Showing 147001 words to 150000 words out of 495987 words
Chapter 50 - Cutar Kai Book Complete Hausa Novels by Aysha Bagudo.txt
riketa na tsawon shekaru batare da nemi inda muke ba "ya Allah ka tsare min rayuwarta da lafiya a duk inda take kasa ta dawo garemu muna tsananin bukatarta a hankali ya tsurawa diary din hannunsa rinannnun idanunsa wadan da suke shatatar da hawaye gani yake kamar fuskarta zata bayyana ajikin bangon diary ransa gurin baccinsa ya koma ya kwanta rungume diary ....."
Bayan kwana biyu
da wuri mumy ta tashi ta nufi kitchen domin haɗawa dady da yaranta breakfast shi kuma dady ya shiga wanka ta shirya dinnig table ita da kisna tana wasa da dariya da tsalle tsalle,dayan bayan daya yaran suka dinga shigowa sanye da uniform ajikinsu suna durkusa wa har kasa domin gaishe da mummy a daidai lokacin da dady ya fito cikin manya kaya shadda fara sol da babbar riga da hula kalar kayan kasancewar ranar juma'a ce , nan suka juya zuwa gurinsa har kasa suka durkusa kan muradi na kasa ya gaishe dashi cikin sakin fuska ya dinga amsa musu tare da saka musu albarka yayinda kisna ta makale ajikinsa tace "dady ina kwana dady yace "lafiya lau sarkin rigima "me ka siyo min jiya daka dawo"? "na siyo miki fura "to ai Ni bana son fura nafi son sweet "ai itama furar dana siya miki tana mota na manta daita "muradi ungo key kaje ka daukowa iya rigimar nan fura ya amshi key kansa na kasa cike da girmamawa ya fice ta kalli dady tace "idan ya dauko bazan ba yajita amman yayi kamar bai ji ba har muradi yaje ya d'auko ya dawo ya mikawa Kisna taki amsa tare da turo baki tasa hannu ta buge goron fura tana furta "bana sha tunda ya taɓa haushi ya kama mumy ta kai hannu zata ɗauketa da mari muradi ya ɗauketa cak ya dagata sama "mumy wannan daga hannu kamar zaki mari babba mamanki ce fa ?" Wallahi idan kana biyewa Kisna zan bata maka rai ,muradi zan ajiye matsayinka a gefe naci mutuncinka fa "kiyi hakuri afuwa mumy "ni ka saukeni banaso ta soma mutsu mutsun sauka ajikinsa aiko Samir da madu suka kama masa da dariya tare da cewa "Allah shi kara ai maganin mai tausayi irinka kenan da kabari an nada mata duka da yanzu ta shiga hankalinta "bazan bari a daki Hajiya kayi ba yayi maganar yana sauketa "ai ba asalin ita bace suna ci dan haka duk tayi ba daidai ba sai an hukuntata dady ma dungure Kisna kai yayi "idan kina yiwa muradi haka zan daina siyo miki komai har suka karasa breakfast dady fada yake yiwa Kisna yayinda afra dan haushi kasa cin abinci tayi ta tsani ana nuna wa muradi kulawa ."
"aliyu dauko min takalmina ka goge min cewar dady har Aliyu ya mike da sauri mummy tace "yi zamanka muradi na goge masa , dady yace " Allah yayi miki albarka taje ta d'auko ta ajiye masa takalmin kusa da ƙafafunsa , a hankali yayi magana a daidai kunnenta "duk wani launi na soyayya kin iya kama namiji dashi salaha ". tayi dariya batare da tace koma ba saboda idanun yara, amman a ranta cewa tayi ai mata ne ke janyowa kansu kishiya , idan mace zata kama mijinta ai babu zance kishiya ,Amman sai kaga amare acikin gidansu kamar wasu jakuna wata ma sai ta kwana biyu jikinta bai ga ruwa ba kayan da kaganta dashi yau gobe shi zaka ganta dashi ,idan kuma ta dade da aure sai ta bari yaya su hanata yiwa miji kwaliya da kulawa da lamirinsa, ta kalli kyakkyawar fuskarsa "dady tashi muje na rakaka dan tasan idan tayi wasa zai bata lokaci , ya mike suka jero "ka ta sani gaba baka son zuwa kasuwa ko ?
"au korata ma kike yi "haba Ni na isa idan kuma zama zakayi muje sitroom nan idanu yara na kanmu "bari na wuce yau juma'a kuraren lokacin ne da wuri zan dawo na soma shirin barin kasar gaba-daya ki huta
Tayi murmushin gefen baki suka ci-gaba da tafiya tana rike da jakarsa da wayoyinsa , ta rakashi har bakin motarsa ya shiga direbansa ya karaso da sauri ya gaisheta cike da girmamawa suka bar gidan ,ita kuma ta dawo ciki dan ta sallame yaranta ,bayan ta sallemusu ta sake kintsa ko'ina ta dafa musu taliya ta zuba a kula sannan ta shige d'akinta ta yi wanka ta kwanta dan ta huta .
*******
Washegarin ranar asabar tun karfe tara muradi da Samir suka shirya zuwa gurin wasan kwallo ,koda suka isa abokansu gaba-daya sun hallara kusan su kadai ake jira ,suna gama k'arasowa kowanensu ya sha ruwa kadan kadan sannan suka fara gaisawa a tsakaninsu suna hirar yadda wasan zai kasance "karka damu jahid yau mune zamuyi nasara inji cewar habib shi dai muradi yana tsaye rungume da hannuwansa a qirji batare da yace komai ba har sanda aka tara su gabadaya acikinsu aka zabi leder guda biyu muradi da Samir domin duk sunfi sauran kwarewa agurin iya buga kwallo aka ajiye takalmi a tsakiya "muradi ina kake so "? Cochi ya tamabaye muradi yana kallonsa cike da farinciki muradi ya nuna inda yake so shima Samir ya nuna inda muradi ya nuna ,ya jefa takalman guda biyu sama suka dawo kasa daya ya kifi daya ya bude wanda ya bude shine na muradi Dan haka muradi ne ya dauki bangaren dama ,daman kuma koda yaushe nan yake ɗauka cochi ya fara cirowa muradi mutanensa ya bar wasu a waje haka ya dinga jerasu har aka fara wasa karon farko muradi ya lashe ,aka cigaba da wasa wasa muradi da members dinsa suka lashe su Samir kamar koda yaushe ,cike da fara suke gaisawa a tsakaninsu muradi ya rungume Samir ajikinsa "kafa yi kokari sosai kawai dai kasan aliyun naka ne sai hankali shima murmushi yayi yana shafa bayansa a hankali ya zare jikinsa jahid ya bashi hannnu "gaskiya ka buga kwallo yau sosai sai dai ban ji dadi yadda kasa min kafa ba "karka ji dadi bayan ka cinyemu da me kake son naji ai ina sane nasa maka kafa jahid ya fada yana dariya suka fara saka kayansu habib yace "ai next time mune zamu cinyeku "."Ku shirya da kyau kafin ku fito Aliyu ya fada yana takunsa cikin isa da izza ."
Mmn sudais
[7/19, 5:32 PM] +234 803 631 5951: 💗💗💗💗💗💗
CUTAR DA KAI
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
Page 25
~TRUE LIFE STORY~
*PAID BOOK*
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
bismillahirrahmanirrahim
"Wannan littafin na kudi ne ,mai bukata karanta shi zai tura 500 ta wannan account number din 1438775094 Aishat Abdullahi Access bank ,Idan an tura sai a turawa wannan number alert +234 803 238 4602 domin tabbatar da an tura , ko wannan number 08059623096 Idan Kuma vtu za'ayi sai a tura ta wannan number 08059623096 ,kada ayi vtu a number MTN sannan kada a Kira number mtn ba'a kira dashi only chart ne . "domin sauraran littafaina sababbi da tsofaffi za'a iya tuntu'bar Channel dina ta Hausa bakwai,sannan muna bada sarin Lagos lace da kamfala ,Lagos rapa , jaka da takalma, getzner na cotonou da chiganvy, volyal lace duk akan farashi mai sauki ,ga mai bukatar siyan ɗaya ko sari yayi magana ta wannan number 08059623096.
Tsuke karamin bakinta tayi tana kallonsa , ganin yaki ɗauke idanunsa akanta yasa ta ajiye ice cream din dake rike a hannunta tasa masa kukan shagwa'ba ,a rud'e ya kamo tafin hannunta cikin nashi yana murzawa a hankali yace "menene my queen "? "Me ya saki kuka "?"Ba kai bane kake kallona nifa bana son yawon kallo ......."
dariya ya badamasi yake tayi a cikin zuciyarsa a tun sanda ta motsa karamin bakinta dan yasan muddin yayi a fili zai ballowa kansa ruwa dan sake birkice masa zatayi "my eshat kin cika shagwa'ba da yawa ban da abunki meye abun kuka akan na kalleki bayan nan gaba kaɗan ma zaki za.. ....
Saurin katse abinda yake son fada yayi cikin tsarkewar murya ," kallo ma tayi masa kuka ina ga ya fadi abinda ke ransa ,ai sai ihu kenan zata saka da kururuwa neman ɗauki , ya cigaba da murza yatsun hannunta yana kallonta "kaga ya badamasi banason abinda kake min ta zare hannunta cikin nashi tana sake rushewa da wani sabon kuka "
"ya Salam meye kuma abun kuka anan daga taɓa hannu,"ni ka daina ummana tace kada na yarda na bari maza suna taɓa min hannu , idan ba haka ba zanyi ciki gashi ni bana son nayi ciki ina yar yarinyata " da kuka ta karasa maganar.."
kuka take sosai kamar wacce ake zarar ranta ganin haka yasa hankalinsa ya tashi matuka "kinga nifa ba wani abu zan miki ba wasa nake miki , kuma rikon hannunki da nayi bazai sa kiyi ciki ba oya kiyi shiru karbi wannan , wani kyawawan hankchif fari sol ya mika mata yana sake tsareta da idanunsa "plz wipe ur tears my queen I don't want to see ur tears Karki min hasarar hawaye ..."
Shiru tayi tana sauraronsa dan bata da niyyar amsa hankchif din , ganin haka yasa ya aje mata akan cinyarta yana rarrashinta "kiyi shiru ki goge hawayenki kukan ya isa haka bazan sake ta'baki ba shikenan ".Cikin sheshekan kuka tace "Allah ya badamasi bana son ana taɓani "to naji na daina sarkin rigima da shagwa'ba dauki ice cream din ki sha".murmushi ta sakar masa yayinda take kokarin share hawayenta "shiru yayi yana Kallonta kasa kasa yana jin yadda zuciyarsa ke sake narkewa akanta saboda kyawun data sake yi masa a lokacin da take kuka , a hankali yace "kinga kyan da kika qara kuwa lokacin da kike kuka? "ni ka daina ganin kyauna banaso tayi magana tana turo masa karamin bakinta saurin zaro ido yayi waje "ai kuwa baki isa ba yarinya ya furta acikin zuciyarsa tare da gyara zamansa "kallo kam yanzu na fara afra har zuwa lokacin da zan mallakeki ,"kana magana ne "?Ta tambaye sa tana shan ice cream ya girgiza mata kai alamun "a'a"har ta gama shan ice cream din yana kallonta yana zolayarta , wani abun tayi dariya, wani ta saka masa kukan shagwa'ba har karfe shida ta buga suna tare sannan ya jata zuwa inda su aunty ummi Zahra, mufida madu da Samir suke daukar hoto rungume da kisna da tuni tayi bacci a kafad'an aunty ummi " idan kun gama muje ko "?
"Mun gama " gabad'aya suka haɗa baki "kun gama a ina to ni ban gama wallahi afra ta faɗa tana turo karamin bakinta gaba duk suka zuba mata ido suna Kallonta cike da mamaki . "zaki zo da wahalar kenan ko ? inji cewar madu "ai kai ne wahalallen tayi saurin dakatar dashi ,kun wani zo nan kuna ta ɗaukar hoto ko a samu wanda zai kirani ai nasan duk sharrin wannan ne ta k'arasa maganar tana nuna Samir "sannu gimbiya saboda ana jin tsoronki ne za'a zo kiranki alhalin kinsa hakan zata iya faruwa dole idan anzo za'a yi hoto , ke da kika san kina son d'aukar hoton me yasa kika ....."?
"Ya isa abar maganar haka inji cewar ya badamasi zo nayi miki hoto my queen ya ciro wayarsa iPhone xx max , tabe baki Samir yayi tare da cewa " yar wahala kawai ke dai idan baki ja mutane faɗa ba bakya jin dadi yar rainin hankalin kawai ". hotuna sukayi sosai daga karshe tasa ya badamasi ya siya mata wani ice cream ,Samir ya dauki ice cream mai chocolate da kayan motsa baki "bari na d'aukarwa muradi ".da sauri ta matso kusa dashi ta tsaya "ka jika da iyayi yana son sha me ya hana shi zuwa "?"Ina ruwanki da rashi zuwansa ko kice zakiyi kayansa zuwa gida"?Tace "kai ne zaka yi kayansa amman dole nayi magana tunda bakina ne ta fada tana yatsina fuska "to babu ruwanki dani idan ba haka ba zamu raba hali yanzu anan "to mu raba mana sai me tsoronka nake ji "?"Kufa gayawa yarinyar nan ni ba sa'anta bane idan ta raina kowa karta ce zata rainani ..."
ya badamasi ya riko mayafinta
"muje my queen Samir fa kaninki ne ki daina biye masa fixge mayafinta tayi tana masa wani kallo "ta ina ya zama kanina bayan akwai wattanni a tsakaninmu ya bani wata biyar fa ta karasa maganar tana nuna masa yatsunta biyar "naji ni ba wannan nake nufi ba idan lokaci yayi zaki fahimci abinda nake nufi ya sake janta Suka nufi inda motarsu take Suna shiga haraban gidan ranta yayi bala'in ɓaci saboda cin karo da fuskar muradi da tayi cikin shirin zuwa masallacin sanye cikin jallabiya baka kafin ya karaso inda motar take pake ta jefa masa wani mugun kallo tana harararsa tare da jan tsaki ta runtse idanuwanta saboda bata kaunar ganinsa a rayuwarta ya ɗan tsaya yana jiran fitowar Samir ta fito daga gaban mota tana yatsina fuska haka nan taji zuciyarta ta bugu lokacin da tayi kusa dashi ".
Aunty ummi ta fito da kyar muradi ya mika mata hannu alamun ta miko masa Kisna "yauwa muradi dan Allah kai ta dakin mumy suka jera tare da Samir yana fada masa yazo masa da ice cream kai tsaye dakin mumy suka shiga ya kwantar daita akan gado ya cire mata takalmi dake sanye a kafafunta Samir na bashi labarin inda suka je suna ƙoƙarin fita daga dakin mumy ta fito daga bayi tace "yauwa muradi zo nan kai kuma Samir kira min ummi har da madu ma ya fito cikin sauri tare suka dawo Mumy ta kalli muradi tace "abinda nake son fad'a maka duk inda kaga kawunka garba ko bature Karka kallesu bare su ganeka , kuma bance ku fadawa wani daga cikin dangina dake garin nan cewar an ga muradi ba " gaba-dayansu suka gyada mata kai alamun sunji "oya kuje kuyi sallah suka fita ummi ta nufi dakinsu su kuma suka wuce massalaci ."
karfe bakwai daidai duk suka hallarar a parlour Samir ya mikawa muradi roban ice cream din daya zo masa dashi ya amsa ya bude yaga ice cream din ya narke duk yayi kunfa daga sama ,Samir dake zaune gefensa ya leka cikin roban saurin dafe goshinsa yayi "ya narke ko ? amman banji dadi ba wallahi shi yasa nace kasha kafin kaje massalaci kaki". ita kuwa afra ranta fesa da jin abinda Samir yace "Allah ya qara ai ka iya gulma da iyayi gara daya narke naga karya sha ta mike daga zaunen dake ta shiga Zariya a cikin parlour'n tana jin dadi saboda hango ɓacin rai mai tsanani a kwayar idanun muradi,a hankali muradi ya ajiye roban ya tashi ya bar gurin ya koma dakinsu yana danne zuciyarsa dake masa zafi yana da tsananin hakuri amman zuciyarsa bata daukar wulakaci, yana da juriya amman kuma yana da taurin kai mai tsanani akan abu , idan ya kafe akan abu ko me zai faru sai dai ya faru amman bazai rusuna ba shifa akan afra za'a iya nemansa a rasa gara yayi rayuwarsa a wani bagiren da bai da kowa kuma babu wanda yasanshi zai fiyye masa kwanciyar hankali hawaye ya zubo masa saboda baya qaunar rayuwar waje kullum zuciyarsa na cike da tarin bakinciki rashin sadiq a kusa dashi baya son wannan yawon da yake " Samir ne ya shigo dakin yaga ya haɗa kanshi da bangon dakin yana sheshekan kukan zuci dana zahiri dan yana hango yadda bayansa ke motsawa , ya zuba wa bayansa ido kafin daga baya ya karaso gurinsa ya dafa shi tare da juyo dashi suka fuskanci juna muradi ya tsura masa ido yana huci qirjinsa har dagawa yake , tsawon mintina ko motsi bai yi ba bare a saka rai zai yi magana illa dauke hawayensa da yayi ,a fusace Samir yace "wai bazaka takawa yar iskar yarinyar nan burki ba ta fita harkarka dan fa taga kana kyaleta ne kazo muje kaci ubanta ya janyo hannun muradi yana ƙoƙarin fita daga dakin amman fur muradi yaki takawa ya tsaya Samir ya juyo ya zuba masa ido cikin ɓacin rai "ka kwantar da hankalinka Samir ni gidan ma zan bar mata rayuwata bata son yawon damuwa "idan ta isa tasa ka bar gidan nan shege nake ai ba da kudin ubanta a gina gidan nan ba bare ka barshi saboda ita," itace zata tattara ta bar gidan ta koma gidansu ka daina raga mata yar iskar yarinya ce wallahi , baka ga tunda naci ubanta muka dawo daidai daita ba , muradi ya sake tsurawa Samir ido a zuciyarsa yace "bazan iya cacar baki da mace ba bare dambe tsakanina da mace ido ne , Samir ya dade yana rarrashin muradi ganin yadda ya shiga damuwa yasa muradi yace "zan zauna darajan wannan soyayyar da ka nuna min kadai ta hanani aiwatar da abinda zuciyata ke gaya min akan zamana a gidan nan rungumeshi Samir yayi yana sake jin kaunar muradi a ransa ."Kowa a gidan yana ji da auta Kisna da sun dan samu dan canjinsu akanta yakarewa , shima muradi yana son daukarta dan Allah yayisa