Showing 297001 words to 300000 words out of 495987 words
Chapter 100 - Cutar Kai Book Complete Hausa Novels by Aysha Bagudo.txt
yake a duniya kisna ta gama tozartashi ta gama wulakantashi duk abinda yayi mata bata gani ba me take so yayi mata idan ba rayuwarsa take son dauka ba, yanzu ya sake yarda da cewar kisna bata qaunarsu bata son ganinsu cikin kwanciyar hankali tunda har yanzu ta kasa rabuwa da wannan yaron da kyar ya iya mikewa yana layi direba yayi saurin riko shi suka nufi hanyar parlour'n cikin haka motar muradi ya shigo gidan ganin dady na daga kafafunsa da kyar yasa yayi saurin fitowa ko tsayawa rufe motar bai yi ba ya biyosu da sauri ya amshi dady a hannun lawan "lafiya lawan me ya sa meshi nan ya shiga koro masa abinda yasa dady ya dawo haka nan take muradi ya waska masa mari cikin zafin zuciya yace "me yasa ka fada masa baka jira na dawo ka fada min ba ?"kayi hakuri yallabai bazan iya masa karya ba "tari dady yayi wanda ya sake dagawa muradi hankali "sannu dady plz take it easy everything will be okay suna shiga dakin ya zaunar dashi ya bashi ruwa yasha sannan ya tasa shi gaba jikinsa a sanyaye yana kallonsa qirjinsa na bugawa da karfin gaske har tsawon minti goma yana zaune a daki batare da yace komai ba dan ya rasa da wani kalma zai yi amfani dashi cikin haka dady yayi karfin halin gyara zamansa hawaye na gangarowa ta gefen fuskarshi "plz dady karkayi hasarar hawayenka a banza ka fada min me kake son ayi ? "wani mataki kake son a dauka akanshi idan cewa kayi a batar dashi a garin nan zan maka dady dan Allah ka fada min bazan juri ganin hawayenka ba ya karasa maganar yana kai hannunsa domin goge hawayen dady "bana bukatar komai Aliyu na gode bisa kulawarka gareni ka damu da damuwata ina sonka bana son rasaka a cikin ahlina "bazaka rasani ba dady saboda ina tsananin sonka tamkar rayuwata.
dady ya runtse Idanunshi sai ga wasu hawaye sharrrr a hannun muradi "ya rabbi dady ka daina kuka haka" dady ya damke hannun muradi jikinsa na rawa kamar mazari "ka min wata alfarma dan Allah "ka fada min dady kowace irin alfamarce wallahi zan maka idan ta kama na baka rayuwata a shirye nake zan maka "ka... ka taimakeni ka auri kisna ......" dady yayi maganar cikin rawar murya .
Wani irin shock zuciyar muradi tayi tare da tsintar kanshi cikin, yanayi mai sarkakkiya da wuyar fassarawa ya ziyarci zuciyarsa dama gangar jikinsa take duniya ta tsaya masa cak ta daina juya masa hatta ac dake aiki a cikin dakin yaji ya daina aiki qirjinsa ban da dokawa babu abinda yake "kayi hakuri dana ba dan bana sonka bane ,ban san yadda zanyi bane duk da na dade da wannan burin acikin zuciyata idan kana ganin akwai damuwa shinkenan abar shi kawai " cikin tsanani tsoro muradi ya dawo haiyacinsa tare da sanyawa jikinsa jarumta yace "meye haka dady ? "dan Allah ka daina min haka dan wannan ai mai sauki ne ba dai auren kisna kake son nayi ba ?" dady gyada masa kai "karka damu a shirye nake ko a yanzu kake so ni mai bin umarnin kane ya karasa maganar zuciyarsa na tafarfasa kamar zata tarwatse a yadda yake maganar kasan zuciyarsa ta shiga rudeni mara misaltuwa dady ya bude baki zai yi magana "karka ce komai dady magana ya kare kace abinci idan baka ci ba bari naje na kawo maka ya mike "ina zuwa dady "
Dady yayi saurin riko hannunsa hawaye ya gani a idanunsa wanda tun bayan barin kisna kasar nan bai sake ganin ba sai yau shima yau din a dalilin matsalarsa daman kuma so tari matsalarsa ce ke haifar da zubar hawayensa hankali dady ya tashi ya mike ya rungumeshi ajikknsa yana kuka "kayi hakuri dana kukan da muradi baya son yi shi yayi dole a dalilin kukan dady sai da sukayi mai isarsu sannan sukayi shiru suka zauna suna fuskantar juna " mumy dake tsaye a bakin kofa tana kokarin shigowa ganin shiru har kusan tara dady bai dawo daga fitar da yayi haraban gida ba ta fito ta tambayi baba mai gadi yace mata ya koma shine ta biyosa anan taji duk abinda suke tautaunawa tayi mutuwar tsaye agurin ta dawo tamkar mutun mutumi da kyar ta sanyawa jikinta jarumta har sanda suka dawo haiyacinsu ta juya jiki a sanyaye tana goge hawayenta ta daura kular abincinsa akan tire da plet da spoon ta dawo ta shigo dakin bakinta dauke da sallama muradi yayi saurin mikewa ya amsa tiren hannunta ya ajiye, shi da kanshi ya zuba musu abinci jiki a matuƙar sanyaye yace "dady sauko muci "babu mutsu dady ya sauko ya zuba masa ruwa ya wanke hannunsa sannan suka fara cin abincin da suke jinsa tamkar suna cin magani mumy ta tsura musu ido kawai tana kallonsu cike da tausayawa ,a ranta tace "wannan auren bazai taba yiwuwa ba sai dai a bada ita acikin danginka amman bazan yarda ba , ina son muradi nasan yadda kisna ta tsaneshi zata iya kashe min shi idan ya mutu ya zanyi? tayi wa kanta tambayar tana kukan zuci ta mike ta bar dakin ta shiga ɗakinta ta kwanta shiru .
har kusan shabiyun dare muradi na tare da dady har yayi wanka ya bashi maganinsa ya sha ya juya zai bar daki ya kira sunansa "Aliyu ..."
"Na'am dady shiga bayina kayi wanka ga jallabiyata can kasa kazo ka kwanta a bayana "babu mutsu yace "to dady ya dauki jallabiyar dady ya shiga bayi yayi wanka ya fito sanye da jallabiya ya hau gado ya kwanta a bayan dady sai dai duk yadda yaso ya runtsa ya kasa tashin hankali iri iri yake hangowa a rayuwarsa idan ya auri kisna sai dai a ransa ya kudurta duk abinda zai faru sai dai ya faru amman bazai taba bujirewa umarnin dady ko kashesa kisna zatayi zai daure a rayuwarsa har kusan daya da rabi Samir bai ga muradi ya shigo ba ya sauko ya shiga dakin mumy ya isketa zaune akan abun sallah tana lazimi ta d'ago idanunta da suka canza ta kalleshi "mumy lafiya ? Ta gyada masa "muradi fa har yanzu na kira wayoyinsa suna ringin bai dauka ba "sai lokacin ta bude bakinta "yana dakin dadynku "Okay ya juya ya fita ..
kwana biyu muradi baya fita ko'ina tambayar duniya Samir yayi masa amman babu kaukwaran dalili haka zalika dady ko nan da kofar gida baya fita nan hankalin Samir ya sake tashi ya damu sosai ya tambayi dady bai boye masa komai ba ya fada masa abinda ake ciki,Samir ya jinjina girman al'amari dady ya numfasa yace " ka dinga bawa Aliyu lokacinka kaji dan yana cikin damuwa ,dan Allah ka kwantar masa da hankali "inshallah dady karkayi ji komai kai ma ka saki jikinka ,hakan ma shi yafi wallahi ayi mata aure Allah ya tabbatar da alkhairi dady yace "ameen "duk mumy na hankalce dasu itama kisna mumy ta hanata zuwa ko'ina hatta mukulin motarta ta kwace abun bai bata mamaki ba dan tafi tunanin direba ya fada mata suna haduwa da Musa ne bata damu ba tasa aranta babu wanda ya isa ya hanata zuwa inda yake ,kuma babu wanda ya isa ya hana aurenta dashi a rana na uku ta shirya ta fito ta shiga dakin mumy ta iske tana bayi ta bude dirowarta nan taci karo da mukullin motarta tasa hannu ta dauka ta fito haraban gidan tana bawa mai gadi umarnin budewa "Alhaji fa yace kar abude miki get "akan wani dalili kenan ?"dan Allah tsoho ka bude kafin na tada mota nabi ta kanka kaji min Tsoho da shishigi tsiya wallahi duk laifin dady ne meye ma zai barka ka cigaba da aiki a karkashinsa bayan ka gama zama taushe ka rube har kana wari "yau sakina ni ne na rube ? "sosai kuwa "to bazan buɗe miki ba "aikuwa ina tada motar zan bi ta kanka wallahi ta karasa maganar tana shiga motar ta tayar ganin da gaske kansa tayo ya dakatar daita da hannunshi "dakata dakata zan bude miki "da dai karka bude kaga yadda zan tarwatsa kanka yanzu babu yadda ya iya ya bude mata ta fita ita ta dawo gidan ba sai karfe shida na yamma dady na tsaye rungume da hannuwansa duka a qirji ta shigo ta paka ta fito "daga ina kike ? daga gurin musa ta bashi amsa kai tsaye da haka babu wani alamar tsoro ko fargaba "daga gurin musa dady ya maimaita amman kafin ki fita me baba mai gadi ya fada miki ? "bai ce miki nace karki fita ko'ina ba "?"eh yace sai dai zuciya bazata iya wannan hakurin ba ni wallahi dady da zaka taimaka da ka aura min Musa kawai , wai wahalar ban da kuke guje min bani zan sha kayana ba ? "
Yayi shiru yana kallonta cike da tsananin mamaki kafin daga baya ya daga hannu zai ɗauketa da mari ta goce ta nufi falo ya biyo bayanta "dan ubanki bazaki auri wannan shegen yaron ba saboda na rigada na miki mijin da zaki aura a tsakiyar parlour'n gidan ta tsaya tana duban dady qirjinta na bugawa saboda jin maganar yayi mata miji "kin dai ji abinda na fada miki kar na sake ganin kafarki a waje inshallahu rana ita yau zan daura miki aure ..... "da wa kenan dady kake kokarin daura min aure ? "Aliyu yaron kirki yaron arziki "waye ma Aliyu zee dake zaune tayi tsigil tace "ina ganin muradi dady yake nufi amman gaskiya kisna da kinyi sa'a ya Aliyu sukuntu guda "dan Allah dan Annabi malama enough ta dakatar daita tana daga mata hannu "akan wannan shegen mara galihu kike cewa nayi Sa'a ?" sa'ar me nayi kenan idan na aure shi?" Suna cikin wannan halin sukaji sautin muryar mumy "Wallahi kisna ki kiyayi kanki kuma kiji tsoron Allah kibi Allah ki bini nida mahaifinki idan bakya son rayuwarki tayi wani iri , ke ba'a kya tare da wasu yara marasa jin magana bare ace su suke koya miki halinki dai yana kokon ranki kina nan kina gina raminki ne wanda zaki fada ciki a watsa miki kasa saboda ni nafi karfinki ,ban uwata ban yiwa ubana ba haka kuma nasan dalilinki bazaki kasheni ki rabani da sauran ya'yana ba sai kwana ya kare duk da kin daura min hawan jini amman bazaki taba ganin bayana ba akan idanunki zan rayu na more sauran yarana ".
"mumy kice Allah shiryata "inji cewar zee "bazan ce ba zainba kudi nawa na kashe akan wannan yarinyar da Allah kadai yasan irin kadarorin dana mallaka amman akanta duk na karar batare da sanin kowa ba ina ne banje ba wani kauyukan yarbawa ne ban shiga ba akanta ,nice nan nice can yar burouba shegiya yarinya "kalmarki bata dace ba mumy kiyi hakuri ki cigaba da yi mata addua kiyi hakuri dan Allah dan Annabi har yanzu da sauran kisna "babu wani saura tunda tasan tayi soyayya har ta tsaya tana fadawa mahaifinta abinda ta gadam akan shege yaro kazami yaron da ko a mai gadin gidanta yayi kadan a dauke shi amman ta tsaya tana wahalar da kanta kuma ai ta wuce a kirata da kalmar yarinya wallahi gabad'aya bana yin kisna yanzu kuma babu wanda ya isa ya aurawa muradi ita a hadashi da wahalar duniya me zayi daita ? wallahi ko ganni kisna bana qaunar yi wallahi na tsaneta kamar yadda na tsani mutuwa......."
Wata killa zan kara page daya kafin ramadan 🤝
Muna saida ingantattun maganin mata masu kyau da nagarta wanda ko da kudinka sai da rabonka tsimi , zumar Mata, gunba, gari insertion,kaza,zakara ,
jigida dadai sauransu.
1.Tsumi Yana saukarwa mace niima Kuma bazataji wuyar jimai ba.
2. Zuma Tana taimakawa wurin Jin sha'awa Kuma itama Tana taimakawa wurin jindadin jima'i.
3.insertion( Dan matsi) daban dabanne akwai Wanda ke matse mace kuma yake saukar da ruwan ni'ima sannan akwai na mallaka , idan ana bukata a tuntubi wannan number
234 815 945 0159..
Mmn Sudais
[7/19, 5:32 PM] +234 803 631 5951: 💗💗💗💗💗💗
CUTAR DA KAI
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
Page 43
~TRUE LIFE STORY~
*PAID BOOK*
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
bismillahirrahmanirrahim
"Wannan littafin na kudi ne ,mai bukata karanta shi zai tura 500 ta wannan account number din 1438775094 Aishat Abdullahi Access bank ,Idan an tura sai a turawa wannan number alert +234 803 238 4602 domin tabbatar da an tura , ko wannan number 08059623096 Idan Kuma vtu za'ayi sai a tura ta wannan number 08059623096 ,kada ayi vtu a number MTN sannan kada a Kira number mtn ba'a kira dashi only chart ne . "domin sauraran littafaina sababbi da tsofaffi za'a iya tuntu'bar Channel dina ta Hausa bakwai,sannan muna bada sarin Lagos lace da kamfala ,Lagos rapa , jaka da takalma, getzner na cotonou da chiganvy, volyal lace duk akan farashi mai sauki ,ga mai bukatar siyan ɗaya ko sari yayi magana ta wannan number 08059623096.
....nan take ya fada masa abinda ya faru , naunauyen ajiyar zuciya muradi ya sauke tare da runtse Idanunshi yana mai tsanani jin bakinciki da takaicin yadda kisna ke jaraban kwakwan son wannan katantawar yaro a hankali ya bude Idanunshi da kyar ya tsura mata ita kuwa banda mugun kallo babu abinda take masa zuciyarta na bugun tara tara wanda yasa gaba-daya ya dauke Idanunshi akanta babu shiri ya kawar da kanshi gefe ba dan tsaro ba sai dan kwarjininta dake gareta a cikin Idanunshi kallonta kawai na haddasa masa jin faduwar gaba .."
"barta Samir ai na dade da sanin ta haukace akan musa mayaudari mun fada yanzu ma muka fara fada kada Allah yasa ki yafe mana har abada inji cewar mumy dake kitchen tana kimtsa kitchen saboda fara shirye shiryen biki " bazamu daina kiransa da mayaudari dan tasha dan iya gurguwa ba ...." mumy na gama fadar haka gaba-daya suka kwashe da matsanancin dariya har da rike ciki banda muradi to shi ina yaga ta wani dariya kisna ta tsareshi da mugun kallo , mumy ta koma kitchen ta cigaba da aikinta shi kuma muradi ya juya da zumar barin gurin dan bazai jurar irin kallon banzar da take masa ba ."
kisna ta juya cikin tsanani fushi ta koma cikin daki tana haki tamkar mai cutar asma ta barsu nan suna cigaba da zagin musa madu yace "ita wannan fa gaba-daya bata da hankali har yanzu kanta na cikin tukunya da gaske bata san lalata mata rayuwa kawai zai yi ya barta da nadama ba amman dan shashanci ta wani kwallafa zuciyarta akan dakikin yaro har akan shi zata tsaya tana mana Allah ya isa," inshallahu wannan satin kawai suka rage miki a cikin gidan nan batare da aure ba, zaki auri muradinmu mu huta ya karasa maganar cike da jin dadi da gudu ta fito daga daki tamkar wata zararriya "ba ameen ba , kuma bakinka ya sari danye kashi , kuma inshallahu babu wanda zan aura sai musa shi kuma muradi Allah ya tsine masa ai kuwa ko gama rufe bakinta batayi ba madu ya rufe ta da duka muradi daya juya yana taku a cikin parlour'n hannunsa rike da waya yana kokarin tura sako ya juyo da sauri ya karbeta daga hannunsa yana masa fada cikin zafin zuciya "haba madu meye haka ne ?" me yasa zakayi haka "? yayi masa tambayar ajere yana furzar da iska "dan girman Allah yaya ka barni na ƙaryata ni zatawa rashin kunya akan wani jaki can ?" dan taga kuna kyaleta ne shiyasa kullum iskancinta ke gaba wallahi ni karairayata zanyi "ka min daidai wallahi madu kara mata inji cewar mumy data leko daga kitchen yarinya kamar mai kunnen kashi kullum rarrashi ake akan magana daya kina botsarewa mutane idan kin cika yar halak idan an daura aurenki da muradi ki kasheshi kiga yadda ba zanyi gunduwa gunduwa dake ba shasha kawai ta karasa magana tana koma kitchen jin abinda mumy ta fada yasa muradi ya nufi kitchen ya tsaya kusa da mumy batare da yayi magana ba .."ya'akayi ko akwai abinda kake bukata ne ?ya girgiza mata kai kawai zuciyarsa na masa zafi tamkar zata kama da wuta da kyar ya bude baki ya fara magana cikin kunnar rai "bana bukatar komai mumy sai alfarma agurinki " uhmmmm ina jinka"alfarma me kake nema agurina ?"dan girman Allah mumy ku daina wa kisna abinda kuke yi mata akwai ciwo fa a aura maka wanda baka so "muddin kina son ganin kwanciyar hankalina mumy ki daina mata abinda kike mata kuma ki fadawa su madu karsu sake taba lafiyarta tunda ita ba jaka bace haba su komai duka duka da abinda ya kamata da wanda bai kamata ba duk duka ne agurinsu gaskiya ni banaso"har ya gama maganarsa mumy bata d'aga kai ta kalleshi ba ya juya ya fita wasu zafafan hawaye masu zafi suka zubo mata na tausayinsa gashi dai kullum shi cikin kokarin kareta da tsare rayuwarta yake amman ita sam ko ajikinta "kije ki rarrasheta a karo na farko ko zuciyarta zata saduda ta amshi aurensa ayi komai cikin kwanciyar hankali , hannunta ta wanke ta fito zuwa falon inda ta iske kisna durkushe tana kuka tamkar wacce akace uwarta da ubanta sun mutu mumy ta kamota jikinta ta sata gaba zuwa cikin dakinsu