Showing 366001 words to 369000 words out of 495987 words

Chapter 123 - Cutar Kai Book Complete Hausa Novels by Aysha Bagudo.txt

amman ya hakura ya danne zuciyarsa ke me yasa bazaki yi yadda yake yi ba".  kin manta da komai ki rungumi mijinki shine aljannarki ki daina wani kunbure kunbure banza dan kinga komai kika yi masa yana  kyaleki wallahi zan fada masa yanzu idan kin cigaba da kunbure  kunbure nan ya mazgeki"cikin Muryar kuka kisna tace "yanzu aunty ummi saboda kin tsaneni sai   kice  ya bubugeni  ?"ni zaki ce a bubuge wallahi kuwa zan yiwa dan'uwanki  bori  ta k'arasa maganar tana dariya "Shikenan bazan ce ya bubbugeki amman ki saki ranki "na  daina  inshallahu zan baki mamaki amman wallahi na rasa me yasa yake bani haushi Amman zan dinga kokari na rinka cire kiyayyarsa a raina zan cigaba da hidimar gabana ku ci-gaba da min  addu'a sun dade kulle a daki sannan aunty ummi ta mike  tayi  mata  sallama ."
******
Tunda   kisna  ta dawo gidan bata  shiga  harkokin muradi  zamansu  kamar da  babu girki babu aikin komai sai tayi ra'ayi sai dai babu zagi babu  kallon banza lamuran gabanta kawai  take   shima   haka  baya  shige  mata ya  barta  har sanda zai samu  wacce zata soshi  da qaddarar rayuwarsa, komai  tayi  ido ne nashi hatta  wayarta da musa ta dawo  babu  ruwan ta ko  a gabansa amsa kira  take  wannan dai ya kasa hakuri dan haka ya shiga ya fita har sai daya ga an kama musa an tsareshi a hannun ma'aikata kuma yace duk wanda yazo kar abada belensa hakan ya kwantar masa da hankali ita kuwa rashin samunsa ya daga mata hankali sai dai ba kamar yadda take ji ada ba wanda idan da ne  bataji muryarsa ba sai tayi kamar zata mutu ya shigo ya isketa tana Zariya a falon rike da waya kallo ya fahimci inda damuwarta ta dosa bai wuce akan rashin samun number musa  ba ya d'auke Idanunshi ya shige d'akinsa  ".
watan   hudu  kenan  da komawa kisna  gidan  muradi  sai  ga  sadiq tare da  madu ya kawo shi a wata safiyar asabar muradi  na zaune a falo yayinda  kisna ke zaune a dakinta  sautin  Muryar muradi dake fita da karfi ne  yasa ta fito  da sauri dan bata saba jin sautinsa haka ba shi din mutun ne mai magana cikin sanyi murya kuma a natse , tana fitowa idanunta ya sauka akan wani matashi  kyakkwa mutun    mai kyaun gaske kamar muradi sai dai shi  dogo ne kuma  baki  sai dai  fuskar da jikinsa  da kwai  alamun yana smoky ta k'arasa shigowa falon  inda muradi  ke faman dukan qirjinsa  "irin  rayuwar da za'bawa kanka kenan kou?"  wannan shine alkwarin da muka yiwa mahaifiyarmu  ?" ka maida kanka dan shaye shaye yanzu zuwan me kayi  "? ka tashi ka bar gidan  nan  banason ganinka har sai ka dawo yadda nake son ganinka ta yadda shi kanshi makiyinmu zai yi nadamar abinda ya aikata mana  madu ya  shiga  tsananinsu yana bawa  muradi baki  akan yayi hakuri "babu wani hakurin da zanyi madu kace  masa kawai  ya wuce  banason ganinsa  wai a kalli sadiq a kalleni ace uwa daya ce ta haifemu  ? yayi maganar kamar  zai yi kuka zuciyarsa na tafasa " na dauka shine wanda zai  tallafi rayuwarmu  a she Shima zai dawo tamkar wancan mashiririnci uban nasa ne ," shifa mahaifiyarmu ta danka amanarmu a hannunsa Amman  kalli yadda ya dawo kalli yadda ya maida rayuwarsa kamar dan daba duk sadiq ya rude sai zufa yake fitarwa yana cewa "kayi hakuri dan'uwana  nima ba'a son raina  bane wallahi zan canza zan dawo tamkar yadda kake son ganina  "ya Ali kayi masa hakuri  kaji abinda yace dan  Allah ka barshi ko zuwa anjima sai na dawo na d'aukeshi daman mumy bata ce ya zauna tare daku ba  tace akawo shine  ku gaisa  " .nan take kisna ta fahimci  d'aunwasa sadiq ne  data take jin labari idan hirar ta dauro a bakin mumy  "ni dai madu kace masa ya tashi  ya wuce banason  ganinsa nasan halin sadiq ya rigada ya dauko mugun halin ubansa   ".
"saboda me zakace ya tafi  ?"ya tsinkayi sautin Mmuryar kisna   cike dakiyar zuciya  ya juyo  yana ffuskantarta ta tsareshi da kyawawan idanunta masu matukar haske."ya madu ka wucewarka kawai  babu  inda zashi muna  nan  tare wani sanyayyiyar  ajiyar zuciya madu ya sauke bai taba jin  kisna ta burgeshi ba  irin  yau yayi murmushin jin dadi tare da yi musu sallama  ya juya  ya wuce."ya  sadiq  ka zauna mana  ya  kake  wani dari dari  ka saki jikinka nan gidan  tamkar gidanka ne zauna  bari  naje  na kawo  maka abun sha " mutuwar  tsaye  muradi yayi  yana dubanta cike da matsanancin mamaki bai taba expecting zata so dan'uwansa  har ta mutuntashi ba zama sadiq  yayi  yana kallon fuskar muradi  kisna  ta shiga kitchen ta fito  da  tire Wanda ke dauke da  ruwa da lemu  da cup ta fito ta ajiye a gabansa ta bude  kwalin  ta tsiyaya a cup ta mika masa  ka fara sha   kafin na gama maka  abinci  ya gyada mata  kawai  sannan ya amsa ya kai baki , shi kuwa muradi kallonta ya cigaba dayi , yaji kamar yace kar sadiq ya sha dan yasan halinta yadda bata sonshi din nan zata iya illata duk wani nashi ,sai dai kafin yayi hanzarin hanashi tuni ya shanye ya sake tsiyaya wani yai  shiru tare da zuba masa ido suna zaune ta dawo da wani plet mai dan girma  Apple da banana  da ya'yan  inibi  ta ajiye masa" kaci kaji ya sadiq wai ma yaushe kazo ne ?"dazu nazo da asuba a gidan takwarana na sauka daga nan aka kawoni gurin mumy shine byn na dan huta tace akawoni nan "ai kuwa mumy ta kyauta  nan dai suna hira tana tashi tana duba abinda ta daura ta burge muradi  sai dai  kuma a ransa yace  duk na  munafurci ne may be wani shiri ne  daita akansa , dan haka ya tattara kayayyakinsa  ya shige   d'akinsa  ya barsu cikin ,  kankanin lokaci ta gama dafa masa taliya ta kawo masa  lomar farko da kyar sadiq  ya hadiye saboda rashin dadin abincin  ga yajin daga zabga   amman haka yayita turawa yana mata godiya ko babu komai ta mutuntashi  yana cin tana jansa da hira har ya gama tace ya tashi suje masaukinsa dakin dake bayan part dinsu ta Kai shi  "ga daki nan  ka shiga ka saki jikinka fa babu abinda zai faru  yace "na gode "baka bukatar gode min ta juya ta koma ciki ai tana fita  ya fada bayi saboda cikinsa daya murd'a dan baya son yaji ruda masa ciki yake nan  ya shiga  zuba zawo sai daya kusan minti goma sannan ya fito yana sauke numfashi "idan na cigaba da cin irin wannan abinci zan mutu nan kusa ya fada yana fadawa kan katifa  ."

  tun zuwan  sadiq bai fi  sati  biyu ba ya fara fahimtar yadda halaiyyar matar  gidan  yake adalilin rashin kulawar da bata bawa dan'uwansa    amman bai tofa nashi ba ya zuba ido  tun  safe idan yayi  wanka  yana  side  dinsu  anan yake wuni kallo sallah ne kawai ke tayar dashi  tun  muradi baya sauraransa har  yazo ya hakura ya rungumeshi  ko babu komai  zamansa tare dasu  yanzu yasa shaye shayen da  yake sauki da alamun damuwa ce da rashin galihu  ya haifar masa dana shi shaye shayen , shima sadiq babu laifi yana da tsafta sosai   shi  ke share haraban  gidan a madadin mai gadi   hatta motocin muradi shi yake wankewa  bai dauki girman  kai yasanyawa kanshi ba shi yanzu rayuwar  kaninsa ta zamo abar sha'awa agurinsa sai duk sanda muradi yagansa  yana aiki zai haushi da fada "dan me yake aiki alhalin ga mai gadi   duk  lokaci da muradi ya dawo daga aiki  tare yake iske kisna  da sadiq suna hira ko tare da mai gadi  hakan kuwa yana  masa dadi dan haka  yayi tunanin  kisna ta canza dan haka ya fara shiga cikin lamarinsu  ,sai dai duk sanda ya sanyo kanshi cikin hirarsu  sai kisna tayi dip  ta dauke wuta ta daina cewa komai  sosai sadiq ya fahimceta sai dai  bai mata magana ba sai dai kuma  baya jin dadin  yadda takewa dan'uwansa shi duk abinda zata masa muddin zata dinga  wulakanta masa dan'uwansa a banza ne a gurinsa  muradi ya gyarawa  sadiq flat din daya ciki  ya zuba masa komai kusan ma sunfi na bangarensa kyau hadadden kafet aka malala  a falon sannan aka saka masa na tsakiya wato grass carpet ga ƙatuwar tv bango da speaker komai  na part din lemo green ne da ratsin fari a  kwana a tashi babu wuya har Sadiq yayi wata uku  tare dasu komai yana tafiya normal wanda haka ke kara saka zuciyar muradi samun natsuwa dan  har ya  fara jansa zuwa  officer".  a daidai  wannan lokacin zee ta haifi danta namiji  santalele  kyakkyawa mai kama da ubansa sak  sosai dangi sukayi murna da wannan haihuwar a ranar muradi suka  je tare  da kisna wannan shine karo na farko da suka fita tare  lokacin da muradi yaga baby tamkar yayi kuka duk zuciyarsa ta jaguke  saboda tuno danashi ya'yan da yayi   da yanzu nashi sun kai isa tafiya ita kam kisna ko ajikinta ba wai dan ta manta ta kashe ya'yan cikinta ba babu kunya zata kwace yaron Samir ya dakatar daita "karki soma taba min da jiki a sanyaye taja gefe tana kallonsu "Samir kamar na wuce da yaron nan ya shiga raina  "ka wuce dashi mana ai danka ne  ka masa huduba kafin ka wuce da duk sunan da kake so " wasu hawayen farinciki suka cika a  Idanunshi  yayi saurin maidasu tun kafin su zubo "na gode Samir na gode da wannan mutuntaka da ka min  "karka ji komai  muradi ka wuce duk yadda kake tunanin matsayinka a zuciyata  soyayyarmu daga Allah ne yayi wa baby huduba da sunan  badamasi ya d'ago adaidai lokacin daya gama "sunan yaro Muhammadu  badamasi Allah ya raya mana shi yasa makarancin Alqur'ani ne yasa ya zamo irin sheik  Aliyu isa pantami irin sheik lawan Abubakar "ameen suka amsa gabadayansu   kwana  nan  su  biyu a sabiti aka sallamesu  dake  lafiya lau ta haihu   bayan sun dawo gidan ya cika makil da mutane hatta mumy da dady sun zo sanda kisna ta gaishesu mumy ce kawai ta amsa amman dady ko kallonta bai yi ya sake maida kanshi ga jikansa wanda yaji ya shiga ransa matuka kusan tun da akayi haihuwar kofa fita ta budewa kisna saboda kullum tana gidan kwakume da baby  Junior wanda  aunty ummi ce tace a dinga  kiransa da haka .
  da zarar ya Samir ya ga kisna  rike da baby babu kunya  zai  kwace yace "kinsan  kina so me yasa  kika kashe naki ?"na rantse da girman Allah na sake ganin kin taba min d'a sai naci ubanki la'ada waje wani kallon rainin Sense take masa hakan bai hana idan ta shigo ta gansa ta d'aukeshi "ranar suna muradi ya kashe kudi kamar hauka komai na baby da zee shi yayi duk wanda yaji sunan baby sai yace an kyauta da'akayiwa ya badamasi kara ,walima na musamman muradi ya shirya wa abokansu a white place dake nan cikin gra , suna zaune a kofar gidan akan fararen kujeru dasu jahid Samir ne kawai baya cikinsu ya shiga cikin gida suna hirar suna duban masu aikin gyaran sa da raguna guda biyu "wai kai bazakayi wani abu akan matsalarka ba haka zaka zauna kana kuntata rayuwarka ?"me zanyi jahid da wuce hakuri da addu'a kuma kullum cikinsa nake fatan dai Allah ya kawo min sauki "malam ka bude idanuka sosai ya kake yi kamar baka san duniya ba kota karfi ne ka dinga kusantarta inji cewar habib "idan tayi ciki ta cire ko ?ni kuma na yita hasara ya'yana a'a ta sha zamanta itama ai tana jin jiki dan ba itace bace" .

"ta dade bata zubar ba daka zauna kana takure rayuwarka kai ba mata ka iya bi ba ai gara kayi abinda nace idan taje ta karar da ƴaƴanta ai kanta ta cuta kai ba sai ka qara wani auren ba kuma ka haihu ka barta da mugun halinta "dan Allah ka saki jiki ka kwashi gara ya k'arasa maganar yana kwashewa da dariya tunda suka fara maganar muradi yaji yanayinsa ya dan sauya dan sam shi ya dade da cire batun wani sex a rayuwarsa ko jiya sanda ya shigo gidan da daddare ya lura da yadda kisna ke faman juyi akan kujera tana mika ga plet din abinci a gabanta da alamun abinci ta gama ci kallo daya yayi mata ya fahimci ba komai take bukata sai sex Amman dan mugun hali irin nata take tauye kanta suna cikin tautaunawa sai ga afra ita da wata kawarta sun karyo kwanar unguwar da fari bai gane ko su waye ba sai da suka yo kusa dasu saboda lalacewar datayi tamkar ba afra ba suka shiga gidan take gaban muradi ya yanke ya fadi ga afra tazo ga kisna na ciki ai suna shiga da kisna suka fara arba cikin wata dakakkiyar shadda pich colour mai shegen kyau sai kyalli take ai kisna na ganinta ta bar abinda take ta kwasa da gudu ta rungumeta "aunty afra nah oyoyo "afra ta shafa bayanta tana cewa "baby nayi fushi ko ki nemi?" Kika sa ina ta tunanin ashe haka duniya take "wallahi aunty afra kina raina kullum dake nake kwana dake nake tashi gashi kona kira layinki baya zuwa ya kwana biyu ?"lafiya wayata ce ta samu matsala ga tashin hankali kawai na tattara na ajiyeta "shiyasa amman Dan Allah kiyi kokari ki gyara "inshallahu zan gyara ko dan saboda baby nah ya labari? Kisna tace "akwaisu lodi lodi na tara miki suka sa dariya sannan ta kalli matar dake gefen aunty afra tace "ina yini aunty ?"lafiya lau ya taro alhamdulillah "mu shiga ciki suka nufi part din zee nan hira ta barke sam cikinsu babu wanda ya nunawa afra kyama daga mufeeda har zahra da zee kowa ya sake daita bayan wani lokaci kisna da afra suka samu kebewa " wai aunty afra meye gaskiyar lamari abinda muradi ya fada a wancan ranar ?" karye me ne duk abinda ya fada " to me yasa baki ƙaryata ba a sanda yake maganar ?" ina Ni in Kare kaina mu da muke cikin tsaka mai wuya ai na rantse da girman Allah sai muradi yasan ya taboni sai yasan ya qulla min sharri zan nuna masa nafishi iya wasan "ki barshi kawai aunty afra ni zanji da komai banason wani abu ya sake faruwa dake saboda ina son naga kin koma gidan ya badamasi ki karasa rayuwarki bana son ki fita cikin family din mu "dawowata da wuya kisna har yanzu bana gaban yayanki duk yadda dady ke fama dashi akan ya mayar dani yaki tayi mgnr kmr zatayi kuka "karki damu inshallahu zaki dawo "ya labarin musa kuwa kuna tare kin hakura dashi ?"ina wannan soyayyar ai daga Allah ne ina mugun son dan yarbawan nan tamkar raina sai dai gurin wata uku kenan bana jinsa kuma jikina na bani ba lafiya ba "okay zan bincika miki duk yadda ake ciki zaki ji ai da dai wannan number kike amfani ?"kisna ta gyada mata a nan suka tsaida maganarsu suka mike suka shiga cikin jama'a anyi taron suna lafiya sai muce Allah raya Muhammadu badamasi ".

*****

A wata safiyar asabar tun safe kisna ta tashi ta fara soye soye har ta gama sannan ta dafa shayi wanda ji kayan hadi over ta zuba a flask saboɗa sadiq musamman komai dan sadiq take yi saboda yana yaba mata sosai tana tsaye tana shirya dinnng table  sai ga muradi  kamar an jihoshi riga ce shirt a jikinsa ta motsa jiki sai wando three quater kanshi cike da suma sai dai daga bayan keyarsa an aske rabi wato dai askin apro gashin sai kyalli yake koda yake daman shi maaboci kula da gashin kansa ne kamar danshi aka haliccnsa , ya tsura mata ido saboda ganinta daga ita sai rigar bacci iya gwiwa suna hada ido gabanta ya yanke ya  fadi  saboda ganin irin shu'umin kallon da yake aiko mata dashi dauke kanta tayi shi kuma ya fada  kan kujera yana cewa "washhhhh sannan ya cigaba da magana a natse  "ki daina tsayawa a falo haka kin dai san yanzu bamu kadai bane a gidan " ya dan saci kallonta  tana cigaba da abinda take bata ce komai ba ganin haka yace  "hado break din sadiq na kai masa tayi saurin cewa "a'a zai shigo ai yayi break anan muradi ya sauke wani sanyayyiyar ajiyar zuciya jin dadi sai dai tana bashi mamaki  zai ga inda ba'a son kani ace ana son yaya , mikewa yayi ya  shiga d'akinsa yayi wanka ya sauya  wasu kayan  ya fito  alokacin da tuni sadiq ya shigo falon  yana zaune tare da kisna  yana kwasar girkin kisna mara daɗi  ya d'ago ya kalli muradi dake shirin fita yace  "dan'uwa kazo kaci abinci mana  bai kai ga cewa a'a ba kisna tayi saurin cewa   "a'a nifa  ban yi girki dan shi ba kai dai kaci idan kuma bazaka ci ba ka ajiye min  kayana na zubar gbdy sukayi shiru suna dubanta  muradi ya tabe baki sannan ya karaso dinnig table din  ya dauki arish kwaya daya ya kai baki ai da sauri  ya furzar yana kallon sadiq "yanzu kai wannan abinci kake ci ?"sadiq yayi saurin take masa kafa yana cewa," dadi kou ai kaf Nigeria babu macen da tafi kanwata iya girki  kai dai ka zauna ba dan halika ba kaci , kanwata kiyi hakuri yaci ko kadan ne  ",no bafa zan bari ba"  yadda ta hade rai a lokacin datayi  maganar ya kusan sa  muradi dariya sai dai ya hadiye yana girgiza kai kawai

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login