Showing 363001 words to 366000 words out of 495987 words
Chapter 122 - Cutar Kai Book Complete Hausa Novels by Aysha Bagudo.txt
din daya sauka ya dawo gidan, duk da taki yarda ta ra'bi inda yake amman shi idanunsa na kanta , yayi tunanin duniya yadda zai samu hadin kanta ya rasa hankalinta baya kansa dan haka duk wasu hikomomi yayi amman kisna tayi kmr batasan abinda yake nufi ba ranar daya fito mata a mutun dinsa sak , byn yace ta dafa masa tea ta haɗa taki shiga d'akinsa ta ajiye har sai daya gaji ya fito yace "kisna ina shayin ne tun dazu ina jiran ki ? fuskarta a hade tace "gashi yayi murmushi yace" shigo ki kawo min taki "idan zaka zo nan ka dauka kazo dan babu inda zani ya fito da kudi masu yawa kana ta fito mata da joystick dinsa yana kada mata yana kada mata kudi da sauri ta rufe idanunta tana cewa "shegen dan burouba baa so kai ne maye kudi jaki kawai mai siffar alade ni zaka kalla kace zaka bani kudi da wannan shigeyar taliyat taka yar karama ya zaro ido yana kallonta kafin daga baya ya soma takowa zai karaso inda take ta dauki Cup din tea ta saita joystick dinsa zata wurga masa sai kaucewa yayi yana mayar daita cikin wando bancin hk da sai a akanta da gudu ya juya ya shige dakin hjy Hafsah ,a gigice ta mike "lafiya isa "ina fa lafiya a she yarinyar nan mahaukaciya ce ,har ni zata wulakanta daga ina mata wasan ina sonta idan ta gama idda zan aureta shine fa ta hau hauka tubaran tsaki taja "kai yanzu me zakayi da yarinyar da maza sukayita kwakuleta atiti shima mijinta fa makala masa ita akayi ba dan yana so ba ni wallahi kabani kunya ma ta fito bedroom dinta tana kiran kisna "ta karaso ta tsaya "ke daga wasa zaki kawowa dan'uwana hauka "abinda yayi shine hauka kuma wallahi ki fada masa ya sake fito min da wannan shegiyar taliyar tasa zan aikasa lahira "lallai kin cika rantiriya dan'uwan nawa zaki kashe ai kuwa yau zaki bar min gida daman darajansa kika ci "gaskiya aunty ki koreta zatayi hatsarin zama "ai ko bakace bari shi wanda ya ajiyeta yazo "ko bakice ba yau zan bar gidan ta juya ta koma dakinta ".
ai kuwa ranar da daddare da kuka ta samu alhj marwan "dady ka taimakeni ka maidani gida ka bawa dady hakuri na zauna tare dasu "ba yanzu ba kisna mahaifinki ya dauki zafi amman ki dan bani lokaci kuka ta dingayi har da burgima tana rokonsa
babu shiri alhj marwan ya ɗauketa zuwa gidan dady bayan dogon hakuri da Alhaji marwan ya bashi yace "kisna dai 'yata ce ko to na rantse da girman bazata zauna min a gida a nemowa shi wannan dan iskan yaron a daura musu aure a wuce gurin ai dan muce bamu yarda bane yasa ta nace lallai sai shi "daman ai abinda tafi so kenan a aura mata yaron amman inji cewar mumy alhj Marwan yace "yaya ka bari ta kammala iddarta , ai tayi laifi wanda zatayi nadama ko da yake tun yanzu ma ta fara nadama dan itace ma ta damu na dawo daita dady ya mike a fusace" batayi nadama ba za dai tayi tunda taci mutuncimu tace bamu isa ba wallahi sai tayi nadama tunda ni banyiwa iyayena ba amman tace lallai sai ta kunyatani da kyar da Allah da darajan mahaifiyarsa ya yarda ta zauna sai dai yace da sharadin zamanta kafin ta gama iddarta "meye shi sharadin ? Alhj marwa ya tambayesa "gabadaya aikin gidan nan sama da kasa haraban gidan wanke wanke , kai rantakaf komai itace zatayi idan fa taji zata iya zama damu idan bazata iya ba ga hanya nan malo tarara ya nuna mata kofa ......."
*****
Muna saida ingantattun maganin mata masu kyau da nagarta wanda ko da kudinka sai da rabonka tsimi , zumar Mata, gunba, gari insertion,kaza,zakara ,
jigida dadai sauransu.
1.Tsumi Yana saukarwa mace niima Kuma bazataji wuyar jimai ba.
2. Zuma Tana taimakawa wurin Jin sha'awa Kuma itama Tana taimakawa wurin jindadin jima'i.
3.insertion( Dan matsi) daban dabanne akwai Wanda ke matse mace kuma yake saukar da ruwan ni'ima sannan akwai na mallaka , idan ana bukata a tuntubi wannan number
234 815 945 0159..
Mmm Sudais
[7/19, 5:33 PM] +234 803 631 5951: 💗💗💗💗💗💗
CUTAR DA KAI
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
Page 53
~TRUE LIFE STORY~
*PAID BOOK*
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
bismillahirrahmanirrahim
"Wannan littafin na kudi ne ,mai bukata karanta shi zai tura 500 ta wannan account number din 1438775094 Aishat Abdullahi Access bank ,Idan an tura sai a turawa wannan number alert +234 803 238 4602 domin tabbatar da an tura , ko wannan number 08059623096 Idan Kuma vtu za'ayi sai a tura ta wannan number 08059623096 ,kada ayi vtu a number MTN sannan kada a Kira number mtn ba'a kira dashi only chart ne . "domin sauraran littafaina sababbi da tsofaffi za'a iya tuntu'bar Channel dina ta Hausa bakwai,sannan muna bada sarin Lagos lace da kamfala ,Lagos rapa , jaka da takalma, getzner na cotonou da chiganvy, voil lace Swiss lace duk akan farashi mai sauki ,ga mai bukatar siyan ɗaya ko sari yayi magana ta wannan number 08059623096.
......." Idanunshi kawai ya tsura mata yana kallonta "bai san har sai yaushe zata shiga hankalinta tayi ilimin ta natsu akan rayuwa ba mace kamar shedaniya ,gabadaya rayuwarta na cike da tarin mamaki sannan cike da iskancin kala kala ,a ganinsa da tasan dukkanin rayuwar ɗan Adam rubutaccen al'amari ne daga Allah da wata kila bata dinga 'batawa kanta lokaci ba gurin matsa masa akan saki ." ya kusan minti goma yana zaune yana kallonta zuciyarsa cunkushe da bakinciki , itama har lokacin kwayar idanunta na kanshi cike da zafin zuciya ta cigaba da cewa " a yanzu na qara jin tsanarka fiyye da sauran lokutan baya saboda bayan karyar daka saba min ta zaka sakeni har da kazafi babu kunyar Allah bare ta mutanen da suka taimakawa rayuwarka ka girma ka zamo mutun amman ka iya bude baki a gabansu kana zayyano karya akan aunty afra koda yake ba tun yau nasan irin tsanar dakayi mata ba , zaka iya fadan kowani irin sharri akanta sai da kasani aunty afra bata da laifi akan cire jarababbun ya'yanka da nayi idan akwai mai laifi nice nan, haka kawai bataji ba bata gani ba kaja an sake ta ai wallahi sai Allah yayi mata mummunar sakawa akanka "ta karasa maganar tana jan tsaki cikin tsananin fushi ".
Tsaki yaja shima sannan a hankali ya yunkura yana ƙoƙarin mikewa tsaye " wannan kuma damuwarki ce daki yarda da maganata da karki yarda duk daya ke ban ma son ki yarda ki dauka a yadda zuciyarki ta dauka da sannu wata rana zaki fahimci komai sai dai zan so ki fahimta tun kafin lokaci ya kure miki, sai abu na gaba maganar takardar sakinki da kika bukata kullum daga gareni wallahilazim ba wai bazan iya sakinki ba kawai dai kina cin darajan iyaye ne bancin haka ba sai kin zauna kina sake maimaita bukatar wannan furucin ba " .ya karashe maganar yana taku a hankali acikin d'akin tare da zura hannuwansa gabadaya cikin aljihun wondansa can byn kamar second biyu ya tsaya ya fuskanceta " idan zaki tashi muje ki tashi idan bazaki tashi ba ki ci-gaba da zama har illa masha Allah dan bazan sake tunkararki da batun dawowa gidana ba "to bazani ba " ta furta a hankali tare da komawa tayi kwanciyarta ta juya masa baya tana kada jikinta , shiru yayi ya kasa kwakwaran motsi ya ci-gaba da kallon bayanta gbdy jikinsa yayi sanyi ji yake kamar zuciyarsa zata buga sai dai zuciyarsa cike take da tausayi saboda ya rigada ya gama cutarta ya gama da rayuwarta ."
a hankali muryarsa ta fito tamkar mai koyon magana "da dai kin daina jin komai a ranki tare da sauke duk wani izza da jiji da kan da kike dan Aliyu muradi ya gama dake ya gama da rayuwarki dan shine mutumin daya fara saninki diya mace wanda baki isa ki dawo dashi wannan budurcinnaki ba ya barki har abada "ni kuwa fa ko a yanzu idan naso zan samu irinki ko guda nawa nake so ". yana gama fadar haka ya juya yana taku a natse tamkar wani jinin sarauta , a mutukar firgice ta mike zaune tana kallon bayansa zuciyarta na wani irin bugawa da zafi tamkar zata kama da wuta har ya kusan fita daga d'akin idanunta na kallon kofar kamar ta tsaidashi ta ggaggasa masa magana son ranta sai dai ina tarasa dalilin da yasa bakinta da gangar jikinta suka kasa aiwatar da komai har ya karasa ficewa ."
A tsakiyar falo suka hadu da mumy ya tsaya cak yana tsutsa keyarsa da key' n mota tana ganinsa shi daya batare da kisna ba qirjinta ya buga da matsanancin karfi gaske ta zuba masa ido tana cewa "ya naga idanunka kamar sunyi ja ?"babu komai mumy kaina ne ya danyi min nauyi " to kuma na ganka kai kaɗai ina ita wannan take ?
"tana bacci tazo zuwa gobe idan Allah ya kai mu ni zan wuce gida " "to Shikenan kayita hakuri kaji har sanda Allah ya zai kawo maka saukin lamarin " yayi shiru kawai batare daya amsa ba ta sake tsaresa da idanuwanta "ko kana bukatar wani abu ne ? " ya girgiza mata kai alamun a'a " ka kama hanya ka tafi dare nayi Allah ya tashemu lafiya "ameen mamana " . ya amsa tare da sa kai ya fice kisna na jin fitarsa ta rushe da wani irin kuka mai cin rai tana juya maganarsa da gaske fa ya cuceni to ni yanzu zanyi na dawo da budurincina ? tayiwa kanta tambayar tana daura hannuwanta duka bisa kanta "to ke me yasa bazaki hakura ki zauna dashi ba? "ki zauna dashi mana tun dai shine ya rabaki da budurcinki shiru tayi ta rasa me yasa har yanzu zuciyarta taki karbasa a matsayin abokin rayuwarta . ta rasa me yasa kullum take tunanin kubuta daga hannunsa ta dade zaune tana kuka tana tunani ,wani zuciyar na bata shawarar ta hakura ta zauna dashi lafiya tunda shine mutumin daya amshi budurcinta da bazai taba dawowa ba kamar yadda ya fada yayinda wata zuciyar ke kwabarta akan zama dashi , tana nan zaune shiru ta saka wannan ta kwance har tunanin aunty afra yazo mata duk cikin abinda ya faru babu wanda yafi damunta ya kuma tsaya mata arai kamar batun aunty afra tana son shi , sam zuciyarta ta kasa yarda da hakan gashi dai agabanta komai ya faru Kuma aunty afra bata mutsa ba kuma idan bazata manta ba tasha ganin aunty afra tana cikin damuwa har ma ta tambayeta dalili to ko dai da gaske ne ba kazafi murafi yayi mata ba ?" Kai karya ne aunty afra tafi karfinsa nima na kasa son shi ina ga
mace kamar aunty afra ."ta lalubo wayarta ta soma neman layinta domin jin cikakken gaskiya daga bakinta amman number shiru bata shiga ta koma ta kwanta lamo hawaye na gangarowa ta gefen idanunta ta dade kwance jikinta a kasalance tana tunani so take bacci ya ɗauketa ta huta ko ta samu zuciyarta da gangar jikinta su samu natsuwa amman ta kasa ". bangaren muradi kuwa da kyar ya kai kansa gida yana jin wani irin damuwa mara misaltuwa kai tsaye d'akinsa ya nufa ta kwanata rigingine akan gado ya d'aga kansa sama yana kallon saman dakin yana tunanin yadda rayuwarsa ke gudana mai tattare da qalubali iri iri idan ya tuna shi din maraya ne bashi da uwa babu wani dan'uwansa da zai nuna yace wannan jininsa ne uwa daya uba daya sai yaji komai ya sake dagule masa cikinsa kuma daya kwallafawa rai wanda yake tunanin zasu maye masa gurbin uwa uba ya'ya da dangi an rabashi dasu " yaja numfashi ya fesar da kyar yana cewa "kisna kinci darajan iyayenki akan abinda kika min dan su kadai zan iya daga miki kafa domin sune mutane mafi soyuwa a cikin zuciya sun tsamoni daga qangi sun inganta min rayuwa wannan abu kadai ya goge duk abubuwan da kika min amman batun yafe wulakanta min ya'ya da kika yi har abada bazan yafe miki ba juyi yake yana jin zafin rabashi da ya'yansa datayi ji yayi abin ya dawo masa tamkar yanzu abun ya faru da kyar ya samu bacci yayi awon gaba dashi a can kusan karshen dare .."
Washegari da misalin karfe goma na safiya kisna ta fito falo sanye da doguwar riga ta iske mumy da dady tare da madu suna karyawa ta gaishesu dasu mumy ce kawai ta amsa mata da kyar amman shi dady ko kallon inda take bai yi , dan kusan har lokacin haushinta yake ji yafi kowa daukar zafi akan lamarin dan ko amsa gaisuwar bayayi mumy ta kalleta "kije ki shirya Ummi na kan hanya zuwa zata mayar dake dakinki bazan dai gaji da fada miki gaskiya ba a matsayina na mahaifiyarki kiyi amfani da damarki idan ta subuce miki zai wuya ki dawo daita dady ya mike tsam ya nufi turakarsa dan bazai iya zama a duk inda kisna take ba tuni ya cireta acikin ya'yansa furtawa ne dai kawai bai yi ba haka ma madu tashi yayi ya fita zuwa haraban gidan ".
" bamu da lokacin kisna ma'anar bamu da lokaci kuwa shine mutuwa tana iya riskar bawa akoda yaushe idan kika mutu me zaki cewa Allah akan rayuwarki da mijinki ?" komai lokaci ne kisna idan Allah yayi nufi ya barki haka wato har mutuwa kina karkashin muradi haka zaki karaci guje gujenki ki hakura dashi , idan kin bi mijinki kin kyautata masa sai kiga gobe kiyama Allah ya baki kima da wata daraja ta musamman idan kuma kika cigaba da kuntata masa gobe kiyama zaki kasamce cikin azabar Allah sai kizo kina nadamar ina ma bakiyi masa abinda kika yi masa a rayuwar duniya ba ". Sannan ki yawaita istigifari kisna saboda hakin ya'yanki da kika kashe Allah bazai barki ba saboda ya'yan nan amana ne agurinki amman saboda zalunci kika kashesu ,kiyi hakuri ki cigaba da addu'a duk abinda yake alkhairi arayuwarki ta duniya Allah yasanya miki a ranki , kisna ina miki fatan shiriya ,Allah ya shiryeki Allah yasa ki gane abinda kike yiwa muradi zalunci ne ki daina duk abinda kika masa nice number one da zan soma shiga damuwa ina miki fatan ya Allah ya Ubangiji ya amshi tubanki idan kinyi dan shi," kisna ko baki bani farinciki ba muddin kika bawa muradi kin bani kuma zan ji dadi sannan zan godewa Allah ina ji ajikina karshen matsalar tazo inshallahu saboda haka ina da kwarin gwiwar cewa da izinin Ubangiji komai yazo final Allah ya baku zaman lafiya ya sake azurtaki da wasu ya'ya masu albarka wanda duniya zatayi alfahari dasu mumy ta karasa maganar tana zubar da hawaye itama kisna hawaye take tana jin wani iri a zuciyarta ta rarrafo gurin mumy ta daura kanta bisa kafafunta tana kuka " mumy ta kasa magana ta daura hannunta akanta tana cigaba da zubar da hawaye suna cikin wannan halin aunty ummi ta shigo ta iskesu "numfashi ta sauke yayinda mumy ta shiga goge hawayenta tana dubanta ta durkusa har kasa ta gaisheta tana cewa "kukan me kike yi? " kardai akan wannan takadiriyar kike hasarar hawayenki mumy ? " ya zanyi ummi Allah ya jarabeni akan kisna ki tayani addu'a ummi bana son na mutu na bar rayuwar kisna haka "Allah ya kyauta Allah ya ganar daita gaskiya ta tashi muje na sauketa akwai inda zani mumy ta rike hannun kisna sannan ta mike ta nufi dakinta tana sake yi mata nasiha mai ratsa jiki ta dauko hijab sabo fil Wanda ta siya musu ita zee ce ta zira mata suka sake fitowa tare still tana sake jaddada mata tayi hakuri da mijinta har bakin mota ta rakasu sai data ga tashinsu sannan ta dawo ciki tunda suka shiga mota kisna ke cika tana batsewa kamar ba ita aka gamawa fada ba ."aunty ummi ta kalleta kawai ta share cikin minti talatin suka iso gidan sun iske muradi zaune a falo yana gaban system yana faman tura wasu sakwanni , sallamar aunty ummi ce tasa shi dagowa daga abinda yake yana ganinta ya saki fuska yana murmushi "aunty nah kenan kece yanzu da sanyi safiyar nan "wani sanyi safiya ka duba agogo kaga lokacin dai yanzu ya wuce akirashi da safiya ". ya kai dubansa ga agogon bangon dake manne a falon yana cewa "gaskiya ya wuce sanyi safiya dake ban dade da shi ba tun danayi Sallah asuba na koma bacci sai dazu nan na tashi nayi wanka na hau kan aiki barka da isowa ina yini ? "ya gaisheta yana matsar da system din daga gabanshi ta samu guri ta zauna tana masa masa " itama kisna guri ta samu ta zauna tana cika tana batsewa bata yarda ta kalli inda muradi yake ba shima iskar data dibo bai kalla ba ya cigaba da kallon aunty ummi "ke me kike nufi bazaki gaida mijinki ba kin wani hakince ?"batare data juyo ba tana shan tace "ina yini ?" tabe baki yayi sannan yace "lafiya atakaice suka shiga tautaunawa da aunty ummi akan matsalar kisna a karshe ta hadasu gabadaya tayi musu fada tana gama magana kisna ta mike ta shege dakinta aunty ummi ta mike ta biyota tana shiga ta rufo kofar dakin "dan girman Allah ki daina kunbure kunbure nan haba me yasa kike cika kike batsewa me yayi zafi kisna ? Dan girman Allah ki rungumi mijinki ki saki ranki kisna wallahi idan kina son kiji dadin rayuwa sai kin saki ranki kin maida komai ba komai ba kin manta .wai auren hadi aka miki , wai ke muradi bai isheki misali ba shima fa baya sonki