Showing 300001 words to 303000 words out of 495987 words
Chapter 101 - Cutar Kai Book Complete Hausa Novels by Aysha Bagudo.txt
ta zaunar daita a bakin gado tana kuka mumy tace "mamana fada min abinda kike so nayi miki ki hakura ki rungume auren muradi ? Kisna tayi shiru taki yin magana illa shesheka" me za'a bata anan duniya da wuce a aura mata musa suje suyi rayuwarsu muddin rai ".
"meye ban miki ba a rayuwa tun kina ciki nake wahala dake har zuwa haihuwarki dan inganta rayuwarki nayi miki komai tunda nayi silar zuwanki duniya nima a karo na farko kiyi min alfarma". mumy ta karashe maganar da kyar tana jan numfashi kisna ta d'ago kanta hawaye na sake zuba mata ta tsurawa mumy idanu kafin daga bisani tace "mumy ke uwace kuma nasan kin min komai a rayuwa amman nasan kin san yadda tasirin soyayya yake a zuciyar dan adam ?mumy tace "kwarai da gaske kuwa nasani sai dai ita kanta soyayyar zai fi kyau ka ajiye a muhallin daya dace ba kowa zaka iya sadaukarwa da zuciyarka ba , kisna ta rike hannunwan mahaifiyarta cikin nata tana wani irin kuka yayinda jikinta ke karkarwa "dan Allah mumy na rokeki ki min rai ki taimakeni ki fadawa dady cewar ya bar zance aurena da muradi saboda bana sonshi ...." da sauri ta mumy ta d'ago ta tsura mata ido tana kallonta tare zare hannunwata dake rike cikin nata "Wallahi mumy da ina sonshi koda cikin cokali ne zan hakura na auresa amman banason shi kwata kwata idan ma na ganshi ji nake kamar na mutu ......."
mumy tace"subhanallahi Kisna ta goge hawayenta da bayan hannunta kana ta cigaba da magana cikin kuka "muddin kina bukatar ganinsa a raye ku janye batun auren nan dan komai zai iya faruwa "... mumy ta sauke ajiyar zuciya a daidai lokacin da aunty ummi ta shigo dakin bakinta dauke da sallama "Assalamu alaikum "
"Waalaikum sallam mumy ta amsa mata a can kasan makoshi tare da cewa "gara da kika zo ki ummi tayani shawo kan wannan yarinyar na rasa abinda ke damun kisna ana gabas tana yamma " aunty ummi ta zauna tana huci ita kuma kisna ta cigaba da rera kukanta mai ban tausayi qirjinta na wani irin zafi mumy ta bita da kallo tana share kwalla wani abu na takare mata a qirji adalilin kalaman kisna "babu abinda zance akan yaron nan musa Ummi sai dai nace ubangiji Allah yayi min sakayya akanshi saboda ya cuceni ya lalata min rayuwar yarinyata " tayi shiru tare da sauke numfashi gaba-daya mumy ta nemi natsuwarta ta rasa ji take kamar zuciyarta zata buga ganin rarrashin da ake mata ma sake tunzura zuciyarta yake tayi tunanin sauyashi zuwa wani sabon hakuri ta hanyar rusuna mata dan haka ta fara magana cikin sigar rarrashi "kisna kiyi hakuri ki rungumi muradi a matsayin mijinki , muradi zabin mahaifinki ne kuma zabinmu ne gaba-daya ba zaki taba yin danasanin ba idan kika auresa , zai kyautata rayuwarki ,kiyi hakuri karki bari wannan damar ta subuce miki wallahi idan kika rasa wannan damar har abada kisna bazaki samu kamarsa ba mumy ta karasa maganar tana kuka tare da zubewa kasa a gaban kisna ta rike kafafuwanta " ni mahaifiyarki ce gani a gabanki na durkusa miki bisa gwiwowina dana haifeki dasu ina neman alfarmaki a matsayinki na diyar cikina ki amince da auren nan zakiyi alfahari dashi wallahi bazaki ta'be ba muddin kika mana biyyaya zaki ga haske a rayuwarki , kisna ta sake rushewa da wani gigitaccen kuka tare da tura kanta a tsinyar cinyoyinta tana kuka ,aunty ummi tayi saurin durkusawa ta kamo mumy tana kuka amman ina mumy taki mikewa tsaye so take taji abinda kisna zata fada ,zuciyarta zata saduda ko kuwa zata wulakantata akan son zuciyarta ? Kuka aunty ummi take sosai kukan da bata taba yin irinsa ba a tsawon rayuwarta , kuka mai cin zuciya domin bata taɓa haduwa da abun tausayi ba a cikin duniyarta irin mahaifiyarta, ganin abun take kamar a mafarki " wai mumy ce durkushe tana kuka tana rokon kisna akan wani da nmj , kuka take sosai ta juya bayanta inda kisna ke rakube ta soma dukan bayan kisna a gigice "haba kisna dan me zaki zabi farinciki nmj akan na mahaifiyarki kalli kiga mahaifiyarki a durkushe a gabanki tana kuka tana rokonki kisna sautinta ya hankarar da muradi cikin tsananin tashin hankali ya nufi hanyar dakin har zai shiga sai kuma ya fasa ya fito haraban gidan ya nufi jikin window dakin ya tsaya take qirjinsa yayi wani irin bugawa sakamakon ganin mumy durkushe a gaban kisna tana kuka yaji gaba-daya duniya ta tsaya masa shi kansa idan yace yana son rayuwa da kisna yayiwa kanshi karya bazai dai iya musawa dady bane sannan auren shi zai sake kwantarwa da mumy hankali kamar ya juya ya bar gurin dan kaucewa ganin bakinciki sai ya tsinci kansa da kasa daga kafafunsa dan haka ya cigaba da tsayuwa "zafa kiyi nadama abinda kika aikatawa kisna zakiyi dakinsani a lokacin danasanin bazai miki amfani ba ina tausayawa ranar da hakin mumy zai bibiyeki ba'a nuna kiyayya ƙarara ga bawa domin baki san me gobe zai haifar ba cikin kuka aunty ummi ta sake yowa kan mumy "dan Allah mumy kiyi hakuri ki tashi ki daina kuka kada zuciyarki ta buga ki tafi ki barmu cikin tashin hankali , "hakika in haka ta faru nima bazan zauna ba mutuwa zanyi don Allah mumy kiyi hakuri ", ke kuma kinyi hasarar rayuwa wallahi , nan gaba sai kinyi da kin sani dan iyaye sun fi karfin haka "ki barni haka ummi har sai naji abinda kisna ta fada zata auri muradi ta zauna lafiya dashi ko har yanzu tana kan bakanta ?" tsawon lokaci mumy na durkushe a gaban kisna amman kisna taki saduda bare ta bude baki tace ta hakura da musa mumy ta sake rushewa da wani sabon kuka don a ganinta shine ya kamaceta shima muradi hawaye yake zubarwa zuciyarsa na quna sai da mumy tayi kuka mai isarta sannan tayi shiru, tunaninta yayi nisa cikin tunowa kanta mafuta ,bazata iya bari a cuci rayuwar marayan Allah ba ɗan da shi kadai ya rage mata a duk fadin duniya tunda zuciyar kisna taki saukowa tana kan bakanta na kin aurensa gara kawai a hakura kada taje ta kashe dan mutane a banza tunda gashi ta furta hakan a zahiri ta mike cikin zafin nama ta juya ta fice itama aunty ummi na ganin haka ta mike ta fita kisna ta bi kofar da suka fita da kallo batare da tace uffan ba dan kamar an kulle mata bakinta illa dai siyayar da hawayen da take ilahirin zuciyarta a kuntace ,muradi ya dade tsaye yana zubar da hawaye sannan ya juyawa window baya yana taku a hankali yana tunanin aibunsa da yasa kisna taki amsarsa a matsayin miji inda mata bilaadadin suke kuka akanshi ga afra macen da kaf family Alhaji lukman suke ji daita a kyau da izza da komai amman yau an wayi gari tana binsa tana kuka tana rokonsa akan ya sota kullum ya bude wayarsa sai yaci karo da sakonninta bilaadadin na yadda ta makance akansa "bazai ce hakin mata ke bibiyarsa yasa kisna taki shi saboda shi yasan bai yaudari diyar kowa ba tun tasowarsa bai taba tsayawa da wata mace da sunan soyayya ba shi dai yasan zai yi aure idan lokacin yayi jiki a sanyaye ya nufi dakinsu kansa na masa wani irin ciwo ya fada kan katifa tare da runtse Idanunshi ....."
har yamma kisna na kunshe a daki tana kuka idanuwanta sun sake jemewa zee ta shigo dakin ita da kawarta naima da wasu kaya a hannunta dan ita tun da'aka ce aure a satin ta soma shirinta cikin tsananin farinciki zee tace "a'a hajiya kisna anan kan sana'ar ? Kisna tayi mata banza tamkar ba da ita take ba "wai meke damunta ne haka duk tabi ta lalace inji cewar naima "barta kawai naima damuwa tasanyawa ranta wai aure za'a hadata da ya Ali shikenan ta damu rayuwarta kan wani can banza wai shi Musa "wani Musa kenan ?"na gidan olegele mana dan yaron nan mai kama da (tana) naima tayi saurin zaro ido tana zama kusa da kisna ta riko hannunta "haba kisna me zaki da wannan tana ?kisna ta d'ago tana zabga mata harara.
"tana mana dan anyi magana kina hararar mutane "meye marabansa da tana ? "Allah ya baki giwa mai zaki yi da tana ?"wallahi ki zabi Giwa ki bar tana dan wannan tana babu abinda zai miki ?" Kisna ta mike a fusace tana cewa "ubanki ne tana ba Musa ba kuma wallahi kika sake ce masa tana sai muyi barauba dake kafin ki bar gidan nan shegiya yar iskar ki tsaya matsayinki bana son shishigi da neman suna ta fito tana zagin naima "ba tana ba ko maciji ne haka nake son shi kuma babu wanda ya isa ya hanani aurensa ta karasa maganar tana ihu kamar wata mahaukaciya gaba-daya mutanen gidan suka fito har mumy da dady da uban gayya muradi kowa yayi tsuru tsuru yana kallonta tana surfa maseefa ta inda take shiga bata nan take fita ba "banason aliyu na fada na sake fada banason shi "kiyiwa mutane shiru da wannan haukan naki ," kisani ko mutuwa kika yi wallahi sai na daura aurenki da Aliyu karewar kiyayya kenan dan haka kiyiwa mutane shiru bana son jin komai daga bakinki "i have to talk dady ,I really has to talk before everything could mess up with me dole na bayyana rashin son da nake masa musa nake so, i say it in from of him and everyone "
"ni Kuma bazan aura miki wannan yaron ba bare na cigaba da ganinku kuna rayuwa tare , ke din diyar cikina ce ,kuma dole kibi umarnina kuma dolenki ki zauna da Aliyu ......"
Suna cikin wannan halin suka ji sautin muryar mumy "dady dan girman Allah " kayi hakuri ka hakura da wannan hadin saboda kasan halin kisna bana ji ta muradi ko wuta mukace ya fada zai fada saboda shi dan albarka ne ada can naci burin kisna bazata auri wannan yaron ba amman a yanzu na yarda ta aureshi "
"Kin yarda ta aureshi mumy ? Samir ya fada yana kokarin matsowa kusa da mumy "eh na yarda Samir tace ya turo iyayensa kawai a daura musu aure sai dai akwai sharadi muddin ta aureshi wallahi babu ni babu ita har karshen rayuwarta ciwo mutuwa duk wani abu da zai sameta karta tako kafarta zuwa gidan nan babu ni babu ita har abada kuma babu ku babu ita duk wanda ya taimaka mata a rayuwa ban yafe ba dady ya numfasa yana cewa "ni kuma muddin ni ne mahaifinta bata da miji sai aliyu magana ta kare lokaci kawai muke jira karki dawo da hannun agogo baya uwar marayu kowa yaje yayi abinda ke gabansa daya bayan daya suka juya kowa ya kama gabansa dady cikin sanyi jiki ya juya yabi bayan mumy saboda lura da yayi ranta a bace yake da maganarsa ta dai ƙasa mutsa masa ne , koda ya shiga dakin kuka ya same tana yi "kiyi hakuri da hukuncina uwar marayu ban haɗa wannan auren dan musgunawa rayuwar Aliyu ba ko cutarwa garesa nayi haka kafin komai ya rincabe mana kema nasan kina son wannan hadin kina dai jin haushin yadda kisna ke nuna tsanarsa a fili ne ,salaha you really has to carry over the tears in my eyes rarrashinta yayi sosai da kyar ya samu ta saki ranta ta dawo daidai yayi Murmushin jin dadi daga gobe za'a fara shirin buki duk da ba wani event za'a yi ba diner ne kawai shima dan Samir ya bukata ne "Allah ya rufa asiri yasa auren ya zamo silar kwamciyar hankalinm da muke fata ."dady ya numfasa tare cewa ameen ..
Da daddare Dady na zaune a dakinsa ya rafka tagumi yana tunani kisna ta shigo cike da sanyi jiki ta zauna a gabansa bai kyalleta ba ya juyar da fuskarsa wani gefe zuciyarsa na zafi a duk sanda ya tuna rayuwar da suke ciki lamarin na kona masa rai "wai yau shine yana fada diyar cikinsa na fada akan wani namiji "dady ta kira sunansa cikin raunanniyar muryarta mai shiga jiki "uhmmmm meye kiyi maganarki ina jinki ? " yayi maganar batare daya kalleta ba "dan Allah dady ka kalleni ina son yin magana da kai "kiyi maganarki ba dole sai na kalleki ba "tayi shiru tana tunani maganar da zata fito daga cikin bakinta yayinda dakin ya dauki shiru yadda bata yi magana ba haka shima bai yi magana ba illa iskar da yake furzarwa qirjinsa na dokawa da matsanancin karfi saboda zuciyarsa cike take da tsoro abinda ya kawota tsawon minti goma sannan ta cigaba da magana cikin sanyi murya "dady ka min alfarma ka barni naga musa yau ina son zanyi magana dashi mai mahimmanci daga nan shinkenan na hakura kuma zan yarda da hukuncinka amman rashin ganinsa wani gagarumin maseefa ne atare dani yayi mata banza tamkar badashi take magana ba "wallahi nayi maka alkwari zan bi umarninka "bafa zan yarda da wannan banzar uzurin naki ba zan aura miki Aliyu ina jiran naga abinda zai faru bayan aure maza ki tashi ki bar min daki shasha kawai simi simi ta mike ta fito daga dakin tana zance zuci "yadda kuka rusa min tsari kusani nima zan rusa muku tsari zan kwantar da hankalina ayi biki amman abinda zai biyo bayansa sai ya tarwasa zuciyar kowa " tana shiga daki ta fada toilet ta kira number musa sun dade a cikin bayi suna waya tana masa kuka shi kuma yana rarrashinta da daukar mata alkwarin baza'a yi auren ba ..."
Tun ranar laraba aka fara gyara gidansu mumy da gidan da kisna zata zauna batare da saninta ba ,daya daga cikin gidan je dady ne dake cikin gra gida biyu ne a hade sai dai get din kowane bangare daban yake , ba zaka ga wanda ya shiga bangaren Samir ba haka zalika bazaka wanda ya shiga bangaren muradi ba dady ya kashe kudi sosai tamkar bai san ciwonsu ba duk da muradi yaso ace ya barsu sunyi komai a aljihunsa amman yaki ."
Washegari mumy na zaune a ɗakinta sai ga madu da wasu abokansa su uku suna shigowa da akwatunan lefe suka ajiye suka sake fita tun tana kirgawa har ta dawo ta daina akwatuna kashi da kashi har kusan set bakwai kowanne set kalarsa da daban sai dai duk iri desing daya ne babu wani bambanci sai na colours take ta fahimta wato akwanan auren kisna ne tana tsaka da kallon akwatinan muradi ya shigo sanye da bakaken kaya da facin cap baki hatta takalmin ƙafarsa baki ne kasancewarsa fari sai kayan suka amshesa fiyye da duk kayan daya saba sakawa sai kamshi yake zubawa fuskarsa ta sake fitowa sosai saboda gyaran fuskar da yayi , ya karaso har gaban mumy ya durkusa yana cire facing cap dinsa cike da girmamawa ya gaisheta "mumy anyi lafiya ?"lafiya lau muradina ya fama da hayaniya ?tayi maganar tana daura hannunta a kanshi ,murmushi yayi sannan yace "alhamdullahi "wadan nan kayan fa "kayan kisna ne " ya fada yana mikewa tare da zama akan kujera idanu ta tsura masa for two second tana masa kallo mai cike da tsantsar mamaki shima ita yake kallo hawaye ne suka fara turereniyar zubowa akan fuskarta yayi saurin mikewa ya dawo gabanta ya kamo hannuwanta duk biyu "no mumy farinciki ya kamata kiyi ba kuka ba wallahi bana son ganin hawayenki yana daga min hankali ganinsu yafi kiyayyar kisna gareni ya kai hannu yana goge mata hawayen sannan ya mikar daita tsaye yana kallonta "bani da uwar da zan kaiwa kayan bare wasu dangin da zasu kawo dole kice uwar ango hannunki suka fi dacewa suzo kai tsaye saboda kece uwata kece komai na rayuwata sai ki nemowa amarya mamanta muje kiga kayan muradinki abinda bai yi ba a karo take fuskar mumy ta bayyana murmushi da tsananin farinciki "wai ma a yaushe ka soma hada kayan lefe ban sani ba ?"jiya zuwa yau ne fa mumy ya karasa maganar yana Murmushin karfin hali cike da shagwaba ya zaunar daita akan kujerar daya tashi "ki zauna a nan ki huta zan bude miki akwatin daya bayan daya yana gama fadar haka ya karasa ya soma budewa shiru mumy tayi tana jinjina kai murmushi ya subuce mata a lokacin daya bude akwatin kayan bacci ganin duk ya zabo hadaddun kayan zamani masu matukar kyau da daukar hankali "da kanka ka zabo wadan kayan bacci ? sai lokaci ya fahimci kuskuren da yayi na bude su agaban mumy duk ya rude cikin saurin murya yace "no !no "ta kalleshi tace "no ? Yayi saurin gyada mata kai alamun "eh " batare da yace mata komai ba da yamma sai ga Samir danashi shima kusan