Showing 108001 words to 111000 words out of 495987 words

Chapter 37 - Cutar Kai Book Complete Hausa Novels by Aysha Bagudo.txt

daukar zafi? "shiyasa fa idan baki yasan abinda zai fada bai san abinda za'a maida masa ba idan baka son ina fada maka babu dadi akan komai kaima ka canza dan Allah ma daya haliccemu  muna saba masa kuma mu dawo mu rokeshi ya yafemana bare mu yan adam yakamata ka canza ka manta abinda ya faru mu rungumi rayuwarmu idan kuma rayuwar daka zaba mana kenan shikenan sai mu cigaba tunda ta soma magana bai kulata ba haka bai dago ya kalli inda take ba  zai shiga bayi  tace "ranka shi dade akawo  coffe ko akwai abinda  kake .. ....?"
Bai  tsaya  jin abinda zata fada  ba ya shige bayi ya rufo kofar da karfi ya  shiga bathtube ya  tsaya tare da kuna showel  a hankali ruwa ke tsiyaya ajikinsa a hankali komai ke dawo masa tun daga maganar     safy  har zuwa wanda  Kisna ta   furta  masa tsaki yaja yana furzar da iska safy  tana   yiwa rayuwar  gidansa shishigi kafin ya dauki mataki zai fara  fadawa mijinta daya ja mata kunneta sannan ya dakatar daita daga zuwa  gidansa har ya kammala zuciyarsa na masa zafi da tuttukin bakincikin "ko ina ruwan ta da rayuwar gidansa "?
Ya fito kungunsa daure da towel fari hannunsa rike da wani ,ga gabobin kirjinsa da damtsen hannunsa sun bude kana ganinsa kaga dan kallo dan alamun motsa jiki ya bayyana ajikinsa saurin ɗauke idanunta tayi dan kallonsa na haifar mata da damuwa muryar a sanyaye tace   "me zaki ci "?yayi mata banza ya wuce ta ya karasa ya bude wardrobe kayan shan iska ya dauka gucci farare  tass  wando da riga   ya saka  rigar ta kama jikinsa sosai  dam ana iya hango murdewar jikinsa da yadda karfin jikinsa yayi tasiri  sumar kanshi sai kyalli  take ya sanya fillifas  fari  da facing cap fari  ya dawo gaban madubi yana kallon jikinsa yana fesa turare ya ajiye kwalban turaren ya dauki system dinsa zai fita ta sake sanyawa jikinta jarumta tace "inda ka dawo mai zaka ci  ?"   dan  ina  son na dafa maka abinda zaka  ...... .."katseta  yayi ta hanyar ce mata "enough kisna kinsan bana son damuwa da yawan naci ko ? " dole sai na fadi abinda zanci  "? Ke baki san abinda ya dace ba saboda hauka ne acikin tunaninki  kike tambayata ya karasa maganar yana  k  nufar kofar dakin . "

"Allah ya huci zuciyarka
ta hanzarta bude masa kofar fuskarta babu alamun damuwa  tayi masa rakiya tana tsaye har  sai  da taga tashin motarsa  sannan ta dawo zuciyarta cike da tunanin ,  sosai  take  jinsa  ajinin jikinta bazata iya rabuwa da shi ba sai dai ta daina daukar duk wani iskanshi yana mata zatayi masa zata bashi mamaki dan bazata saba alkawarin da tayiwa kanta ba sai ya dawo ya rusuna mata kafin wata biyar dinsu ya cika ..."

Bayan muradi ya bar gidan gidan nasir ya nufa   bai shiga  cikin gidan ba ya tura mai gadi tare da mai gadi nasir ya dawo nasir na sanye da kananan kaya wando tree quater sai shirt yaja ya tsaya yana binsa da mugun kallo cikin tsananin zafin rai "muradi lafiya ka tsaya daga waje kamar wani bako?a fusace muradi ya katseshi nazo in sanar da kai kajawa matarka kunne ta daina yiwa rayuwar gidana shishigi idan ba haka sanadin ta'adancinta zai haddasa gagarumar matsala a tsakaninmu "haba muradi me yasa zaka fadi haka bayan ba ita bace silar haduwarmu tare fa matanmu suka bude ido suka ganmu bai dace ka fadi haka ba na maka alkawarin zan dauki mataki akanta  da kyar nasir ya shawo kanshi sai dai yaki shiga gidan daga nan yayi masa sallama ya wuce inda zashi
A daren kasa runtsawa yayi  duk yadda zuciyarsa ke  bukatar natsuwa, gashi yanayin garin yayi sanyi zai yi dadin bacci amman  ya kasa samu ajiyar zuciya ya dinga saukewa wanda duk Kisna tana iya juyowa , abubuwa zuciyarsa ke tunawa zuciyarsa ta jagule kamar ya daura hannu aka yasa ihu ko zai ji sauƙin zafin da take masa gani zai juyo inda take tayi saurin kawar da idanunta tare da runtsewa sai da yayi mata duban tsanake ya tabbatar da bacci take sannan ya mike ya karasa inda yake ajiyar abubuwansa masu mahimmanci ciki har da sirrin daya shafi rayuwarsa tun daga kan mahaifiyarsa  har zuwa rayuwarsa da Kisna    bude karamin akwatin zinarin yayi wanda agurin gasar kwallon duniya yaci ya cire wani kyakkyawan diary mai tsananin kyau ya mike ya fito daga dakin ya nufi parlou'n sama ya zauna idanunshi na kan diary yadda yake kallon diary haka komai ke dawo masa a hankali kamar yanzu abun ya faru ya bude  ya soma bin komai daki daki  har yazo inda mahaifiyarsa ta hadu da mahaifinsa mutumin da yake jin tsanarsa fiyye da kowa a duniya, bayan shi sai Kisna da afra wadan nan mutanen bazai taba manta su a rayuwarsa ba domin kuwa sune mutanen da suka hujijiga rayuwarsa ..."

BENUE

  daga   garin  jos benue haroon  mahaifin Aliyu ya nufa ya cigaba da fantamawa  yadda ransa ke  so ga mata ga kudin holewa  da yake samu daga gurin yammatansa dan ta kai ta kawo  baya kula ya'yan talakawa sai ya'yan masu kudi ,yayan talaka sai dai su kalleshi su kyasa amman babu fuskar da zasu  kusanci  inda yake ba dan suna  jin  tsoro ko bazai  saurarensu ba kawai kwarjinin yake  musu  cikin haka ya hadu da wata yarinya mai suna Benedicter  gebrel   asalinta  yar  kauyen  gishiri ce amman suna zaune acikin benue  ,
benedicter  dai diyar  mai kudi  ce sosai  a garin  Benue  wacce ta kammala  da karatunta na gaba da secondary a kasar enugu  tana   aiki  ne a  karkashin pot-ortority ne a garin  benue, tana samu kudi sosai ,mahaifinta ya jima da rasuwa dan a lokacin yana nema shekara goma ,ba wani girma tayi ba amman a lokacin mahaifiyarta ta damu tayi aure  dan lokacin shekarunta bazasu fi 25 ba kullum sai mahaifiyarta tayi mata mitar ta fidda miji sai tace mata ita bata samu wanda take so ba ,a lokacin akwai wani dan kawar  momynta  dake maseefar sonta dan kusan gaban kowa yake nuna  yana sonta tun daga lokacin dataji yana sonta ta dauki tsanar duniya ta daura masa ga wasu bad habit d'insa data tsana shaye shaye ga bala'in son mata duk macen daya ganin sai ya kyasa  wata rana mahaifiyarta ta sameta akan   nanyak  domin son sanin  ko tana da ra'ayinsa  bata mata mutsu  ba ila kalma daya data fahimtar da mahaifiyarta  bata son nanyak ya nemi matarsa a gaba itama zata kawo nata miji kwatsam  ta haɗu da haroon
sanadiyyar saurayin   kawarta ,  kallo ɗaya tayi masa taji ya shiga ranta har taji zata iya aurensa a lokacin da bai wuce shekara   30  a duniya ba, tashin farko ta  nuna masa  tana son shi kuma da aure sai dai ya nuna  mata  shi bashi da ra'ayin yin soyayya ko  aure a halin da yake ciki
a lokaci  kawarta Elizabeth  tace " dicter Karki wahalar da kanki  wannan guy din  bashi da lokaci soyayya   bare  lokacin wani aure , gashi  baya zama guri daya kamar mai aljanu haka  yake bashi nan gari  bashi wancan gari  gashi duk abinda kika tsana daga nanyak  yana aikatawa yana shan sigari kamar hauka  kuma yana mu'amula  da mata dabam dabam  nasan kyawunsa ne ya rud'eki  ko "? dicter  ta girgiza mata kai alamun ba haka bane  "ba kyawunsa bane ele  har ga Allah ina son shi kuma zan iya muslinta  saboda shi matukar zai aureni  halinsa  kuma zan sauya shi  "da  digiri dinki da kyawunki dicter  zaki tsaya  'batawa kanki lokaci akan wannan "?" jobles  ne fa bashi da aikin yi  sai zaman banza  da shaye shaye  "koma dai menene ele ina son shi  haka  kika sani ko ta dalilina  ya samu natsuwar zuciya  ya zauna  guri  daya har ma ya daina abinda yake  gyada kai kawai Elizabeth tayi tare yi mata   addu'ar  fatan samun nasara tunda taga ta zurma .

a hankali dicter  ta dinga shigewa  haroon   tana fahimtar  dashi yadda take jinsa a zuciyarta  dariya maganarta ta bashi  tare da mata  wani irin kallon kasan ido wanda ya zame masa jiki  dan ya sha jin ire iren wannan banzar kalmar daga bakin yammata dayawa wanda shi sam bai d'aukesu da wani tasiri ba, dan gani yake har lokacin ba'a haifi matar da zai aura ba,duk yawon garuruwan da yayi bai samu macen da tayi masa ba bama zai kirga mata nawa suke binsa da sunan soyayya  ko aure ba ,har tambayar kanshi yake yaushe ma zai samu wacce zata sace zuciyarsa kamar yadda yake sace zuciyar yammata ? face to face ya fitowa  dicter  ya nuna mata bai sonta  .
taji zafin ciwon  furta mata haka a ranta  sai dai ta danne  taki hakura da shi ta cigaba da binsa dan su shaku  a hankali  har  shakuwa mai karfi ta shiga tsakaninsu tana zuwa inda yake shima idan ya bushi iska yana kai mata ziyara  ganin yadda haroon  ke kawo mata  ziyara yasa mahaifiyarta  ta soma mata mitar  akan lallai tace wa mai zuwa gurinta   ya fito suyi aure, ta cewa mahaifiyata ta bata lokaci zata masa magana wanda ita tasan har ga Allah ko tayi masa maganar kamar  dagulawa  kanta lisafi    zatayi dan ba aurenta zai yi ba  tunda ya sha faɗa mata baya shaawar yin soyayya dan baya son ayi breaking heart d'insa ko aure zai yi sai dai yayi kawai ba dan yana son matar ba  ,ganin kyawunta da tarin ilimin bai dauke hankinsa ba yasa ta shiga   kashe masa kudi  kullum cikin siya masa kaya take  tace zata maida shi karatu saboda lura datayi yana da tsananin ilimi sai dai bashi da kwalin da zai samu nagartaccen aiki shirme ya dauki maganarta tare da sharewa , a tsarinsa wata biyar zai yi  a benue sai gashi ya kusan lasar shekara  ,
sosai suka shaku da juna a cikin irin shakuwar da sukayi ne dicter ta bashi labarinta  ta karashe da  tambayarsa nashi labarin da  garinsa ganin yadda ta ajiye batun soyayya gefe   take bashi kulawa da  kashe masa kudi  duk kayan data gani muddin zai yi masa kyau sai ta siya masa haka albashi ta idan ta amso shi take mikawa ,shi yasa ya sakankace  daita ya fada mata shi dan wani gari ne  da yadda ake zuwa garin ilo  ."

Haroon  bai iya neman kudi  ba amman ya iya kashewa dan  baya d'agawa kudi kafa duk yawansu   suna shigowa yana cinyesu kamar wani dan caca a haka dai shakuwarsu ta juye zuwa sha'awa agurin haroon dan   har suna romancing sosai lokacin daya nemi ya kusanceta  bata hanashi kanta ba dan ganinta   kamar wata dama ce  ta samu  tunda dicter ta d'an d'ana haroon   ta sake  rikicewa  akansa ta  makale  masa taji duk duniya babu abinda  ya isa ya   rabata dashi ....."

  Aiko shigar farko sai ciki bata fahimci ciki gareta ba haka suka cigaba da muamula har abin ya zame musu jiki kullum suka haɗu sai sun kusanci juna sai biyu sau uku   sai da tayi wata uku dauke da cikinsa ta fahimta  cike da murna tazo masa da labarin ciki yayi mata wani banzar kallo  tare da cewa "a she wawiya ce ke ban sani ba"?" me zanyi da wani ciki yanzu da zaki wani kwaso jiki ki zo min da mugun labari  ?
"Ki san yadda zaki yi dashi dan ni ban shirya  haihuwa da kowace mace ba ,ke ban da dabanci irin naki meye  abun yi ciki"?ni yanzu ma shirin tafiya ma nake zan bar garin nan tayi saurin zaro ido tana takowa zuwa inda yake tsaye yana shirya kayansa " ina zaka tafi ka barni haroon  duk duniya ban taba son wani halitta kamar yadda nake sonka ba, ka shiga zuciyata haroon  dan Allah haroon  karka bar rayuwata ka barni na zamo abokiyar rayuwarka shi dai haroon  jinta kawai yake yana cigaba da shirinsa har ya gama ya fuskanceta bai ce komai ba "ta kamo hannuwansa duka cikin nata "kamin magana kace na bar cikin jikina ko zan rage jin rad'ad'in dake cikin zuciyata i love you haroon kuma ina son jininka bazan iya zubarwa ba.
Ba karamin haushin  kalmar yaji ba take haushinta ya sake kamashi madadin ya kwantar mata da hankali sai  fixge hannunsa yayi  daga cikin nata yana zabga mata ƙatuwar  harara "gaskiya ciwon hauka ya kamaki da har kika yarda soyayya ta maidake haka ya karashe maganar yana ɗaukar jakar kayansa tare da goya school bag ya nufi kofar fita tayi   hanzarin biyosa hawaye Shabe Shabe akan  fuskarta "zan bika dan Allah ka tafi dani  duk inda zaka takarasa maganar cikin tsananin  kuka  "gaskiya kin haukace  wallahi ke yanzu a tunaninki zan iya daukarki  na tafi wani guri dake? " ko ina sonki dicter  bazan daukeki na tafi dake ba bare bana sonki , ke ko  iyayena basu san  yadda rayuwata take tafiya ba sannan bana yawo da kowa bare wata aba mace saboda kullum cikin samunsu nake dan haka ki cire cikin jikinki   ki cire haroon  a rayuwarki  zai fiyye miki alkhairi ".

"yanzu ko  darajan budurcina daka rabani dashi ba zan ci ba ?
Yayi murmushi yana mata kallon kaskanci "darajan spam dina ma daya zama ajikinki bazaki ci ba bare wani budurci da kullum cikin samunsa nake , na sadu da mata sama da dari biyu  a rayuwata wanda rabi daga cikinsu duk  viging ne dan haka ki adana maganarki ki san yadda zakiyi da cikin jikinki zai fiyye miki alkhairi  ya raba ta gefenta ya  fita daga  dakin......"
 




Mun sudais
[7/19, 5:32 PM] +234 803 631 5951: 💗💗💗💗💗💗
  CUTAR DA KAI
     💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

Page 18

~TRUE LIFE STORY~

*PAID BOOK*

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
bismillahirrahmanirrahim

"Wannan  littafin na kudi ne  ,mai bukata karanta shi  zai  tura 500 ta wannan   account number  din  1438775094 Aishat Abdullahi Access bank ,Idan an  tura sai a turawa wannan number alert  +234 803 238 4602   domin tabbatar da an tura , ko wannan number 08059623096 Idan Kuma vtu za'ayi  sai a tura ta wannan number 08059623096 ,kada ayi vtu a number MTN sannan kada a Kira number mtn ba'a kira dashi only chart ne .  "domin sauraran littafaina sababbi da tsofaffi  za'a iya tuntu'bar  Channel dina ta Hausa bakwai,sannan muna bada sarin Lagos  lace da kamfala  ,Lagos rapa , jaka da takalma, getzner na cotonou da  chiganvy, volyal lace  duk akan farashi mai sauki ,ga mai  bukatar  siyan ɗaya ko sari  yayi magana ta wannan number 08059623096

.....A  hankali  ta  juya ta soma   d'aga   kafafunta  da   suka  yi  sanyi   tana kallon    bayansa  tana  biye   dashi , gabad'aya  hankalinta  yayi  bala'in tashi   kanta  ya kule ta rasa   mafita , ji  take  kamar  ranta  zai bar gangar  jikinta   tsabar tashin  hankalin  data tsinci  kanta a dalilin maganarsa  .
  shi  kuwa  haroon ko  ajikinsa  tafiya  kawai  yake  yana  bubbude  kafad'a   har   ya   k'arasa  fitowa   kofar   gidan ya  gyara  zaman   jakar bayansa  idanunshi  na kan  abokansa  dake zaune  akan dogon banci suna  hira ." suna   ganinsa   dukkaninsu   suka   fad'ad'a   fuskokinsu da fara'a   ,daya   daga cikinsu   mai  suna Muhammad   ya  mika masa  hannu ,shima haroon  hannu  ya  mika masa fuskarsa a d'aure ,  ɗaya  bayan  daya  suka gaisa  domin  yin sallama  ,jikin  dicter   na kyarma   tazo   ta wuce ta  kusa  dashi  tana hawaye  ta  tsaya  nesa kaɗan  dashi  rungume da   hannuwanta duka  a qirji  tana jira ya gama ta sake rokonsa shi kuwa   ko  kallon inda take  bai  yi  ba   ya  sake  gyara  tsayuwarsa  yana  cigaba  da magana   ."

  Abokinsa   Abdul   ne ya mike  tsaye  hannunsa   cikin  na  haroon    suka ɗan   yi  nesa  kaɗan  da sauran  mutane  dake zaune ,  muryar Abdul    can kasa yace  "ya naga  dicter  duk  tayi  wani iri  ? " Ko da yake  nasan daman hakan  zai  kasance muddin  taji  labarin tafiyarka  ,  wallahi yarinyar   na  maseefar sonka  fiyye  da tunaninka  ..."
   "wannan  kuma damuwarta  ce  ba  tawa  ba   dan  bansata ta soni dole   ba  ,yanzu  ma baka  ji  yadda na  k'ara tsanarta  a cikin  zuciyata  ba , dan  karin haushi   ina  tsaka da haɗa  kayana  tazo min da  wani  banzar magana  ko a ina  ta taɓa ganin ana  irin  wannan rayuwar yanzu  da duniya ta ƙara samun  cigaba  da girmanta da komai zata kawo min hauka ."?

"Haukan  me  tazo maka dashi ? Abdul  ya  tambayeshi  hankalinsa a  matukar  tashe "wai ciki  ne  daita ni ban ma tsaya  bata     lokaci   ba   nace  ta  cire dan  bana bukatarsa a rayuwata   ya karasa maganar yana  huci "kai kuwa  haroon  bai kamata  kace mata haka ba  ko   bazaka amsa abinda   ke cikinta  ba sai ka  lalla'bata  ka  samu  ku rabu  lafiya, yanzu  dai mu   k'arasa  inda  take."
"nayi   mata  me?   yayi maganar  a  zafafe  yana yatsina  fuska  cike da zafin   zuciya  ? "dan  Allah  ka  shareta   lokaci na  tafiya  so  nake karfe shida  daidai  ta min a Abuja   "kai  dai muje  dan Allah nasan   abinda  zance mata , lalla'bata zanyi ta yarda  ta cire cikin  a wuce  gurin  dan   idan ka tafi  baka  shawo kan matsalar  ba zakayi nadama   "nadamar  me zanyi?   ya     sake  aikawa Abdul   da wata tambayar yana  jan  dogon  tsaki. "idan  yan'uwanta  suka sani  ni zaka saka cikin  matsala   ".
"Me  zasu  iya  yi ?  kai fa ka fiyye tsoro  wallahi  "dole naji tsoro haroon  yayyenta  daga  soja   sai   police  duk aikin  kaki 'yan gidansu suke  ina zan yarda  ka  tafi  ka barni cikin tashin hankali ? Haroon   ya     numfasa  tare da cewa  "kasan       Allah  banci akwai abinda zai kai ni Abuja yau wallahi idan na bar garin nan akanta shege nake ba zani     ko'ina  ba tunda babu lallai babu dole akan sai na amsa" ni wallahi  ban ma san tsautsayin daya kai ni ba "kai  dai  kasani  muje dan Allah ".     

A  hankali  suka  jero  tare  suna  cigaba  da tautaunawa  akan lamarin  har  suka karaso inda  take   tsaye tana goge  hawayen  idanunta daya  ki  tsayawa  sai  faman  gogewa  take  wasu   na  turereniyar zubowa  daga cikin  idanunta "dicter ....."
Abdul  ya  kira

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login