Showing 432001 words to 435000 words out of 495987 words
Chapter 145 - Cutar Kai Book Complete Hausa Novels by Aysha Bagudo.txt
,hannunsa ya kai wuyanta yana shafawa da bayan hannunsa yana lumlumshe Idanunshi tamkar wani maye kafin daga baya yayi kasa dashi zuwa qirjinta nan fa numfashinta ya fara sauyawa ya koma yana fita da kyar ,yayinda kasanta ya fara mintsininta yana tsiyayar da ruwan sha'awa bata san ya'akayi ba sai ji tayi ya zuge zip din gaban rigarta ya fara shafa saman brest dinta still bakinsu na haɗe yana aikin tsotsa lip's dinta da haƙoranta kamar ya samu sweet ,banda tsiyaya babu abinda kasanta ke yi ,wani irin zabura tayi tana sauke wani wahalallen numfashi a lokacin da taji yana murza kan nipple's dinta yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa gbdy ya gama rikitasu da salonsa, da zai samu fiyye da hakan daga gareta yana so a hankali ya zare harshensa cikin bakinta ya suke numfashi da ajiyar zuciya atare ."
tayi saurin sunkuyar da kanta kasa tana wasa da yatsun hannunta saboda wata irin kunya data ziyarci ilahirin jikinta ,kullum itace ke fara ƙoƙarin fito da maitarta fili kafin shi , hannu ya kai ya mayar mata da zip dinta sannan ya tsura mata ido yana cigaba kallonta "yaushe zaki tare kisna ? ,taji tambayar daga sama batare data tsammaci jinta ba , maganar ta doki kunnuwanta sosai gbdy ta rasa amsar da zata bashi "ko baki ga ya kamata ki tare a gidanki ba a matsayinki na uwar gida kafin amarya tazo ?"ta d'ago idanunta da sauri suka shiga cikin nashi ,hawaye ne ya cika idanunta ya fara zuba akan kuncinta a hankali ta fara rera masa kukan shagwa'ba tana kallonsa sai lokacin ta tuna wai aure zai yi dan soyayyar da ya nuna mata a yanzu ta mantar daita komai ,da sauri ya kai hannunsa ya tare hawayen "meye kuma abun kuka daga maganar tarewa ? ,ta girgiza masa kai alamun babu komai tana kokarin goge hawayen fuskarta ."
a natse ya janyota ya d'aurata akan cinyarsa ya kai bakinsa daidai saitin kunnenta ya soma rad'a mata magana cikin kasalalliyar muryarsa da tayi sanyi tsabar sha'awar dake d'awainiya dashi "kis.....nah "
" ki tare a yau din nan ina bukatar hakan "ya k'arasa maganar yana zira harshensa cikin kunnenta take jikinta ya sake ɗaukar rawa gbdy tsigar jikinta suka dinga mike yrrrrrrrr " zaki tare a yau din ?ya sake tambayarta yana tsotsar cikin kunneta wani irin abu taji suna yawo a sansar jikinta tun daga tafin kafafunta har zuwa tsakiyar kanta nan da nan ta rasa sukuni da natsuwa, gabobin jikinta suka dinga bud'ewa suna amsar sakoninsa masu matukar tsayawa a rai cikin sanyayyiyar muryarta mai matukar kashe jiki da tsuma zuciya tace "ka bari bayan biki sai na tare yanzu lokacin ya kure ". tayi maganar kwalla na sake cika idanunta ," haka kika fi buƙata ? ta gyada masa kai alamun" eh ! tausayin kanta take ji tasan zuwa nawal rayuwarsa itace sila faruwar haka , itace ta jawa kanta duk da hakan na cikin qaddarar rayuwarsa amman itace sanadin zuciyarta ta sake yin rauni tana mai jin tsoron tarewa , karsu je suna abubuwan da zai tunzira zuciyarta har tazo tayi abinda bashi bane ita kuma a yanzu bata bukatar wani damuwa bare tashin hankali ."
shiru yayi na second biyar sannan ya mike tsaye yana daidaita natsuwarsa da jijiyarsa dake faman harbawa ya nufi kofar fita ya murd'a key ya fice daga d'akin, tana ganin fitarsa ta sake rushewa da wani kuka mai cin zuciya sai da tayi mai isarta sannan
tayi shiru sai dai ta kasa fitowa daga d'akin tayi kwanciyarta ta dade kwance gbdy bata da niyyar tashi ta shirya zuwa dinner , kowa ya shirya banda ita ,abubuwan dake faruwa yanzu a tsakaninta da muradi ke ta'bata fiyye da tunanin mai karatu har ya sanya zuciyarta jin wani irin matsanancin kishinsa akan aurensa da nawal har take jin bazata iya tarewa ba a lokacin ,
sannan bazata iya zuwa gurin dinner ba taga takaici hawaye suka shiga gangarowa a gefen idanunta har suka jika pillow da kanta ke kwance akai, "wannan ranar itace ranar da tafi tsanar zuwansa a rayuwarta , "babu wanda bai mata magana akan ta tashi ta shirya zuwa dinner ba taki " kisna wai ba dake ake magana ba kina jin mutane ?, muryar aunty ummi ce ta doki kunnenta cikin d'aga murya ta juya da sauri tana kallonta batare da tace "uffan ba sai dai idanuwanta sunyi jazur hawaye kawai ke fita a cikinsu, so take tayi magana amman muryarta taki fitowa saboda abinda take ji yana taso mata a kahon zuciya , "kiyi yunkurin danne abinda ke karkashin zuciyarki kisna , karki yi wautar barinsa ya bayyana shawara nake baki dan sai kisa kanki a baki da farko kamar bazaki damu ba amman me yasa yau zaki damu zuciyarki akan abinda kika san babu fashi auren nan dole za'a daura shi ? da sauri ta mike zaune tana cewa "a da ban damu ba amman a yanzu na damu sosai har ina jin bakincikin auren nan aunty ummi saboda ina tsananin son mijina musamman a yanzu da nake hango tarin soyayyarta a cikin kwayar Idanunshi ..." haka zaki daure ki danne komai ki tashi ki shirya muje ai abinda baki sani bane tun tuni muradi na tsananin sonki so kuma mai girma rashin kwantar da hankalinki ne yasa kika kasa fahimtar haka auren nawal kuma qaddarar rayuwarsa ce babu yadda zai yi dole sai ta kasance a karkashin ikonsa dan haka ki tashi ki shirya tana gama fad'ar haka bata tsaya sake sauraron abinda kisna zatace ba ta nufi hanyar fita daga d'akin mikewa kisna tayi ta kulle kofar d'akin sannan ta koma tayi kwanciyarta cikin tsinkewar zuciya da fad'uwar gaba dan babu inda zata taga bakinciki da takaici haka kawai taje taga abinda zai d'aga mata hankali idan ranar kamu taje shi babu yawon mutane kamar dinner shima dan sun matsamata ne if not da bata zuwa ..".
******
Karfe uku daidai da mintuna goma sha biyar gaba-daya mutanen gidan dana gari suka fara hallara a hall din the king dake cikin redysymblue domin da jiran karasowar amarya da ango yayinda a lokacin ango ke zaune cikin hadaddiyar sabuwar motarsa lates wrangler a kofar gidansu nawal domin jiran fitowarta sanye cikin black suit da farar riga aciki, haka ma takalmin dake sanye da kafafunsa black ne tare da agogon sliver , gashin kan nan nashi da kullum ake kashe masa kudi ya sha gyara kaɗan aka aske daga baya sai kamshi turare darham silver ke tashi ajikinsa ya daura hannunsa daya akan ƙafarsa daya yana dan dukanta kaɗan kaɗan yana ciza lip's dinsa ."
a hankali nawal take taku cikin hadadden White lace ita ma komai na jikinta white ne kawayenta na biye daita rike da wani bangare na rigarta , yayinda wasu daga cikin yan'uwa da kawaye ke faman ɗaukarta hoto da video har ta karasa fitowa kawarta Khadijah tayi saurin buɗe mata kofa motar ta shiga ta zauna tana gaida shi kanta a kasa cikin tsananin tsoro da fargaba tana wasa da yatsun hannunta muryarsa a dake ya amsa mata tare da kafeta da Idanunshi yana sauke ajiyar zuciya adaidai lokacin da nasir ya ja motar , tayi kyau sosai sai dai ya tabbatar da kisnarsa ce cikin shigarta sai ta zartata a komai ,wani sanyayyen dadi ya lullubeta jin Idanunshi akanta ,byn kmr second biyu ya dauke Idanunshi zuwa wani ɓangare , ganin yadda ya dauke kanshi tare da shareta yaki magana yasa ta kai hannunta ta riko laulausan tafin hannunsa cikin nata tana sauke naunayen ajiyar zuciya bai ce mata komai ba har suka ci rabin tafiya ta ɗan kawar da tsoronsa kaɗan tare da sanyawa jikinta jarumta tace "plz my norr kayi hakuri akan abinda ya faru inshallahu baza'a sake magana akan komai ba tunda na yarda akan tsarinka tun farko dole kowa ya yarda ", muradi dake kallon gefen titi ya juyo a hankali ya tsura mata ido shi take kallo idanunta na kokarin zubar da hawaye "naji amman koda wasa wallahi kar naji wani ya nemi taka min uwa ko mata dan bazan ɗauka ba "inshallahu babu wanda zai aikata hakan ta k'arasa maganar cikin rauni ya matse hannunta dake cikin nashi gam yana cewa "karki yi kuskuren da hawayen nan suka zubo cike da farinciki tace"owk my norr ta soma kokarin maida hawayen ,nan suka bude shafin soyayya suna tafe suna hira suna nunawa juna tsantsar soyayya kafin su karasa komai ya daidaita atsakaninsu, ita kanta tasan muddin tana son zaman lafiyarta dashi ya zama dole ta kwantar da kai tabi tsarinsa , amman muddin tace zata nuna dagawa ko nuna ubanta wani ne to baza'a su zauna lafiya ba ,dan shi babu ruwansa da wani kudin ubanta ."
a haraban hall din the king nasir yayi perking ya fito ya shiga ciki ko cikakken minti goma bai yi ba ya dawo ya bude bangaren da muradi yake ya fito yana gyara zaman yar saman suit dinsa sannan ya zagaya cikin isa ya buɗe inda nawal take zaune ya mika mata hannunsa yana sakar mata kasalallen murmushinsa dake kasheta akan soyayyarsa kallonsa tayi kamar ranar ta fara ganinsa ganin yadda ta zuba masa ido ya shafi gefen fuskarta tare da bude baki yace "fito muje baby ", lumshe idanunta tayi sannan ta yunkura ta fito suna fitowa abokan ango dana amarya suka hau daukarsu hoto suna canza stly sannan suka jera zuwa cikin hall suna shiga aka saki sauti mai dadi nan mutane suka hau daukar su hoto har suka isa mazauninsu suka zauna."
duk yadda dangin nawal suke ji da kudi , isa da mulki da jiji da kansu sai da suka raina kansu da suka ga dangin muradi komai a natse suke yinsa cikin shiga iri daya lace onion colour da ratsin marun da gold ajiki yayinda gyalen kowannensu ya zamanto gold , su din basu kai su kudi ba amman akwai mutunci da daukaka tare da girmamawa da kamewa da sanin ciwon kai , haka bangaren abincisu dabam basu dogara da abincin dangin nawal ba , sun tanadi komai nasu wannan na wanne wannan a cikin hall adaidai wannan lokacin aka kawo uwar amarya da mukarabanta cikin hilus sai jiniya ke tashi ta fito da kyar cikin wani arnen lace wanda aka yiwa dinki bubu da kyar take taka kasa kawayenta na taka mata baya gaba-daya ahlin kowani bangare daga dangin amarya har zuwa na ango sun karaso amman banda kisna hakan kuwa yayiwa nawal dadi dan tasan muddin tazo to zata ruguza mata tsarin bikinta ne ."
shi kuwa muradi sai faman baza idanu kawai yake yaga ta inda zata shigo , sai dai har tsawon minti talatin da suka shigo babu ita babu alamunta sai yaranta dake kai kawo a tsakanin mutane ,shiru yayi can ya kasa hakuri ya kira aunty mufeeda ya tambayeta, a kunne ta rad'a masa tace bazata zo ba fa " yayi shiru yana tunani dalilin da yasa ta fadi haka , haka ya cigaba da zama kawai ba dan yaso ba har sanda mc ya bude taro da addu'a aka kawar amarya ta bada tahirin amarya haka Samir abokin ango kuma danuwa ya bada tahirinsa sannan akira amarya da ango zuwa fili sunyi rawa haka danginsa , mumy da kawayenta sun shiga rawa cikin anko iri daya muradi ya taso yayi mata liki sosai itama tayi masa tare da nawal , an ci an sha amarya da ango suka yanka cake uwar amarya da mumy tare da amarya da ango a tsakiyar sukayi hotuna sai ranar uwar amarya hajiya mardiyya tasan mumy , itama mumy sai ranar ta taɓa ganinta a haka har aka gama taro aka watse Allah Allah muradi yake a mayar da nawal yaje gidan yaji dalilin da yasa kisna taki zuwa gurin dinner ya tsaya a bakin kofar ɗakinta yana knowcking a hankali amman shiru tamkar babu mutun acikin d'akin, muradi duk ya rude sai zufa yake fitarwa aunty ummi ta karaso ta tsaya kusa dashi tana cewa " dama kayi yafiyarka ka huta abun ne ya motsa yau nasan zuwa nan da gobe zata sauko , ya girgiza mata kai yana cewa "haba Aunty ummi sai Kuma a barta a d'aki batare da an san halin da take ciki ba ?,to ya kake so ayi mata nayi mata magana tun kafin mu tafi dinner taki ".
sake fuskarta kofar dakin yayi yana kiran sunanta bata amsa ba illa sautin kukanta dake tashi a hankali lumshe Idanunshi yayi cikin tsanani tashin hankali yana furta " ya salam kinji ko aunty ummi Kuka take fa a cikin dakin suna nan tsaye har mumy ta karaso itama dai cewa tayi yayi tafiyarsa yaje ya hutu gobe yana da zuwa daurin aure ,haka ya juya ba dan ransa yaso ba ya tafi cike da tunaninta ,sai gurin shadaya na dare ta bude kofa ta fito idanunta sunyi jawur tamkar garwashin wuta babu wanda tayiwa magana acikinsu haka itama babu wanda yayi mata magana ta shiga kitchen ta daura ruwan zafi ta dawo falo ta dan zauna jim ta sake mikewa ta shiga kitchen ta juye ruwan a flaks ta nufi hanyar daki safy ta mike ta biyo bayanta suka shiga dakin a tare tana cewa " haba kisna ya zaki rufe kanki a daki ?, hakuri dai zaki kara akan wanda kikayi ki danne komai nasan is not easy da wahala kuma da ciwo amman ki daure , yanzu mijinki na tsananin sonki ba kamar da ba yanzu gaban kowa yake nuna kulawarsa gareki wallahi baki ga yadda ya damu akan kinki bude kofar ba , kisna ta juyo tare da rungumeta ajikinta tana rushewa da kuka "kowa murna yake da auren nan koda hakan yana nufin mutuwata "ya zasu yi kisna dole ce tasa haka , dole suyi murna kodan darajan muradi idan ba haka ba zai dauki abun wani iri ta kamata ta nufi kan gado daita ta shiga lallabata , a ranar dai bacci ya gagari idanuwan kisna sai faman juyi take akan gado shima muradi ya kasa runtsawa gashi ya kira numberta bata shiga jin sautin kukanta yafi komai daga masa hankali Allah Allah ya dinga yi gari ya waye yaje yaga lafiyarta .."
Safy dake kwance tana sharar bacci ta farka saboda mutsu mutsun kisna dake damunta ta kunna fitilar dakin tana kallonta zaune ta rafka taguni cikin zullumi da tunani,kisna ta dan juyo suka tsurawa juna ido babu wanda yace kala safy ta sake kashe fitilar ta koma ta kwanta dan tasan dole ta kasa bacci kishiya ba wasa ba barin idan kana qaunar mijinka me ma za'a yi da wata aba kishiya bancin ita din dole ce bisa fadar Allah da babu macen da zata yarda akawo mata dan wata tana zaman zamanta lafiya da mijinta cikin rufin asiri da zarar kishiya tazo komai zai rikice musu ,wata kuma a zauna lafiya daita cikin lumana da kwanciyar hankali Allah dai ya had'amu da abokiyar zama ta gari ."
washegari da misalin karfe bakwai bacci ya dauki kisna bata farka ba har sai bayan da'aka daura aure sannan ta farka ta tsurawa agogon bango dake manne a dakin ido da alamun so take ta gano tsawon lokacin data dauka tana bacci agogon ya nuna mata shabiyu saura ta maida kallonta akan safy data shigo yanzu tana kokarin daukar bakar leda "a'a kisna kin tashi ?, shigowar muradi biyu kina bacci bari na tura a fada masa kin tashi ta gyada mata kai kawai tana fita ta mike ta murdawa kofar key ta nufi toilet ta soma wanka ."
Safy na karasowa falon ta kalli inda Aryan yake zaune tare dasu Junior tace "aryan je kacewa babanku mamanku ta tashi yaron ya mike da ɗan gudunsa ya fita zuwa kofar gidan inda muradi ke zaune cikin mutane ka rantse nan gidan ne gidansu amarya saboda yadda mutane ke cike a kofar gidan ga wasu na shige da fice ana kai wa uwar ango gaisuwa tare da Allah ya sanya alkhairi ,aryan ya fada masa sakon safy ya shafa sumar kan yaron batare daya tashi ba shi kuwa sai faman taba shi yake yana sake maimata masa sakon mamansa ta tashi cikin maganarsu ta yara ,ya gyada masa kai ya mike tsaye a hankali ya dinga tsara mutane cikin farar shada har ya k'araso bakin kofar ɗakinta ya murd'a handle din kofar sai dai ya jita gam a rufe nan ya shiga knowcking aryan na tayasa har kansa ya fara sarawa "wai meke faruwa ne ?, Ya tambayi kansa tunani ya shiga yi sosai akan abinda yasa kisna ta canza acikin lokaci kankani wanda har hakan ke neman tarwatsa masa kwakwaluwa, dan ya kasa gane abinda take nufi dashi "me aka mata take fushi da kowa ?,me yasa ta kulle kanta a daki tare da nisanta kanta dashi ? tambayar da yayitawa kansa kenan a fili ya furta "oh my god plz kisna allow my brain to rest don Allah ki bude dakin bana cikin moon na rigima dake yanzu , kema kuma banason ki damu kwakwaluwata kusan minti goma yana tsaye yana magana yayinda ita kuma take bayi tana wanka batare da tasan da tsayuwarsa ba har ya gaji ya juya cikin fushi da niyyar bazai ƙara zuwa nemanta ba idan ta gaji da abinda ke damunta ta sauko ya koma cikin abokansa."
Da misalin ƙarfe biyar na yammacin ranar lahadi aka kawo nawal gidan mumy aka danka amanarta mumy ta rungumeta cikin tsanani farinciki tana cewa " Allah ya sanyawa rayuwarku albarka ai nawal diyata ce ba surukata bace sannan aka wuce daita zuwa