Showing 105001 words to 108000 words out of 495987 words
Chapter 36 - Cutar Kai Book Complete Hausa Novels by Aysha Bagudo.txt
haroon sake fitowa saboda tsadaddun kayan da yake sakawa jikinsa ya famtama gari gurin abokai , duk sanda uncle garba yayi masa maganar aiki kuwa ranar babu zaman lafiya a gidan ya dinga nunkurfici kenan yana cewa "shifa ba zai iya harkan canji ba ci baya ne agurinsa dan ba zai iya tsayuwa a bakin titi yana kiran mutane suna masa wulakanci ba su da sukaji zasu iya su cigaba da tsayuwa akan titi bai zai hanasu ba amman shi bazai iya ba , iya gata hajiya kayi ta nunawa haroon , duk abinda yake so tana masa saboda kasancewarsa mai sunan kanin mahaifinta kuma shi ya riketa har aure tana ji dashi sosai .."
" Mahaifina kuwa asalin iyayensa yan kano ne a karamar hukumar kiru , sai dai shima zama ne ya kawo iyayensa lagos , anan cikin garin lagos aka haifeshi a unguwar agege shi da sauran yan'uwansa ,kakana na gurin uba alhaji lukman shararraren mai arziki ne wanda sunansa ya shahara a jahar lagos sannan ya karad'e sauran garuruwan dake cikin nigeria kasancewarsa ɗan siyasa , Alhaji lukman yana da tarin ya'ya da yawa wajen su a shirin da shida ya haifa , ya mallaki maza da mata ,maza shabiyar mata goma amman gabad'ayansu kansu a haɗe yake duk da wasu daga cikinsu sun mutu sauran ashirin a raye , mahaifina yana da yawon yan'uwa sai dai yawansu bai sa kansu ya rabu ba , hakan kuma ya samo asalin ne agurin mahaifinsu shi ya haɗa kan ya'yansa ,hakan yasa yaran suka taso kansu a haɗe cikin tsananin son juna babu ruwansu da wannan uwarsu ɗaya ubansu ɗaya, wannan uba daya ne , suma haka zalika iyayen ma kansu a haɗe yake haka ma jikoki muna matukar qaunar junanmu .."
" mahaifiyata salaha da mahaifina Alhaji realwan sun haɗu ne a wani zuwa bikin abokinsa idiaraba soyayya mai karfi ta shiga tsakaninsu ,sunyi aure bayan gwagwarmayar rayuwa da mahaifina ya sha kafin mahaifin mahaifiyata Alhaji sani ya yarda da aurensu a cewarsa ba zai ɗauki tilon diyarsa mace ya bawa bare kuma yare da ban ba zarma d'an'uwansa ba , dan asalin zarma basa bada auren ƴaƴansu ga wani yare baya ga yarensu bisa nasu ra'ayin ,dan har yanzu ba kowane bazabarme ke daukan ya'yansa mata ya aurawa bahaushe ba , sai dai zabarmawan dake zaune a garin lagos suna kokarin su bawa bahaushe idan sun san asalin daga ina yake kuma sun san halinsa amman yawancin na kauye basa bada yaransu saboda suna ganin hausawa basa rike aure ga saurin saki , har yanzu har kwana gobe ba kowani zarma ke daukan d'ansa ya bawa bahaushe ba sai dai su kan yarda ƴaƴansu maza su auro ya'yan hausawa mata ."
Tun bayan da'akayi auren iyayena Allah bai nufesu da samun haihuwa ba sai da suka kai kimanin shekaru goma da aurensu sannan Allah ya basu haihuwar ya badamasi , yayinda a wannan lokacin tuni uncle garba da uncle bature sun yi aure kuma a rana daya kuma duk yaren zarma suka aura mazauna Idiaraba .
bayan bikinsu bada jimawa ba hajiya kayi ta koma ilo da zama ita da mijinta kasancewar girma ya soma zuwan musu wanda kusan al'adar zamar ne basa karashe rayuwarsu a wani guri sa'banin garinsu na haihuwa , duk yadda suka kai ga neman kudi aguri da zarar girma yazo musu zasu tattara su koma jaharsu su cigaba da rayuwa ..."
A wannan lokacin kamar yadda muka samu labari uncle haroon bai bi bayan iyayensa zuwa ilo ba acewarsa mai zai yi a kauye babu wuta babu network babu jin dadin rayuwa tsakaninsa da kauye sai dai kallo ya tattara ya bi wani abokinsa farhan zuwa jos ,duk sanda mommy taje ilo gurin mahaifiyarta dan kai mata ziyara ta dinga mata kuka kenan akan uncle haroon tare da bar mata wasiyya iri iri akanshi , "Idan garba da bature sun juya masa baya salaha karki juyawa d'anuwanki baya " ina son babakarami tamkar raina ,dan Allah kema ki so shi kamar yadda nake son shi ki janyosa jikinki ko bayan raina idan Allah yasa ya dawo kuka hajiya kayi keyi sosai wanda har yasa mommy kuka suka rungume juna gam suna kuka yayinda Alhaji sani yayi shiru yana Kallonsu cike da takaici da bakinciki dan duk tautaunawarsu yana shiga kunnuwansa , kuka suke kamar ransu zai fita , cike da zafin zuciya alhj sani ya tako zuwa inda suke rungume da juna ya fara magana cikin zafin zuciya yana cewa" momy karki kuskura ki ɗauki maganar mahaifiyarki da mahimmancin da zai sai ki damu rayuwarki akan takwaran Alhaji dan ko ya dawo garemu bashi da muhalli acikin gidan nan, ban ciresa a cikin ya'yana ba amman na ciresa a cikin zuciyata dan bazan amshesa ba ,ba dai yana gudun zama damu bane saboda bamu da arziki yaje duniya ce gashi nan gata wanda bai zo ma tana jiransa "hajiya kayi ta zabura ta mike tsaye tana fuskantar shi cike da mamakin jin furucinsa sannan tace "saboda me zaka fadi haka alhalin d'anmu ne babakarami bashi da iyayen da suka fimu ",ana ki tunanin ba ai shi bai daukemu a matsayin iyaye ba , kafin kace me gurin ya hargitse da magana da rudani tsakanin hajiya kayi da Alhaji sani zuciyar hajiya kayi ta tsinci kanta cikin rashin natsuwa da jin hukuncin mijinta , ranar tamkar mutuwa akayiwa a gidan mommy da hajiya kayi babu abinda suke sai aikin zubar da hawaye yayinda shi kuwa a lokacin haroon yana can yawon duniya bashi wannan gari bashi wancan gari duk garin da yasan zai ji dadi zashi ,kullum kuma cikin samun sabbin abokai da yammata yake kuma har wannan lokaci mata basu daina kashe masa kudi ba , a hankali har ya shiga harkan neman mata da smoking kamar yadda momy ta samu labari mata na biyansa kudi dan ya kwana dasu , ranar kuwa momy tayi kuka tamkar ranta zai bar gangar jikinta bata fadawa kowa ba ranar da zazzaɓi ta kwana a jikinta ta aika masa sako ya dawo gida ya bar harakar da yake duk abinda yake so zata masa amman yaki yace shi yanzu bazai iya rayuwar gida ba ..."
Numfashi kisna ta sauke a lokacin data zo nan sannan ta fuskanci safy fuskarta cike da tsananin damuwa tace "a iya nan zan dakata bazan iya cigaba da bakin labarin ba saboda akwai wani boyayyen sirri akan ya aliyu ba kuma zan so wannan sirrin ya fito daga bakina ba ta karasa maganar wasu hawaye na gangaro mata safy ta numfasa tace ,"to ai baki faɗa min yadda kuka yi aure da Aliyu ba dangantakanku kawai kika fada min ni rayuwar aurenku nake son ji " "Muddin zan faɗa miki yadda muka yi aure dashi dole zan bayyana wannan sirri " .
murmushi safy tayi sannan tace" kisna kenan ba dai zurfin ciki ba sai naji kin sake shiga raina ina matuƙa son mutun mai rike sirri wanda samun irinku yanzu kuke da matukar wuya, kisna ta gyada mata kai kwayar idanunta na kallon sama dan ita kaɗai tasan yadda take jin zuciyarta a hankali ta mayar da idanunta zuwa ga safy ta cigaba da magana "ciki ba'a yisa dan abinci kawai ba duk mutumin daya kasa rike sirrinsa karka yi tunanin zai iya rike na waninsa ta karasa maganar hawaye na sake gangarowa daga cikin kwarnin idanunta "wannan magana taki haka take amman naso naji yadda kuka yi aure da Aliyu gaskiya " parlou'n ya d'auki shiru babu wanda ya sake yin magana har aunty zee wacce ke aikin mayar da kayan lefe cikin jakunkuna, " Kisna kiyi hakuri ki daina kuka bana son ganin hawayenki yana sani jin wani iri wallahi "ai indai kisna ce yanzu haka take abu kankani ke sata kuka saɓanin da ta mike ta karaso kusa da kisna ta rungumeta suna kukan tare wani abu ya tokare makoshin Kisna dan komai daya faru ya shiga dawo mata daki daki suna cikin kukan muradi ya shigo parlou'n ya iske su
cikin wannan halin suna kuka safy na basu hakuri saurin katse sallamar yayi daidai lokacin da aunty zee ke magana murya can kasa tana gogewa Kisna hawayen " .
kyawawan idanunshi masu matukar kyau da haske ya sauka akan kisna dake zaune tana matso ruwan hawaye tamkar wacce aka yiwa mutuwa tare da kare mata kallon tsab idanunta sun canza daga fari zuwa kore , a hankali ta d'ago idanunta suka hade da nashi wani irin mummunar faduwar gaba taji ,take gaba-daya ilahirin jikinta ya dauki rawa lokacin da kwayar idanunta ya haɗe da nashi kallonsa kaɗai nasata jin abu biyu a lokaci daya, faduwar gaba tare da alfahari kasancewarsa uban ya'yanta .
kusan minti biyar ya dauka tsaye a bakin kofar dakin yana Kallonta sannan ya soma takowa a hankali yana mata kallon kasan ido ,nazarin yanayinta yake, wannan yanayin daya gani a tattare daita yanayi ne na damuwa dan kuwa idanunta sun tabbatar masa da haka guri ya samu ya zauna akan kujera yana kallon safy dake faman zuba sannan yana kallon kisna ta gefen idanu muryarsa a kasalance ya soma magana cikin tsigar tsokanar safy "ya kika ga kayan amaryarta sun bugeki ko "?"Sosai kuwa duk sun burgeni sai dai gabad'aya kayan sunfi dacewa da kisna ba wannan mai kama da busashen bishiya ba, ko ka taba ganinta da irin wannan waɗan kaya"?ta karashe maganar cikin tsigar wasa tare da yunkurawa ta tashi "wannan kuma son ranki kika faɗa saboda kina da wata manufar munafurci a ranki ai sai na zuga mijinki ya qara aure " kalmar munafurcin daya dangantata dashi ya mugun bata rai murmushin takaici tayi tana rataya jakarta "kai ma daka hakura mai mata kamar kisna mai zai yi da wata nawal din banza mai siffar munafuka "? Ta fada tare da nufi kofar fita tun kafin ya antayo mata bakar magana data fi na farko tana cewa "sai anjimanku " aunty zee ce ta mike tayi mata rakiya har haraban gidan kalmar ta bala'in bata masa rai zuciya tazo wuya a hankali ya dinga girgiza ƙafarsa daya ...."
Kisna ta mike tsaye ta karasa inda yake ta durkusa muryarta cike da rauni tace "sannu da zuwa " ta'be baki yayi batare daya amsa mata ba , bata damu da rashin amsawarsa ba tunda idan da sabo ta saba da halinsa .
ta soma cire masa canves din dake sanye da kafafunsa hawaye na ziraro mata sanda ta karasa cire masa kafafunsa ya saura da safa kawai , ita kanta aunty zee data dawo parlou'n ta ganta durkushe a gabansa kasa daurewa tayi sai da wasu suka qwalla zubo mata ta kawar da kanta tare da danne abinda taji bawai shishige masa da kisna take bane yafi damunta irin banzatar da rayuwarta da yake kai tsaye juyawa tayi ta nufi kofar fita tana goge hawaye "zainab ya kira sunanta muryarsa a dake cike da ɓacin rai tsayawa tayi cak batare data juyo ba "kowa murna yake akan auren nan da zanyi banda ke da wannan yar iskar me yasa kika manta abinda yar iskar nan ta aikata ga rayuwata kunnuwan Kisna suka jiyo mata sautin muryarsa yana fadar haka a can kasan makoshi , kamar ta cigaba da durkuso a gabansa ta cigaba da sauraronsa tare da rarrashinsa da bashi hakuri sai zuciyarta ta haneta dan haka ta mike hannuta rike ta canves dinsa tana kokarin hawa sama kamar zai mata magana sai kuma ya fasa ya cigaba da magana "wallahi kina biyewa son zuciyarki dana wannan abar sai dai bata isa bakincikinta ya kasheni ni kadai ba kamar yadda taso faruwar hakan kafin taga mutuwata ina tabbatar miki ni ne zan soma ganin nata duk da nima nasan bazan cigaba da zama ba amman wallahi tallahi ba zan barta tayi rayuwa mai dadi ba ina nan akan bakana har sai nayi magani iskancin data min numfashin Kisna ya soma fita da sauri da sauri , ta kasa cigaba da daga kafafunta aunty zee ta gigice ta juyo tana kallonsa cikin tsananin damuwa itama Kisna ta juyo tare da tsura masa ido canves din hannunta ya subuce shima kallonta yake cikin tsana muryar a zafafe Kisna ta soma magana cikin kunar rai "kai cika mutun mara imani hakika na soma danasanin kasamcewa mata kuma uwar yayanka a rayuwata ,alfaharin da nake na kkasancewarka ubansu Aryan reef da janye domin sun yi hasarar uba wallahi ,kasani wani bakincikin ne dabam zai kasheni ba sanadin ciwon zuciyar da kake kokarin haifa min ba kuma duk abinda kake yi Allah yana kallonka zai saka min sannan auren nawal da kake ganin yana cikin bakinciki da zaka kunsa min wallahi ko ajikina saboda banga abinda zai sa na daga hankalina akan matar da tsinannu kadangarun bariki suka gama da rayuwarta yar iska da kowa yasan ba yar mutunci bace kawai bakar zuciyarka ce ta hanaka ka fuskanci komai ni kuma da kake kira da yar iska duk iskancina ban bari yan iskan kadangaru bariki sun .........."
shiru tayi sakamakon toshe mata baki da aunty zee tayi tana girgiza mata alamun tayi shiru saurin cire hannu aunty zee tayi a bakinta "ki bari na fadi abinda ke raina ta yaya zai dinga dangantani da kalmar iskanci wallahi duk matakin da kake shirin dauka akaina ka dauka amman ka kwana da sanin cewa Allah bazai barka ba saboda ina da hakki akanka kuma babu inda Allah yace dan nayi maka laifi ka tauye hakina daya rataya a wuyanka ya mike a zuciye yayi kanta yana huci ya daga hannunsa zai doketa yana auna mata zagi aunty zee ta kare "haka zaki kare cikin tsananin bakin ciki a gida nan rayuwar farinciki sai dai kiga ana yinsa a wani gida .."
"da ikon Allah sai Allah ya kunyataka, karewa cikin bakinciki tana gurinka mutumin da baya yafiya tunda har nadamata bata sanya kaji zaka iya hakura da abinda nayi ba hakika zaka ga yadda rayuwa zatayi da kai hakina dana yayana bazai barka ka zauna lafiya ba aunty da zee ta rikesa gam da hannuwanta duka tabashi hakuri saboda jikinsa dake tsuma da kyar ta samu ya zauna yana huci duk cikin maganganun ta babu wanda ya taba zuciyarsa da tsaya masa arai kamar kalmar data danganta nawal daita take gumi ya rufeshi gabadaya ya nemi natsuwarsa ya rasa ji yake kamar zuciyarsa zata buga a yanzu da ya soma jin soyayyar nawal na dan shigarsa shine zata fadi mummunar kalma akanta yasan tayi haka ne dan kawai ta bakanta masa amman bazai yi sakacin da zuciyarsa zata amince da kalamanta ba,cikin tsananin zafin rai Kisna ta juya cikin sauri ta hayewarta sama zuciyarta kamar zata buga ,itama aunty zee ta fita ko dan rarrashin data saba yi masa a duk sanda ya hau sama bakinciki yasa ta kasa sannan taki masa magana akan yadda za'a yi da kayan lefe dan nan ta barsu yasan yadda zai yi dasu ai ta gama mai wuyar , duk yadda zuciyarsa taso ya yarda da kalaman Kisna akan nawal kin yarda yayi domin ganinsa yana yin nasara akan komai dan tun daya taso yake samun nasara arayuwarsa yana da tabbacin zai yi nasarar samun nawal cikakkiyar mace a gidansa kamar yadda ya saba nasara dogon tsaki yaja wayarsa dake qara ya ciro yanayin yadda ya soma magana kasan shi da mommy ne.."
Tana tsaye a dakin tana datasanin abinda tayi ya shigo dakin yana cire yar saman rigarsa ya ajiye akan gado ta karasa zata tayashi cire sauran ya dakatar daita yana zabga mata harara taja ta tsaya tana kallonsa ta madubi gabanta na cigaba da faduwa ",sannu tantiriya Kinga ma ci min mutunci ke da wancan yar rainin hankalin yanzu shine ɗan iskanci zaki wani nuna ke mutuniyar arziki ce yayi maganar yana ajiye rigar akan wanda ya cire ya ɓalle agogon diamon din dake daure a tsintsiyar hannunsa ya ajiye "bai kamata kaji ciwo ba , babu inda maganata ta shafi ta safy data biyayyar aurena da kai ,magana ka fada na baka amsa daidai da maganarka meye abun