Showing 279001 words to 282000 words out of 495987 words

Chapter 94 - Cutar Kai Book Complete Hausa Novels by Aysha Bagudo.txt

takalma, getzner na cotonou da  chiganvy, volyal lace  duk akan farashi mai sauki ,ga mai  bukatar  siyan ɗaya ko sari  yayi magana ta wannan number 08059623096.

A  matukar  gigice  kisna take  kallonsa  cikin tsananin  tsoro da firgici sam  batayi  tsamanin zai  daga  nikaf dinta ba ganin  asirinta  ya  tono no  going  anywhere  yasa ta  rushe da matsanancin  kuka  ɗan batasan  menene zai faru daita  ba idan Samir ko madu suka ji   sannan batasan  abinda zatace dan kare  kanta ba agurinsu  dan ta muradi   mai sauki ne  zai iya kyaleta taci bulus batare daya taba lafiyar    jikinta ba   gabad'aya   jikinta ya kama  rawa kamar mazari a zahiri yake iya hango tashin hankalin data  shiga  bata ce masa  komai ba  illa ta durkusa  kasa  bisa gwiwowinta  dan  tasan na  lahira sai ya fita jin dadi  a  gurinsu  samir  idan suka ji abinda tayi kokarin yi  sai sunci ubanta , hakuri take son bashi amman ta kasa magana ."

kugunsa  ya  rike da hannu  daya  yana cigaba da mata kallon mamaki yayinda  tawagar tafiyarta  kowacce tashiga  rawar jiki da neman  hanyar  gudu yayi  saurin  kallonsu  yana zare  musu  idanunsa yace "duk  ku  dawo nan ke kuma  zinnira  har dake  a saka hannu gurin fitar  kisna  gida bayan kinsan  komai ? "uhm ammm  wallahi .... " ya daka  mata wata razannaniyar  tsawar data  hargitsa ya'yan cikinta  "yi min  shiru  stupid  bana  son jin komai  daga  bakinki na dauka kina da hankali a she kema ol the same ne daita   nan   zinnira ta fara kuka wiwi tamkar ance  uwarta da ubanta sun  mutu  "ke kuma ina kike shirin zuwa ?ya tambayeta yana tsareta da idanunshi masu matukar  firgitarwa  a rikice tace "gidansu zinnira zamu ko zinnira ki faɗa masa gidanku zani wani gigitaccen mari ya kifa mata sai da jinta da ganinta ya tsaya na wani lokaci  "you are very stupid ni  zaki  yiwa  karya  you better   tell   me where are  you  going to  kafin na tatttakaki ?"Cikin  Muryar  kuka tace " gurin musa  zani ..."
"What ? Ya furta da karfi qirjinsa  na luguden bugawa   take wata irin zufa ta shiga tsatsafo masa a gabad'aya ilahirin jikinsa kamar an watsa masa ruwa ya kamo lip's dinsa na kasa yana cizawa da karfi ko zai rage jin bugawar da zuciyarsa ke yi fuskarta dake tsiyayar ruwan hawaye ya cigaba da kallo "wannan wace irin maseefa ce ?"yaushe zukatansu zai hutu da matsalolin kisna ?shiru yayi na tsawon mintina yana tunani da kallon fuskarta yayinda kawayenta kowacce cikinta ya duri ruwa jira suke ya gama daita ya dawo kansu cikin haka sai ga Samir ya shigo da sauri  dan shirin  zuwa buga wasa turus yayi yana kallon muradi daya tasa kisna gaba da ido gefe guda gasu zinnira sun hada uwar gumi suna juya hannu kallo daya yayi masa ya fahimci yana cikin tsananin ɓacin rai kuma yasan ko yayi masa magana a lokacin da wuya ya bashi amsa dan haka ya sa kai ya shige cikin gida yadda muradi  ya dauke kisna da mari haka ya juya ya dauke sauran yace duk su cire nikaf din fuskarsu
tsab ya gane sauran biyu din ummana da sala ne daman kuma ya lura suna da dan rawan kai har gara zinnira.

  ya  tasa keyarsu  zuwa cikin gidan suna kuka suna rokonsa banda kisna da haushi ya taru yayi mata  yawa  har saman dakinsu ya kai su simi simi suka shiga yayinda kisna taki  shiga  aiko ya cicibeta ya shiga dakin daita ya direta "maza ki kama kunnenki kafin nayi miki ruwan kyankyasai take tayi saurin kamawa suma sauran sukayi tun kafin ya waigo ya tsare kisna da ido "kinsan Allah ko da wasa naji kin sake ambar sunan yaron nan zan mugun  baki mamaki kinsan tunda kike wulakancinki a cikin  gidan  nan ban taba sa hannuna ajikinki ba tsakanina dake nasiha ne wallahi  karki bari na nuna miki tru colour dina shekarunki shabiyar a duniya amman har yanzu kina hauka yanzu haka shi yana  can ya manta dake a rayuwarsa me kike son maida rayuwarki yau shekara day day har biyar ana kan abu daya wannan wani irin naci ne ? fada sosai yayi mata  kisna banda kukan bakinciki babu abinda take tana jan kunne  ,zama yayi ya fasa zuwa inda zata shi dan tuni ya cire takalmin ƙafarsa  da rigar jikinsa ya saura daga shi sai  singlet   da gajeren wando  ya ja karamin table din glass din  dake tsakiyar dakin ya daura kkafafunsa ya fuskanci su zinnira    "ku kuma kananun yan iska har kun  san kuyi wayon fitar daita kou ? a tare  suka girgiza  masa kai  hawaye shabe shabe a fuskarsu suna bashi hakuri "you are very stupid da hakuri da kuke bayarwa  maza ku canza  zuwa frog jump marasa kamun kai kawai  babu mutsu suka canza har kisna "dan  Allah  kayi hakuri "inji cewar zinnira "shiiiiiii kiyi abinda nace  samir ya gama shirinsa ya fito "halan wannan uwar yan rigimar tayi halin nata yayi shiru yaki yin magana "ya zamu fita kuwa naga ka cire kaya ? "wallahi ina ganin bazani ko'ina ba Samir yace "shinkenan mu bari gobe kawai bari naje na fadawa jahid wai me kisna tayi ne ? "ka fa daina  goya mata baya  sam bata  da mutunci duk yadda samir yaso jin abinda tayi kin fada  yayi, muradi ya bala'in wahalar dasu jikinsu sai rawa yake ko'ina ciwo yake musu  Samir kuwa sai kara zuga yake dan yasan duk abinda yasa muradi punish din  kisna da kawayena abu ne mai girma suka masa dan haka ya dauki din madu ya shiga zabga masu ta ko'ina suna ihu suna susa duk inda belt ya sauka sannan  ya fita.

  kai tsaye  dakin mumy ya nufa yana shiga yaga abun mamaki dan tarar da mumy  kwance rashe rashe akan gado ga zee kusa daita ko wadataccen numfashi bata saukewa  karasawa yayi cikin sauri ya kai hannu gurin hancinta  yaji babu numfashi haka ma zee shi abinda ya daga masa hankali bai taba ganin mumy tayi bacci bayan sallahr  la'asar ba da sauri ya juya ya bar daki jikinsa na rawa Yayi hanyar sama  "tun daga kan step  yake ihun  kiran  sunan muradi cikin  tsananin tashin hankali " kazo  na shiga dakin mumy na gansu gaba-daya a kwance kamar basa motsi wata irin zabura  muradi yayi ya mike tsaye shi kuwa Samir tuni ya juya ya bar dakin da sauri , kulle kofar muradi   yayi ya bar gurin da sauri cikin kankanin lokaci aka kira ya badamasi nan ya tabbatar da suna raye anyi musu amfani da maganin bacci mai karfi ne nan da nan yace a hada musu coffe har asabe dake zaune a kitchen tana bacci   a basu  cikin knkanin lokaci aka hada aka  basu sai dai basu dawo haiyacinsu ba muradi ya juya ya nufi dakinsu domin jikinsa ya bashi aikinsu kisna ne  yarinya kamar aljanna  ya tsura mata ido yana hadiye wani kulli daya tsaya masa a makoshi kisna ta ɗan tsaya    tare da  bude idanunta da yayi mata nauyi taga shi ne wani sabon marayan kuka ta fashe dashi tana shesheka  dan ya tausaya musu kawayenta na tayata murya a shake yace "duk ku biyoni suka mike da kyar suna rike kafafu har dakin mumy nan take gabansu ya buga ganin an cika a dakin har dady    .

"kune kuka bawa su mumy maganin bacci ko  gabad'aya suka yi tsuru tsuru tare da nuna kisna  dake tsaye "wallahi itace itace tasa mata mu babu ruwanmu mu dai tace mana mu taimaka mata ita kuma  zinnira wai sonka take shine kisna tace idan ta taimaka mata taje gurin musa itama zata taimaka mata  ta hadaku aure  inji cewar sala  "ya subhallah muradi ya furta yana kallonsu daya baya daya, takaicinsu  bai bari yabi ta kan maganarsu ba yace "ke ....a ina kika  samu maganin bacci gashi kin illata  mumy  dasu asabe  ? yayiwa kisna  tambaya yana kallonta  "cikin Muryar kuka tace "wannan makira  ce ta kawo min"  tayi magana  tana nuna ummana da yatsa  take  jikin ummana ya dauki rawa  ta fashe da kuka  tace "ai kece kika ce  na .."tsaya tsaya ya dakatar dai ta  ta hanyar buga mata tsawa "me yasa da tace ki kawo mata  baki fadawa daya daga cikinmu  ba kika biye  mata  sai na police sun kamaku yau  ke  Kuma kinga rayuwarki  ko  "kina cewa wata makira bayan gaki ƙatuwar  makira   dan  har yanzu mumy bata motsa ba a sanadiyyarki  idan wani abu ya sameta sai kinga yadda zamuyi dake  da kuka kisna takarasa inda mumy take kwance tana kuka "dan Allah mumy ki tashi karki mutu wallahi bazan sake ba ina  sonki bana son ki mutu ki barni  Samir ya cakumo wuyanta zai buga kanta da bango muradi  yayi hanzarin  hanashi dan yasan yana buga kanta ta tashi aiki  "barta  kawai Samir  dukanta bazai sa mu huce bakincikinta ba  da kyar muradi ya  amsheta a hannun Samir dake tsuma  sannan ya  kora  su  zinnira  zuwa  gidajensu da kyar aka samu   asabe  da  zee sun  farfado  a ranar amman mumy kam   sai da'aka danganata da  asibiti  da kyar aka samu ta dawo daidai  lokacin data tashi taji abinda kisna tayi ta rushe da kuka "wayyo Allah kisna zaki kasheni  wannan wacce irin yarinya ce .."?" wallahi dana san irin kisna zan haifa da na cire cikinta a lokacin dana samu kuka take sosai tana zuba surutai yaranta suka zagayeta suna share mata hawaye , "wallahi mumy ko nan gaba kisna ta baki abu karki ci dan zata iya kasheki inji cewar madu .."
Tun  daga  ranar dady bai sake samun sukunin  ko walwala  ba haka itama mumy yayinda dady ke  mamakin nacin  irin na kisna  yasa aka kira masa ita tana zaune a gabansa idanunta na kallon tayis din  dakin" sakina ya kira complete name dinta ta d'ago kanta da kyar tana kallonsa  "kina bukatar rayukanmu ko ? ta girgiza alamun a'a ",to me yasa kike son daga mana hankali da dagula mana lissafi ?"kin fi  son yaron nan  akan rayuwa damu ko "?ta sake girgiza kai " karki ce a'a kin fi sonshi mana  tunda kin fi jin magabarsa akan tamu sosai ya dinga mata fada da nasiha daga karshe ya sallameta .."

Da  fari   dady  kanwarsa  Hajiya  ummah   ya soma tunanin  ya  samu da  maganar  kisna  bayan kwana  biyu  da faruwar lamarin ya shirya direbansa ya kai shi gidan inda ya isketa  tare da mijinta  kasancewar weekend  ce  suka  gaisa a  mutunce   Alhaji   tijjani  muhamud  adam ya mike dan basu guri ya koma  can nesa kadan dasu ya zauna yana duba magazine  hajiya ummah tasa aka  kawo dady ruwa  da  lemun chivita mai sanyi aka ajiye agabansa    dady ya numfasa  sannan  ya  fara magana  a tsanake "ummah  nazo ne akan ifitila'in  daya samemu gabad'aya" jiki a sanyaye tace" Allah  ya kyauta ya shirya mana kisna koni abun  ya  dameni addu'a dai zamu cigaba da yi "haka ne muna kanyi yinta na  dade  ina tunani yadda  zan  shawo kan matsalar dake faruwa da kisna   sai  gashi cikin sauki aka fada  min cewar  dana  nazir   yana  cikin  wadan da suka nuna suna  son kisna  abun  yayi min dadi    kwarai  da gaske yanzu dai atakaice  nazo ne na sheida miki idan da  gaske  yake ya fadawa mahaifinsa  azo   neman aurenta  bana bukatar komai nashi sai sadaki kai  sadakin  ma zan biya cikin  tsananin  firgita da tsinkewar zuciya Alhaji tijjani muhamud adam ya juyo  ya fuskanci inda  suke  zaune  dan duk yana jin maganarsu  cikin  tsuma  da  karkarwa  ya mike  tsaye yana nade jaridar  hannunsa ya soma  takowa a hankali tare  da murtike fuska yace  "kayi  hakuri Alhaji realwan  dana nazir bazai auri wannan yarinyar ba sai  lokacin  hankalin Hajiya  ummah ya kai garesa tace  "saboda me zaka fadi wannan kalmar kuma  a gaban dan'uwana kana son  'bata mana zumunci ne  ?"  bayan  kasan kusan auren  da'ake yi kenan a cikin  family dinmu gashi da alamun naxir din yana sonta dan ya fada min da bakinsa   kuma  naji dadin  haka   jira  nake  kisna  ta dan kara  ayi maganar aure  shine zaka ....."
"nazir danki ne ko nawa ? Ya katseta ta hanyar fadan haka tayi shiru tana dubansa kamar  yadda dady yake kallonsa  cike da mamakinsa tunda shi din ma kusan  danuwa ne  kakaninsu   uwa daya uba daya  ne  jiki  a sanyaye tace "dan ka ne "
"Alhamdullahi da kika ce dana ne  to  na dade da   samar masa  matar da zai aura nima lokaci kawai  nake  jira  
"da ina da wani dan sai ya aureta amman kiga shi kadai gareni Allah yayi mata zabi mafi alkhairi."

juya maganarsa  take a zuciyarta  taji wani abu ya  tsaya mata rai  ta tsaya sosai tayi masa duban tsanake sannan tace "me yasa tun farko baka sheida min ba sai yanzu da kaga yaya yazo da bukatarsa sannan zakace ga zance ga magana  ?"babu wani ga zance ga magana nayi haka  ne  saboda dana ne idan lokacin yayi zaki  kisani  dole  ranta yayi mugun ɓaci ta soma  magana  cikin daga murya  da zafin zuciya nan  suka shiga  fadawa juna magana  ganin  rayuka zai  ɓaci a banza kuma ba'a samu biyan bukata ba  yasa  dady ya  sauke naunauyen ajiyar zuciya yace  "Alhaji  tijjani ka zauna duk abun bai kai  na  tashin hankali ba d'a dai kamar yadda ka fada danka ne kuma inshallah  baza'a sake maganar  akanshi ba kuskure  na ne  sai dai  na dauka  a halin da nake ciki  kana  cikin mutanen da zasu rufa min asiri su tallafawa rayuwata amman babu komai Allah  zai nuna min yadda zanyi  "dady na  gama fadar haka ya  mike tsaye cikin sanyi jiki  yayiwa  hajiya ummah  sallama  ya   wuce  Alhaji tijjani  ya  ta'be baki ya zauna bisa kujera ya cigaba  da magana "ina wallahi  bazata  sabu ba" 
"Gaskiya ban ji dadin abinda kayi  ba ai ba kai kadai  ka haife nazir ba "muddin dai  kinsan dana ne nazir ba shegensa kikayi ba  na  gama magana  babu batun aure  tsakaninsa  da wannan yarinya  mara jin magana  ,  yarinya da ko aurar daita akayi sai ta gudu taje gurin saurayin da take so ke yanzu kinga  dacewar su  dan Allah ? "Duk mutumin daya san ciwon kansa bazai soma amsar auren wannan yarinyar ba shi kuma zai zo ya sameni sai naci mutuncinsa idan na sake jin labarin yaje gidan da sunan zance zai ga abinda zan masa Allah ya nuna masa yadda zai yi ya aurar daita amman muddin ina raye nazir bazai aureta ba "amman ka cika butulu wallahi ba yaya ya kamata kayiwa haka mutumin da ..."dakata gori zaki min ko me ?"shi din ma ai sai ayi maka fada sosai sukayi sannan ya fice daga gidan ,a kasalance ta koma ɗakinta ta kwanta dan ta huta ko ta samu zuciyarta da gangar jikinta su samu natsuwa ..


Daga gidan hajiya ummah   gidan abubakar tafida  shima dai the same thing ya iske abinda ya faru a gidan Alhaji tijjani muhamud adam shi ya faru  jiki a sanyaye  dady ya dawo gida tare da matsananci ciwon kai yaji kamar yayi kuka da kyar ya fito daga cikin motarsa yana tafiya babu laka, da sauri muradi daya shigo domin ganin shigowar motarsa ya biyo bayansa har ya kai daki   "lafiya dady?  ya fada sanda yake fuskarshi sai yaga kamar Idanunshi yayi ja tamkar garwashin wuta "babu komai dana kaina ne yayi dum  muradi bai sake yin magana ba amman ya mika masa dukkan attension dinsa yana bukatar ƙarin bayani dan zuciyarsa bata yarda iya ciwon kai ke damunsa ba  da kyar ya bude bakinsa ganin dady bashi da niyyar cewa dashi komai "dady nasan ni din dan riko ne a gurinka sai dai ban taba jinka amatsayin marikina ba ina jinka ne tamkar uban daya kawoni duniya dady baka taba boye min komai ba duk damuwarka na sani tun a can baya adalilin soyayya da yarda tasa damuwarka ta zama tawa saboda ka cancata kai din nagartaccen mutun ne ka cancata a shiga cikin lamarin damuwarka dan Allah kayi hakuri dady ka fada min damuwarka " ya karasa maganar cike da tausayawa .."

Dady ya nunfasa sannan ya fara magana cikin tsananin tashin hankali "damuwata bai wuce akan kisna ba nan take dady ya warware masa komai labarin daya tsuma zuciyar muradi saboda tsananin tausayin dady ya sake kamashi  har kuka muradi yayi yana kallonsa cike da tausayawa tausayinsa ya mamaye zuciyarsa  yaji tozarcin da'aka masa yayi yawa dady bai cancanci haka daga yan'uwa da abokan arziki ba ya cancanci su ji tausayinsa su kaunaci bukatarsa hannusa ya kamo ya zaunar dashi akan kujera yaje ya bude fridge ya dauko masa lemu mai sanyi ya tsiyaya masa a cup ya bashi "ka sha dady ya amsa ya rike kawai yana nazarin rayuwa batare daya sha ba " abinda bazai taba yiwa Abubakar tafida da tijjani ba a rayuwarsa shi suka masa sun nuna masa iyakarsa sannan sun fahimtar dashi kowa kansa ya sani Idanunshi suka sake rikedewa suka yi jazur muradi ya kwantar da kai ya fara magana cikin sanyi lafazi "dady kasanyawa zuciyarka hakuri duk abinda ya faru da bawa a rayuwarsa da sanin ubangijinsa tun daga haihuwa har zuwa mutuwarsa a tsare yake a rubuce a allon lauhul mahfuz bawa bai isa ya tsarawa kansa rayuwa ba iyakacinsa bin umarni duk inda aka kai shi da rungume komai aka jefa masa da hannu biyu biyu hakika Ubangiji na jaraba bayinsa mafiya siyowa a gurinsa ta fannoni da dama kuma yana murna da masu godiya a duk halin daya barsu da rungumar kowacce qaddara, Allah yana son bayinsa masu tawakalli da hakuri domin har yana fada acikin Alqur'ani mai tsarki cewa "innallaha ma'assabiri wato lallai yana tare da masu hakuri dan haka ka kara  hakuri Allah na tare da kai ka manta damuwar da suka kunsa maka dan zai iya cutar da kai baka isa ka daukewa kisna rayuwar da take ba sai Allah ka cigaba da yi mata addu'a

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login