Showing 294001 words to 297000 words out of 495987 words

Chapter 99 - Cutar Kai Book Complete Hausa Novels by Aysha Bagudo.txt

zama  cikakkiyar budurwa komai yaji ajikinta suna tsaye lawan ya shigo da akwatinta ta yatsina fuska kamar tayi magana sai kuma ta fasa tunawa datayi a gaban sahebarsa take ."

Jan akwatinta tayi  ta nufi  dakinsu ta shiga  sai  dai  bata iske  zee  ba  ,dan haka  ta fada  toilet ta  watsa ruwa sannan  ta sanya  wata doguwar riga mara nauyi ta nufi shashin mumy  tana tambayarta zee "tana makaranta zuwa anjima zaki ga "kisns ta yatsina fuska wanda ya rigada ya zame mata jiki sannan tace "gaskiya naija akwai ci baya mumy  yanzu har na kare karatu na bar aunty zee ?"  tayi  fa kusan  2 year's kafin na bar kasar nan  koda yake  da taso da kun turata wata kasar itama  ". haka ne zee ce akwai kulafin gida "kulafucin  gida ko kulafucin son ya samir ? "Ban sani ba muje kici  abinci,  abinci kusan kala hudu taci suna hira da mumy sai bayan  la'asar  zee   ta shigo da murnarta  tun daga haraban  gidan ta samu  labarin   dadowarta ta tsaya  bayanta ta  rufe mata idanuwa tana fadar "canki ?" Kai tsaye kisna ta kira sunanta  cike da doki tayi dariya ta bude mata ido  suna  cikin  haka sai ga aunty afra wata irin Kara  ta saki  sannan ta rungume kisna itama ta  rungumeta "kisna kice haka ? "Kin ganki kuwa ? Kamar wata  balarabiya ko  ?"inji cewar zee "wallahi babu wani  bambanci suka sa dariya gaba-daya har kisna afra ta ja hannun kisna  zuwa ainihin  parlour'n gidan yayinda zee ta shiga daki dan watsawa jikinta ruwa   hira ta  balle tsakanin aunty afra da kisna suna  cikin  hira kisna ta kalli afra tace "aunty afra ya naga kin Kara lalacewa fiyye da  lokacin da nake kasar nan"?  "wai meke damunki ne haka  "? " Ko dai kina da matsala da yaya badamasi ne kika barwa cikinki kina azabtar da kanki a banza ?".. tayi mata tambayar ajere tana sake kafeta da idanunta domin jin abinda zata ce ganin tayi shiru ga yanayinta gbdy ya sauya alamun dai tana cikin damuwa yasa kisna kamo hannunta "plz tell aunty afra ki fada min damuwarki dan Allah  ban  ji  dadin yadda naganki ba" "damuwata tana girman da bazan iya fada miki ba  amman karki damu da sannu zan shawo kan komai ai dai kinsan auntynki babu sanya gurin dabaru "? Kisna ta gyada tana murmushi .."

Bayan  aunty  afra ta koma bangarenta  zee ta fito ta  shiga kitchen ita kuma ta  koma daki ta kwanta ta soma  tunani musa tsawon wasu awannni ta dauka tana tunaninsa ita kanta wani lokaci tana mamakin yadda  girman son shi yake a zuciyarta ta yadda bata ita  hadashi da kowa dan tana jinshi kmr rayuwarta ne a haka har bacci ya dauketa mai cike da mafarkinsa kala kala hayaniyar jamar gidan ne da suka  dawo  aiki  ne ta tayarda ita daga naunauyen baccin  daya sureta tun byn sallahr la'asar ga shi yanzu har an idar da magrib,  madu ya shigo yana cewa "mutanen London kenan an dawo lafiya  ?dariya tayi tace "lafiya  ya madu na sameku lafiya ""
"Alhamdullahi  kije  inji mumy ta mike  "ina zuwa" Toilet ta nufa ta dauro alwala tai sallar magarib da isha'i sannan ta fito zuciyarta na wani irin tsinkewa a lokacin data hango muradi a saman dining yana cin abinci qirjinta yayita bugawa  kujerar da mumy ke zaune  ta raba  ta zauna ayangance  tana fadar "mumy yauwa  na manta daman ina son nace mai  yasa ba'a turo ya Samir ko madu ko direba daukata ba  sai wannan sauran kadan fa yau da gawata za'a kawo miki  "
"na sha fada miki muradi ya wuce wannan agurinki  yayanki ne fa  "nifa yayyayena guda  hudu ne  fa ki daina sakashi  a sahun yayyayena sannan shi ai yasan matsayinsa kece dai kike kai shi inda Allah bai kai shi ba  "karki fara da bani ciwon kai kisna  daga dawowarki  ,yanzu ke ba yarinya bace "bari na sake tuna miki matsayin muradi  ɗan yayana ne da muke ciki daya  kamar yadda na sha fada miki "yaakayi har tsawon lokacin nan bamu taɓa ganin yayan naki  ba wanda ya kasance mahaifinsa  ? Wata tsawa mumy  ta daka mata " kinsan banason tambaya ko maza tashi ki bar gurin  nan  tsorace ta mike ta nufi hanyar  shiga dakinsu  "ina zaki  hajiya kayi ? yayi dauriya fadar haka dan kar mumy ta fahimci damuwarsa ta galla masa wata ƙatuwar harara . "dawo  ki ci abincinki "  yatsina fuska tayi a ranta tace baza'a dawo  ba  uban yan iyayi kawai  ta koma ta  zauna kan kujera kasa cigaba da cin  abinci  yayi  ya  tsura mata ido zuciyarsa  na raya masa al'amura da dama sai  da ya mike  ya dawo kan kujera  sannan  ta dawo taci abinci..

Dady  yayi  matukar  murna da dawo war  kisna ,ganinta zaune akan kujera ga alamun   natsuwa a tattare daita yasa zuciyarsa samun natsuwa "auta ya furta a hankali jin muryar dady ya sakata tsalle ta nufo inda yake a guje tana kiran "dady nah !dady na!! Ta fada jikinsa tana faman kyalkyala masa  dariya yace "mamana sannu dawowa fatan an kare karatu lafiya ? A shagwabe "tace lafiya lau dady tun dazu nake jiran dadowarka "to yanzu gani na dawo bari naje na watsa ruwa maza ki fito min da tsarabata kafin na dawo tayi murmushin jin dadi tana gyada masa kai ,daki ta koma cike da doki ta fito da akwatin data zo dashi a lokacin Samir madu muradi har ma da zee suna zaune ana chapter  ta zauna  ta  bude ta soma raba tsaraba  ta bawa  Kowa nashi ta cire wa masu aikin gidan ta kirasu ta basu hatta baba  mai gadi ta cire masa nashi amman  banda muradi duk suka tsura mata ido har ta gama sannan samir yace "ina tsaraban muradi naga kin bawa Kowa ban dashi ta dube shi sosai fuskarta a hade "wane ne haka kuma  ya Samir ? "Kina hauka ne ni zaki tambaya waye shi ?  Yayi mata tambayar a kufule kamar zai wanka mata mari "ni ban san shi ba dan haka banyo tsarabata dashi ba kamar jira suke ta fadi haka gaba-daya suka dawo mata da tsarabanta suka mike tsaye  suka barta daga ita sai muradi wanda  ko  kallon inda take bai yi ba, harkokinsa yake akan system  dan kallonta ma   na sashi jin matsanancin faduwar  gaba    tsaki taja ta mike "aikin banza sai me idan kun dawo min dashi me zai dameni ? "Babu abinda zai dameni sai ma wasu da zasu mora ta kwashi na dady ta nufi bangarensa a daidai lokacin daya gama shirinsa yana ganinta ya fadada fuskarshi da murmushi "duk tsarabata ce wannan mamana  ?kisna ta gyada masa kai  sannan ta zube kayan  akan kujera "gaskiya mamana na gode nima kuwa zan miki kyakkyawan tukuici tare da neman alfarma agurinki  ya kamota ya zaunar daita shima ya zauna "maman kin kara girma kinyi kyau tayi murmushi tace "haka kowa yake cewa "wannan gaskiya ne  idan na natsa akwai magana mai mahimmanci da zan yi dake nasan zaki fahimceni da kunnen baseera tunda ga dukkanin alamun mamana tasan ciwon kanta yanzu "ta sake gyada masa kai kusan minti goma suna magana su Samir kuwa suna dakin mumy babu wanda bai zage kisna  ba ",wallahi mumy har yanzu kisna na nan da mugun halinta sam zuciyarta bai da kyau na rasa abinda muradi yayi mata data dauki karan tsana ta daura masa inji cewar madu "babu abinda ya mata da ikon Allah mugun halinta akan zai kare duk ku fita harkar shegiya ta karasa maganar tana fitowa .
     a nan dakin  dady  mumy ta biyosa  da abincinsa tana zabgawa kisna harara  take tasha jinin jikinta "ya da hararar min uwa  kuma daga dawowarta ? "ai tasan abinda  tayi kuma wallahi idan bata canza manufarta akan muradi ba kowa zai ji mu daita a gidan nan   "ta fadi haka tana sake zabga mata harara ",wani abu ne ya faru ? "Gaskiya nima akan Aliyu zamu samu matsala mamana   ganin  sun hade mata kai sai fadar yadda suke qaunar muradi suke yasa  simi simi ta bar musu dakin suje su karata bata masa tsaraba kuma babu wanda ya isa yasa ta bashi  .."

Yau kwana uku da dawowar kisna amman babu mai shiga lamarinta duk wanda tayiwa magana baya kulata kowa ya dauke mata wuta akan abinda  tayi itama ta sharesu amman samun kiran musa da tayi  yana son ganinta a  waya  itama kuma tana son ganinsa   wannan  dalili yasa ta saki fuskarta sosai da kowa  amman still babu wanda ya waiwayeta  ta bawa zee  hakuri   "kiyi hakuri aunty zee daga fushin da kuke yi dani "to ke din ce baki da kirki ai ba'a yin haka ya Aliyu na matukar kula da rayuwarki tun kafin ki bar kasar nan har zuwa sanda kika dawo duk kudin da za'a aika miki London  daga aljihunsa yake fita shine mutumin daya  tsaya bisa lamuranki ta ya zaki bawa Kowa abu ki hanashi muji dadi bayan har masu aiki  kin bawa?"  "naji nayi kuskure ni yanzu bana son na samu matsala da kowa a gidan nan muje ki rakani na bawa ya Samir hakuri da kyar ta lallaba zee  ta tajata  dakinsu   ta bashi hakuri yace "muddin kina son na hakura sai kin bawa muradi hakuri "muryarta a raunane tace "kayu hakuri "yayi kamar bada shi take magana  ba har sai da ta sake maimaitawa  "wuce " ya fada atakaice  batare daya kalleta ba kai tsaye daga dakinsu na mumy  suka shiga dan bata hakuri itama fada tayi mata sosai  sannan  tace  ya wuce amman ki canza "naji mumy  .."

******
Washegari  gidan ya hargitse da farinciki  kowa ya saki ranshi sai chapter suke a tsakaninsu  har dady dake kokarin fita office tare dasu Samir  kisna ta mike bari naje na shirya zanje gidan granny  ta shirya ta fito cikin wata  hadaddiyar doguwar riga bata ga dady ba da su ya Samir da alamun sun fita zuwa office "mumy bani mukulin motarki zanje gidan granny na dawo " mumy ta girgiza mata  kai "ban yarda ba kuma kice zakiyi diraving da kanki sai dai ki bari direba ya kaiki  idan kina so kenan cikin jin haushi tace "na yarda mumy ta kira lawan   ta bashi umarnin ya kai kisna gidan Hajiya aysha kuma ya tsaya har ta gama ya dawo daita  ya amsa mata da "to"  yayi gaba ta biyo bayansa har haraban gidan ya bude mata baya a natse yake yin komai saboda yana da labarinta agurin mai  baba gadi daya zama kamar dan'uwa yanzu a gurin Alhaji realwan .

  suna  fita  daga  gidan tace "dauki hanyar agege ogba  yayi  mamakin jin abinda tace Idanunshi ya dago   ta glass din  cikin motar ya kalleta sosai  domin jin karin bayani "kallon me kake min  ko bazayi abinda nace bane ? Muryarsa a sanyaye yace "zanyi sai dai Hajiya ......"shiiiiiii muje kawai inda nace  kwarjininta ya hanashi musamata ya cigaba da tuki yana mamakinta  ta ciro wayarta  ta kira number musa tace su hadu dashi a ogba garding  , basu dade da zuwa ba ya karaso akan  mashin  ta  mike tsaye  daga zaunen da take suka rungume  juna har da manna mata kiss  a baki  rayuwar yoroba dai sak kisna keyi da musa tana biye masa ga abinda yake bukata  sannan suka zauna tsuru  lawan direba yayi yana kallon daga inda yake  lamarinta yafi karfin tunaninsa yar muslima daita take irin wannan  rayuwar "?
   cikin wata irin kasala Musa ya riko laulausan tafin hannuta cikin nashi  yana murzawa a hankali tare da tsura mata Idanunshi itama tsura masa ido tayi har bata son kiftawa wani Murmushin jin dadi ya sakar mata itama bata san sanda ta sakar masa ba  " yaushe zamuyi aure ifemi  ?" ina son  muyi aure  saboda bana son wani ya kwace min ke dan jikina ya soma  bani saboda wannan kyaun da kikayi da wuya ace tun dawowarki wani bai ce yana sonki da aure ba, kinyi kyau sosai kamar wacce ta fado daga sama ya karasa maganar yana shafa saman kirjinta  kuma duk akan idanun direba daya dawo tamkar wawa a inda yake labe  yana lekansu wani irin yanayi ta tsinci kanta gaba-daya tsigar  jikinta  suka  mike  ta Lumshe masa ido tana sake jin kaunarsa "naji dadi sosai ifemi da kai yi nasarar hasashen abinda ke zuciyata ina son muyi aure very soon  "ya numfasa sannan yace "to da farko dai a shirye ni yanzu  nake damin abinda zan rikeki Allah ya hore min  aikina na bogilari  zai ishemu idan bai ishemu ba  ga karatunki wanda nasan saboda ni da yaranmu  kika yi shi " ta gyada masa kai alamun haka ne  maganarsa.  sun dade suna tautaunawa akan yadda zasu yi aure  daga karshe ta ciro dalolin kudi  masu  yawa  ta bashi "gashi kaje ka siya mota domin nan gaba kadan zamu daina haduwa a waje zaka dinga zuwa gidanmu  kamar  zai  hadiyeta dan murna sai da batun zuwa gidansu ya dan razanashi tare suka jero suna magana "ifemi ina jin tsoron nufar kofar gidanku "be a mana ifemi nima na tattara tsoro na watsar bare kai boye boye bazai kai mu ba gara asan muna tare "wannan kuma haka "dan haka ka sanyawa jikinki jarumta ka kuma cire tsoro muddin kana son aurena "angama ifemi ina alfahari dake  har jikin mota ya rakata  tare da bude mata ta shiga ya sanyo jikinsa ya kamo bakinta ya tsotsa  son  ranshi  sannan ya  fito ya rufe  mata murfin motar  ya hau machin  ya wuce tana jiran lawan  direba bayan yazo   suka dauki hanyar   gida  akan hanyarsu tace su wuce gidan hajiya aysha  da sallama ta shigo parlourn  Hajiya aysha  " a'a sakina ce ? Kisna tayi murmushi tana fadar "nice tunda baki zo  min sannu da zuwa ba gashi ni nazo nuratu jika ce ga granny diyar mace ce  ta fito daga daki a guje tana ihu murna suka rungume juna  da kisna hjy tayi murmushi "yar nema anki anzo din " nuratu  ta jata suka shige daki saman gado suka haye nan fa hira ta balle ta yaushe gano nuratu ta dinga bin kisan  da kallo har ta tsargu ta zungureta tana cewa "ya dai mutuniyar na canza miki ne da kike kallona "allahumarzukuni  fi miji na gari wallahi sakina kinyi kyau kin kuwa ga yadda kika hadu ?" Kisna taja tsaki in dai irin wannan maganar ce har tagaji da jinta a bakin mutane har ta dawo bata jin dadinta  nuratu  tace "ai kinyi ne wallahi ina ma namiji ce ni da wallahi sai na aure ki wata irin dariya kisna tasa suka tafa tace "gaskiya nuratu baki dama ana ta bata lokaci sosai sannan suka wuce gida haka duk bayan  kwana biyu zata shirya tace zata gidan hajiya aysha  alhalin  ba gidan   take zuwa  kai tsaye ba sai ta gama da musa zuwa  guraren shakatawa sai su dauki awanin kafin su rabu  sannan ta nufi gidan granny .
A wata  safiyar monday tafiya ta kama  muradi  zuwa Abuja kwananshi  biyu ya dawo da misalin karfe goma na dare  yana  sanyo hancin  motarsa unguwarsu idanunsa suka  ci karo da mugun abu domin kuwa  wata kyakkyawar fuska ya  hango cikin mota Camry  tana  manne da fuskar namiji da bai san kowaye ba suna tsotsan bakin juna da fari har zai  rage hasken motarsa  sai ya fasa  ya sake kara haske sai da  yayi kusa dasu sosai sannan ya fahimci kisna ce da Musa suke makake da juna suna shan bakin juna ,hasken fitilar motarsa yasa suka dawo haiyacinsu ta gefen motarsu ya wuce gabansa na faduwa sannan yana jin babu dadi tare da tausayin iyayenta sai dai ya kudurta bazaa ji komai a bakinsa ba yayi mata addu'a yayi hon aka bude masa ya shiga babu kowa a parlour'n ya shiga  ɗakinta mumy  bai ganta ba  da alamun tana dakin  dady ya leka dakin su zee tana kwance itama bacci take ya fito ya haura sama nan ma madu da Samir suna cikin kowane yana lamarin gabansa nan take ya fahimci rashin su a parlour'n ya bawa kisna damar fita a lokacin ya shiga wanka ya fito ya sauya kaya ya fito yana bawa mai gadi umarnin kar ta sake barin  kisna ta fita da zarar isha'i ta wuce yace "an gama dan albarka "

kisna na zaune dady yayi mata kyautar mukulin mota yace idan zataje gidan hajiya ba sai an kaita data mumy ba tayi farinciki tare da yi masa godiya ta fito haraban gidan  ta duba motar taga irin wacce take so ce 4mart ta dawo parlour'n da sauri "dady gaskiya ka burgeni yaakayi kasan irin motar da nake so ? "nifa babanki ne duk abinda zai min nasan zaiwa mamana ta rungumeshi ajikinta "thank you my dad Allah ya Kara budi "ameen kisna fatana ki zauna lafiya har zuwa sanda zee zata karasa karatunta a saida maganar aurenku ta sake rungumeshi saboda jin dadi ga dama ta samu da zarar an tambayeta miji Musa zata kawo ta sausata rungumar da tayi masa    "dady  kace akwai magana mai mahimmanci da zamuyi har yanzu ka min shiru "kaiki damu nan kusa zan yi miki fatan bazaki zuba min kasa a ido ba ? ta girgiza masa kai ya shafa fuskarta tare da nufar hanyar step ..."
A cikin wannan satin direba ya tuka kisna  zuwa gurin musa sun dauki lokaci sosai basu dawo ba har  dady  ya dawo  gida ya   kira direba   a waya ya tambayesa  inda suke  yace  "suna wani guri  a ogba yayi shiru ya  kasa cewa komai sai wajen karfe takwas da wasu mintuna  suka dawo  gidan  tayiwa mumy sannu da gida ta shige  daki  ta afka  toilet mumy ta mike ta fito dady dake tsaye a bancoly dinsa ya mike ya sauko kai tsaye haraban gidan ya nufa ya kira direba "karka boye min komai ina ka kai kisna yau ?"direba bai boye masa komai ya fada masa gaskiyar inda yake kaita a duk sanda suka fita da zumar zuwa gidan hajiya aysha dady ya zuba masa ido kawai yana kallonsa yana jin wani zallar ɓacin rai na ratsashi hawaye na bin kuncinsa ji

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login