ya kwad'aitu da son zuwa kanon nan shima dai, dan kuwa duk 'Yammatan da yake faman biya wa buqatar sha'awar su ta waya suna ce masa a kano suke wasu a wasu sassan jahohin arewa suke kaɗan ne a kudu,Sule ya yi qaurin sunanda da ace mutanen da yake mu'amala da shi za su san asalin ko shi wanene tabbas da babu mai sake kula shi a cikin su,da muryar shi mai shegen daɗi yake yaudarar matan da suka kwashe kayan su daga gaban ma'aikin Allah suka kai gaban shaid'an suke kwasar ilimin yanda za a saɓa wa Allah.

Sunan da Sule ke amfani da shi a social media ma kan shi abun kyama ne ga dikkan mutum mai hankali, dan kuwa baya ma b'oye abinda yake aikatawa a social media. Da damar matan da ke tura masa kuɗi da data ta waya da account ɗin shi sun matsu su yi tozali da gwarzon kyakkyawan namijin da muryar shi ke ɗebe masu kewa amma sule ya yi fafur ya ki yarda kowa ya gan shi. Hasali ma hoton wani matashin buzu ya sanya a profile picture ɗin shi na kowanne kafa ta sada zumunta da yake amfani da shi, dan haka da damar matan nan sun amince wa kan su sule fa kyakkyawan saurayi ne mai kuma murya mai daɗi.Duk wadda Sule ya yarda ya nunawa kanshi to fa shaƙuwar su ta kai shaƙuwa ne ya sanya shi bayyana mata asalin fuskar shi.

Sun jima sosai Mommy ta na bashi labarin yanayin gidan da aka sauke ta kafin daga baya su yi sallama ya kuma yi mata alqawarin idan Baban su ya dawo zai haɗa ta da shi da mutanen gidan ta waya su gaisa,kafin nan zai sanar da Innoh sun isa lafiya, godiya ta yi masa suka yi sallama ta kashe wayar.

Band'aki ta shiga ta tara ruwa a kwamin wanka ta zuba kayan wanka kamar yanda Billy ta sanar da ita ta shiga ta kwanta yanda taga turawa na yi a cikin ruwa idan sun shiga haka itama ta yi.

Ta jima zaune ciki tana dirzar jikin ta kafin daga baya ta fita saboda k'wank'wasawa qofar da ta ji ana yi,towel ta d'aura a jikin ta sannan ta fita kan nan ya sha wanki sai d'igar ruwa yake yi ya cunkushe waje ɗaya,fatar ta sai ta qara wani sheqi da kyau da santsi


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login