Showing 438001 words to 441000 words out of 495987 words

Chapter 147 - Cutar Kai Book Complete Hausa Novels by Aysha Bagudo.txt

abun arziki zai zama na tsiya  yanzu meye laifina daga fadar gaskiya ?
yayi mata banza  yana hura hanci  a ransa yace "haka ne abun arziki   ?
Kamar taji abinda yace  a ransa tace ""tam  shikenan nayi shiru bari  ma kagani na kama gabana  daman a shiryena nake mufeeda zahra kun tashi mu wuce tare  ko kuwa  anan zan barku ?, suka kwashe da dariya tare da  mikewa  tsaye "yau dai an ganku a rana akan kisna sai kiyi taka tsantsan aunty ummi ki fara neman gidin zama agurin uwargida sarautar mata inji cewar zahra ,suka sa dariya  gbdy  ban da muradi dake ciccin magani aunty ummi  tace "ai kuwa naga alama  sai na bige da neman gidin zama  suka  nufi d'akin  mumy dan yi mata  sallama  ."

kisna dake tsaye ajikin kofar dakin tayi  kasa  tana   manna  bayanta da jikin kofar ,wani  murmushin  farinciki ya bayyana akan fuskarta lallai  sai  yanzu  ta tabbatar   da  muradi  ya  soma  sonta ko babu yawa  ,sai  dai hakan bazai  sa ta fito  su hadu ba  sai  tagama jinyar zuciyarta  ta mike da kyar ta koma ta kwanta amman har lokacin tana jin bugun zuciyarta akan mijinta dan soyayyarsa ta zame mata abincin ruhinta , tunaninsa ta shiga yi yayinda sautin maganarsa dake tashi a hankali ke shiga kunneta kadan kadan  ,yana  nan zaune tare da Samir  da zee  su aunty ummi  suka fito "to mu zamu   wuce  sai wani lokaci a gaishe da  amarya  ko kallonsu  bai yi  ba  bare ya amsa  suka fita suna masa dariya ."

Ita kuwa nawal jin shiru har kusan uku da wasu mintuna bata ji motsinsa  ba ,  ta fito daga part dinta ta tura kofar falonsa ta shiga da sallama taga baya nan wani faduwar gaba taji,  a hankali ta nufi kofar bedroom dinsa  data gani tayi knowcking a hankali saboda tasan halinsa shi mutun ne mara son hayaniya yafi son duk abinda za'a yi ayi shi a natse ,jin shiru ta sake yin knowcking amman still shiru babu motsin komai alamun ma babu wani halitta a cikin dakin  jiki a sanyaye ta murd'a kofar dakin  dan gaba-daya a tsorace take dashi ta shiga dakin kallon dakin ta shiga yi zuciyarta na rawa babu kowa acikinsa kallon dakin ta cigaba yi komai a kimtse very niet sai kamshi  turarukansa ke tashi , a hankali ta karasa bakin gadonsa tana kallon farin bedshit din dake shimfide tana tunanin inda ya tafi batare daya nemeta ba , ta zauna tare da kwanciya akan katifa ta janyo pillonsa ta rungume  ajikinta gam  tana jin tamkar shi ta rungume a hankali ta fara rera kuka "Please my norr karka guji rayuwata wallahi ba laifi bane yaudarata akayi  ,rayuwa babu kai numfashina zai tsaya , kuka take sosai can ta zabura ta mike zaune tana sauke numfashi da kyar idanunta na cigaba da tsiyayar ruwan hawaye hannu na rawa ta kai ta dauki frem din hoton kisna ta tsira mata ido tana murmushi ta dauki hoton cikin wasu kananan kaya rigar da kadan ta wuce cibiyarta wanda kallo daya namiji zai mata yaji sha'awarta ta tsarga masa tana kallo hawayenta na dinga  akan hoton a hankali  ta jin wani abu na taso mata , bata da tantama kishin mijinta  ne ya yunkuro mata  ta lumshe idanunta  tana jin zafi a ranta "why norr me yasa zaka ajiye hoton nan  a nan alhalin kasan dole zan ji babu dadi idan nagani ?,  ta sauko daga saman gadon tana jin kamar ta saki frem din akan tayis ya tarwatse tun kafin nata zuciyar ya samu matsala sai kuma tayi wani tunani ta fasa  ,ta mayar dashi inda yake ta fito da gudu ta fada ɗakinta tana kuka tamkar ranta zai fita "me yasa na yarda na basu kaina gashi na jama kaina tashin hankali agurin mijina ?, wayyyohhly Allah ka taimakeni kada na samu matsala da mijina  .."

har  sanda  karfe hudu ta buga muradi da Samir  suna  nan suna hira  sannan  suka  fita tare   zuwa massalaci ,bai dawo gidan  mumy ba   gida ya wuce  dicret  zuciyarsa na  tuttukin bakincikin yana shigowa  parlour ya iske  nawal da wasu mutane  guda  biyu zaune  a kasa ita kuma tana zaune akan kujera bai   tsaya  bi   ta  kansu ba  ya shige d'aki ya zauna  shiru  can ya mike ya  zare jallabiyar jikinsa da agogon dake daure da tsintsiyar hannunsa   ya  shiga  bayi ,  cikin natsuwa nawal ta turo kofar dakin ta shigo gabanta na faduwa , ta hadiye wani abu data ji ya tsaya mata a makoshi jin saukar ruwa a bayi ta fahimci wanka yake tana kokarin juyawa taji an bude kofar bathroom  ya fito daure da white  towel sabo a kugunsa,  murdadden jikinsa sai sheki suke zubawa ruwan wanka na yawo ajikinsa ga kwantaccen suma qirjinsa da yayi kasa har kasan mararsa  gabanta na faduwa ta fuskancesa  idanunta ya shiga cikin nashi saurin dauke Idanunshi yayi kamar bai ganta ba , ganin yadda yayi  yasa  gbdy ilahirin jikinta  ya dauki rawa kamar  mazari tare da juya masa baya dan ya samu damar kimtsa wa  ,ta cikin mirror  ya  tsurawa bayanta  ido yana jan tsaki "aikin  banza kawai ko kunyar uwar me take ji ? yayi maganar a kasan zuciyarsa ."

turare  ya  ɗauka ya fesa sannan  ya  karasa inda kayansa suke  ya dauki kaya marasa  nauyi  ya saka duk  abinda yake tana tsaye  batare data juyo ba  gabanta na cigaba da faduwa   ya raɓa  ta    gefenta ya fito  zuwa parlour  bátare daya ce mata komai ba tsayuwa ta  cigaba da yi kamar wacce  aka da sata  cikin tsananin  tashin hankali wasu hawaye suka yi nasarar  zubo mata tana kokarin  gogesu ya sake shigowa a dakin a zuciye ya karaso gabanta ya tsaya  yana cewa  "ke ....wadan can  mutane  dake  falo su waye  ?, muryarta   cike da  in Ina tace "ma ...masu aiki ne "
"Masu aiki ya maimata yana mata kallon sama da kasa ?  ta gyada masa kai alamun "eh!  "to bana  bukatarsu acikin  gidan  nan dan haka  maza a sallamesu su kama gabansu  yayi  maganar yana furzar  da numfashi tare da juyawa ya bar daki jikinta na rawa ta fita zuwa falon ta sallamesu ."

ta zauna tana fuskantar shi  tana sake danne kukanta  gbdy yaki kallon inda  take  illa remut daya  dauka ya kunna tv ta  rasa abinda ke mata dadi  a rayuwarta a dan fusace yace "wai meye haka  ne da  zaki sakani gaba da sheshekan  kuka ? "wani irin bugu  gabanta yayi da karfi  ,take  tashiga kokuwa da numfashinta dake  barazanar  daukewa  tana kokarin tsaida sheshekan da take ta  durkusa  tare da jan gwiwowinta ta  karasowa gabansa tana kuka " kayi hakuri dan girman  Allah "me kika  min da  kike  bani hakuri  yayi maganar batare daya kalleta ba Idanunshi na kan tv .

ta share hawaye fuskarta " nasan  laifina  shiyasa nake  baka hakuri , wallahi  ban kasance mazinaciya  ba tsautsauyi  ne my  norr kuma nayi ƙoƙarin na fada  maka yadda komai ya faru a can baya sai dai   tsoron  karka  gujeni  yasa nace maka   maza uku sun yaudareni  "kenan karya kika fada min ?, a'a ta furta cikin murya kuka "gara ki fada  min cewar mazan  uku   sun  kusanceki  kafin ni hankalina zai fi dauka , cikin  rawar jiki ta shiga bashi hakuri  akan wancan karyar da kika girba min  "
Jikinta na rawa tace " fada maka komai daya faru bashi da wani amfani sai tarin bakinciki  da damuwa ni  dai ka  yafeni dan Allah ka kuma rufa min asiri nasan kai mai hakuri ne kayi hakuri dan girman Allah ta karasa maganar  tana rungumeshi  ajikinta tare da fashewa da wani sabon kuka ta zagaye weist  dinsa  da duka hannuwanta ko motsi bai yi ba bare tasa rai zai yi magana  sai data sha kukanta sosai sannan ya zareta ajikinsa yana fuskantarta "kace ka yafe min  my norr  yayi mata shiru "zaka ci gaba da zama dani ko kuwa zaka sallameni  dan nasan ganina zai iya haddasa maka komai ?, nan ma shiru  yayi  mata kawai dan idan ransa ya baci baya iya magana ko kadan haka tayita masa magana batare data fada masa dalilin dayasa ta bawa samarinta na baya kanta ba ."

mikewa yayi ya koma d'akinsa  ya dauki hoton kisna   ya tsurawa hoton Idanunshi da suka kada suka ja ya manna hoton a qirjinsa  yana jin wani irin buguwar  zuciya ,bai taba jin yana tsananin sonta ba sai a wannan lokacin ta shiga zuciyarsa sosai "kisna kin  samu kyakkyawan mazauni a  zuciyata da rayuwata  dan Allah ki bani dama  na ganki i love you so much I really miss you ,nayi kewar komai naki , gangar jikina na bukatarki  ,ki taimama ki bari na ganki  ya  kwanta  rungume da hoton bai sake fitowa ba sai washegari shima yana gama abinda zakiyi ya fice  a gidan  ko tsayawa break  bai yi ba  ,bai  dawo  gidan ba sai byn isha'i  ya shige d'akinsa ya kulle ya  kwanta.

nan fa abun duniya ya  damun nawal hankalinta ya daga sosai   Cike da tashin hankali nawal ta dauki wayarta ta soma neman number mumynta tana dauka ta  sakar  mata  kuka , murmushi ne akan  fuskar hajiyarta amman bata san sanda  ya koma zuwa damuwa ba "ya da kuka nawal?tayi maganar tana saka wayar a handsfree " ina missing dinku mumy hajiya Mardi ta kalli mijinta dake zaune kusa daita sannan  ta sakar  masa murmushi kafin tayi magana , nawal taji sautin Muryar mahaifinta "haba dai mamana jiya ne kawai fa  bama tare , ki daure mamana ke din  jaruma ce ban san ki da ragwanta ba "Allah dady kamar na dawo gida nake ji  "ya numfasa kana ya cigaba da magana  "ina kika taba ganin  akai mutun gidan miji shekaranjiya yace kamar ya dawo gida yau  ?, duka kwananki daya ne fa dariya suka saka mata "Allah dady bazaka fahimci halin da nake ciki bane a  kwana dayan da nayi , gbdy na rasa meke damunna "kinga kiyi hakuri aure dan hakuri ne , ki  rike mijinki ki zauna lfy da danginsa kinji idan an  kwana biyu da kaina zanzo na ganki Allah yayi miki albarka  mumy ta mike tana cire wayar a handsfree ta shiga bedroom dinta "ke sai naga masu aiki sun dawo lafiya dai ko "wallahi mumy cewa yayi baya bukata"  ga dan iskan yaro to uwarsa ce zata  miki aikin gidan ?

"kinga  mumy  mu  ajiye maganar  masu  aiki akwai  fa matsala nan ta shiga  korowa mahaifiyarta  komai dake tasan komai sai jan numfashi tayi "kina jina ki kwantar da hankalinki idan Allah ya kai mu gobe ki kira wacce uwar goyon tasa kiyi mata kuka amman karki kuskura ki fada mata komai ,nace kiyi haka ne  dan nasan ita kadai ce wacce zata shawo miki kansa da sauri kafin ita wacece matar tasa ta tare    "kin  kawo shawara  mumy zan yi kokari kiranta gobe yanzu ma dan dare yayi ne da yanzu  zan kirata "ya za'a yi  da masu aiki a sallamesu  ne dan gsky ni bana bukatarsu ? "a'a mumy ki dan barsu zuwa wani sati muga yadda yanayin zai yi idan da hali  sai su dawo idan babu na hakura kwa dinga aiko min da abinci nan suka  shiga wata   hira nawal  har  da dariya byn wani lokaci  sukayi sallama ."

washegari ma kamar jiya da sassafe ya fita ko breakfast bai yi ba  yana  fita ta soma neman layin mumy  bugu biyu mumy ta dauka cikin sanyayyiyar  muryarta tayi  sallama kawai taji ta sanya  mata kuka cike da tashin  hankali tace "nawal  me ya faru ?,mumy ina yini ?,yasu aryan ?suna lafiya meke faruwa nawal kinsa hankalina ya daga "wallahi mumy ina cikin damuwa  ta kare maganar tana sakin kuka "damuwa ubangiji ya rabamu daita " mumy laifi nayiwa muradi ya dauki  fushi dani mai tsanani "subhanallahi to ya isa kukan sannan bana bukatar jin laifin dan mijinki sirrinki ne  inshaallahu zan masa magana ke kuma ki kiyaye abinda zai bata masa rai  kinji Allah yayi maku albarka "ameen mumy Allah ya qara girma suka yi sallama mumy  na katse kiran ta kira muradi tace maza yazo tana son ganinsa cikin kankanin lokaci ya karaso bakinsa dauke da  sallama ya shigo  cikin dakin mumy tana zaune rike da waya ta karba masa sallama a hankali ya karaso ya durkusa har kasa gabanta  "ya gida mumy cikin haɗe fuska mumy ta amsa  yace "mumy lafiya yana  ganki  kamar kina cikin damuwa ? "dole ka gani haka har yaushe akayi daren muradi yau duka kwana biyu datarewar yarinyar nan har ka fara damun rayuwata ? .

naunayen  ajiyar zuciya ya sauke yana runtse Idanunshi "bazan dauki ka wulakanta musu yarinya ba kai baza'a maka laifi kayi hakuri  cikin dadin rai ba sai ka dagawa mutane hankali  ... " mumy ki tsaya ki fahimceni itace tace nayi mata wani abu ....?ban sani ba idan ba ita bace yaushe zan sani sauran kuma idan ka koma gida ka hauta da bala'i wallahi zaka hadu da fushina da baka taba gani ba , mumy ta inda take shiga ba ta nan take fita ba shi kuwa tun da  ta fara magana ya sunkuyar da kanshi kasa bai d'ago ba har sanda ta dasa aya  ..

Shiru ya ɗan  ratsa dakin can muradi ya d'ago ya sake duban mumy sannan yace "kiyi hakuri mumy inshallah komai ya wuce hakan bazai sake faruwa ba duk abinda kike so shi za'a yi  "ka dai ji abinda na fada maka banason jin wani tashin hankali sai zaman lafiya ka tashi ka bani guri "dan girman Allah mumy kiyi hakuri karkiyi fushi dani wallahi na hakura ki yafe min duk ya dawo kalar tausayi sanbna ta saki ranta tana sakar masa murmushi ta shiga yiwa yaronta da  addu'ar zaman lfy  sai lokacin hankalinsa ya kwanta ya mike ya  fito  yana fita mumy ta kira nawal tayi mata fada sannan tace itama ta kiyaye abinda zai dinga motsa masa zuciya dan fushinsa bai da kyau "inshaallahu mumy na gode sosai a gaishe min dasu aryan da   mutan gidan tana ajiye wayar tayi wani tsalle ta fada kan gadonta  ta kwanta lamo can ta mike ta fada bayi tayi wanka ta fito ta sauya wasu kaya zuwa kanana kaya gbdy ta dawo one  babu wani tsari  babu  fasalin ta kira gidansu  tace akawo mata  abinci cikin kankanin  lokaci komai yayi ready karfe  biyar daidai ya shigo gidan ta mike tsaye ta isa kusa dashi cikin sanyi jiki tayi masa sannu da zuwa ya amsa  ya  nufi hanyar d'akinsa ta bishi stil tana sake bashi hakuri babu yadda ya iya haka ya hakura yayi wanka suka dawo parlour tun kafin ya zauna ta kamo hannunsa zuwa dinnig ta bude wata hadadayar   kula sai kyalli take ta zuba masa freidrice dataji kayan hadi   ,abinci kadan yaci dan shi bai damu da abinci mara nauyi ba  ya tashi ya koma daki ta bishi daki tana lallabashi da bashi hakuri ,  ya sanyawa zuciyarsa ya  rungumeta suka cigaba  rayuwarsa  duk wani kulawa nawal  tana yi masa amman hankalinsa  da zuciyarsa sam  basa gareta  suna gurin  kisna gashi ita kuma ta  boye masa  kanta ko yaje gidan baya ganinta  gashi soyayyarta  tattare da matsananciyar sha'awarta ta addabi ruhinsa  duk zuwan da zai yi baya ganinta sai dai yaga yaransa hankalinsa idan yayi dubu to a tashe take   ".

Tun daga lokacin bai kara samun  walwala da sukuni ba har mamakin kansa yake kullum cikin damuwa yake baya wani cin abinci  kirki  gashi kowa  ya  gane halin da yake ciki yanzu  gidan mumy da nawal ita kanta ,sai dai ko sun tambayesa sai  yace musu  babu komai  yanzu haka aiki yake agaban system amman tunaninta ya hanashi aiwatar da komai ,ya ture system din gabansa ya mike ya fara zagaye cikin  d'akinsa  ya dauki lokaci a haka  yana kai kawo sannan '  ya dawo ya zauna a gefen kujerar dake dakin  yana jinjina girman alamarin kisna  duk ilahirin jikinsa sunyi masa mugun sanyi , ahankali ya sake mikewa   ya koma kan gadonsa  ya zauna  yana son ya cigaba da aikinsa  idanushi  suka  sauka akan dan karamin fream dinta dake ajiye akan  bedside  ,ya zuba mata  ido kawai yana kallonta shi kansa ya amince tun ba yanzu ba yana na matukar quanarta   fiyye da komai, Itama kuma    haka take matukar sonsa tamkar rayuwarta kamar yadda ta sha fada masa a cairo ,   " duk duniya byn mahaifiyarsa da mumy  to ita kadai yake ji a gangar jikinsa , soyayyarta ta zarta na sauran matan duniya   'ahankali  ya kai hannunshi ya dauki karamin fream din yana cigaba da kallonta  yayi  matukar  kewarta sosai, yayi kewar komai nata  ,kusan kwana  bakwai  Kenan rabonshi da sanyata acikin kwayar  idanunshi wanda kuma hakan ya faru ne a sanadiyyar zuwan nawal , bancin haka yasan zuwa yanzu da tuni tana makale dashi  tana bashi kulawa ,runtse idanushin yayi sosai Yana jin yadda kaunarta ke sake ratsa zuciya da gangar jikinsa"tsawon lokaci idanunshi na runtse  sannan ya budesu fes yana sake kallon hotonta   tare da  sake jin haushi da takaicin nawal  a ranshi. "

********

Bangaren mumy kuwa bata bar kisna haka ba kullum cikin tsuma diyarta take da kayan mata dana gyaran jiki , yanzu ma tsaye take a bakin kofar ɗakinta tana knowcking daga cikin dakin kisna ta amsa da waye ?,ki bude nice jin muryar mumy yasa ta taso ta bude mumy ta shigo hannuta rike da kula wacce ke dauke da hadin jijibi , naunayen ajiyar zuciya mumy ta sauke ta ajiye kular hannunta ta janyo karamar kujarar ta zauna tana fuskantar kisna dake zaune gbdy jikinta ya sake sauyawa , tayi kyau sosai farinta ya sake fitowa  tamkar wacce take wanka da madara ita kanta mumy kisna tayi mata kyau sosai ,sai dai ta dan rame shima tasan hakan baya rasa nasaba da rashin mijinta, murya a sanyaye tace "ga jijibi nan a

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login